lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Juyin juya hali na gaskiya da ma’abotansa


Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

Dukkanin godiya da tabbata ga Allah madaukakin sarki tsira da aminci su kara tabbata ga fiyayyan halittu baki daya da mutanen gidansa tsarkaka

Da yawa yawan mutane kan jawo hankulan gama garin mutane sakamakon yawan sallarsu da tsayuwar dare ko kuma yawan azuminsu da zuwa hajjim, har zaka takai ga ire-iren wadannan mutane kan dimauta idan suka gafala daga wadancan ibadoji nasu ko da kuwa kwana daya ne rak!

Gaskiya ne lallai wadannan ayyuka wajibai daga Allah da suka rataya a wuyans, sai dai cewa ba a iya ganin wannan ibada da suka siffantu da ita aikace wato shine jihadi da umarni da kyakkyawa da hani da mummuna, saboda Allah madaukaki yace:

 ( ان الصلاة تنهي عن الفحشاء والمنكر ) .

Ita sallah tana hani da alfasha da munkari.

Mai tsayar da sallah ba tare da hani da alfasha da munkari ba misalinsa kamar misalin mai shuka kan kurman dutse yake!

 Su zantuka kamar gangar jiki ne su kuma ayyuka matsayin ruhi suke ba zai taba yiwuwa ba gangar jiki da rayu ba tare da ruhi ba hakama akasi, dukkanin biyun suna lazimtar juna a hakikance da waki’ance, dukkanin wanda yake da wadannan siffofi biyu lallai shine mafi gasgatar mutane, mafi alherin misalin da zamu iya ganin cikin wannan shine auna sahabban Imam Husaini (as) da makiyansa.

Yawancin makiya Imam Husaini sun kasance suna bautar Allah ne a fatar harshe a bayyane da sirrance, ayyukan wadannan mutane sun tafi a wofi ba tare da wata fa’ida ba kuma sun kara musu wuta a ranar kiyama, sunyi hasara duniya da lahira, hakan ya kasance kansu sakamakon fitowarsu don yakar Husaini (as) da kasha zuriyar manzon Allah (s.a.w) da sahabbansa da ribatarsu ta kamasu.

Makiyan Imam Husaini (as) sun kasance masu karyata kankin kansu gabanin yin karya kan Allah da manzonsa, sun kasance suna fadin abinda yake sabanin kangararriyar zuciyarsu.

Sun kasance suna rikar addini matsayin tsanukan cimma burukansu da muradansu na duniya, a hakika sun kasance masu bautar shaidan koma bayan ubangiji.

Sannam gefe guda kuma zamu yanda sahabban Imam Husaini (as0 su kasance mafi gaskiyar mutane sakamakon tsayuwarsu kyam a tare da gaskiya karkashin jagorancin Imam Husaini (as)

Sahabbansa (as) yawan adadin makiya nai razana su ko tsorata su, sun kasance tare da gaskiya kamar yanda Allah madaukaki yake cewa:    

 ( رجال صدقوا ما عاهدوا الله ... ) .

Mazaje ne da suka gasgata abinda su kaiwa Allah alkawari…

Sun kasance kan basira cikin lamarin addininsu da duniyarsu da lahirarsu, sakamakon sun kasance masu jikkanta ibadarsu ta yau da gobe wacce suka shuka ta cikin zukatansu da jama’arsu sakamakon gasgatuwar zantukansu da ayyukansu.

Sahabbansa (as) sun tabbatarwa da mutane cewa dukkanin wanda ya kasance yana bautar Allah a iya fatar harshe zuciyarsa bata tasiranta da ibadar  kuma baya yakar zalunci da danniya, to lallai shi kamar misalin mai gini ne cikin hiyali da wahami!!

Shi muslunci ba takaitu cikin sallah da azumi basa sauran ibadoji ba, bari dai shi muslunci addini ne na aiki da takawa da umarni da kyakkyawa da hani da mummuna, sannan mafi alherin dalili kan haka shine fadinsa madaukaki:  

 ( اعلموا فيسرى الله عملكم .... ) .

Kuyi aiki da sannu Allah zai ga aikinku….


Tura tambaya