TARBIYYAR HALITTA DA MUSLUNCI 9
WANENE MAI TARBIYA ? 10
KASHE KASHEN TARBIYA 12
ABUBUWAN DA SUKA RATAYU DA ITA 13
IYALI CIKIN MA'ANAR LUGGA DA ISDILAHI 13
IYALI A LUGGANCE : 14
■ AUREN DABI'A 24
KASHE KASHEN AURE: 41
ADADIN MAZAJE: 44
HANYOYIN TABBATAR AURE : 46
5 - KASANTUWAR MIJI DAYA RAK MACE DAYA RAK: 46
SAMUN CIKAR KAMALA CIKIN AURE 54
DALILAN YIN AURE CIKIN SUNNA MAI DARAJA 60
1 TAUHIDI: 61
2-TAQAWA : 62
3- MAFI SOYUWAR GINI WAJEN ALLAH: 62
4- SUNNAR ANNABI: 63
5 - QARUWAR ARZIQI : 65
6 – QARUWAR IMANI : 69
7- ALFAHARI : 70
8- QARUWAR IBADA : 71
9- GARKUWA : 71
10 – SADAR DA ZUMUNCI 72
11- ADDINI : 72
12- DEBE HASO: 73
1- ASALI 76
2- WATA CIKIN BURUJIN AQRABU : 76
HUKUNCIN ILIMIN BUGA QASA CIKIN SHARI'A MAI TSARKI 77
MAHALLIN DA MUTUM KE RAYUWA CIKI 84
SON MATA 84
MATA MASU MUTUNCI DA DARAJA 88
1 MATAYE MAFI KYAWUN FUSKOKI MAFI QARANCI SADAKI 90
2- QARANCIN BUQATU DA SAUQAQE HAIHUWA: 91
3- KASHE KASHEN MATA CIKIN KYAWAWAN HALINSU 91
TSARA CIKIN AURE 116
FAFUTIKA CIKIN AURE 133
AUREN WURI 134
HUDUBA 136
SADAKI 142
HADARIN TSADAR SADAKI : 148
AUREN SHARI'A 150
DAREN ANGONCI 150
AYYUKAN DAREN ANGONCI : 154
ZAMA TARE DA AMARYA HAR TSAWON KWANAKI BAKWAI : 155
WALIMA 155
RARRABA ALEWA KO DABINO 157
LADUBBAN SADUWA DA IYALI 158
1- MAFI DADIN DADADA 160
2- WASA DA MATA GABANIN JIMA'I : 160
4 – HUKUNCIN AZALO : 174
5 – ADDU'A YAYIN KUSANTAR IYALI 175
35 – daga abu rabi'i ashshami, ya ce 175
1 – HAQURI 178
2 – KAMEWA DAGA ZALUNCI DA CUATARWA 179
HAQQOQIN MATA 180
CIYARWA DA YALWATAWA 185
TAUSAYAWA DA KAMEWA DAGA ZALUNCI 187
KAMEWA DAGA BARIN DUKA MAI CUTARWA 187
UMARNI DA KYAKKYAWA DA HANI DA MUMMUNA 193
GARKUWA 196
8 – KYAUTATAWA : 196
9 - KYAWUNTA ZAMANTAKEWA 197
3 – TAUSAYAWA MIJI : 208
4 – HIMMATUWA DA KULA DA CIKIN GIDA DA KAYYAKINSA : 209
5 - HIMMATUWA CIKIN SAUKE HAQQOQI 209
6 – JIMA'I 210
7 - ADO 213
8 – KAMEWA CIKIN MAGANA : 219
SHUGABANTAR IYALI 225
DALILAI DA SUKE SANYA DAWWAMAR AURE 227
1 – SON JUNA 228
2 – YAWAITA AIKATA ALHERI: 228
4 – SANYA FARIN CIKI: 229
5 – BIYAYYA DA NEMAN YARDAR MIJI: 230
6 – KIYAYE MUTUNCI DA DUKIYA : 230
7 – TAIMAKO DA TALLAFAWA 230
8 – TARBAR MIJI DA KYAWUNTA BANKWANA DA SALLAMA : 231
9 – KALAMIN AQIDOJI MAI KYAWU DA QARFAFAFFEN FURUCI. 232
10 – KARBAR UZURI DA YIWA JUNA UZURI : 232
11 – BINSU SANNU SANNU CIKIN KOWANNE HALI : 233
12 – KYAWUNTA LAFAZI CIKN KOWANNE YANAYI : 233
13 – RASHIN SAURARON KYAUTATA AIKI DARI BISA DARI 233
14 – RASHIN IKON DAUKAR NAUYI A RAYUWANCE : 234
15 – RASHIN GORI KAN MIJI : 234
16 – RASHIN QAURACEWA AL'AMARIN SHIMFIDA: 235
17 - YIN SHAWARA DA MATA BANDA BIYE MUSU: 235
18 – TAKA TSAN TSAN DA KUMA FARKAWA : 238
19 – HANKALTA 239
20 - MIJI SHI NE MUTUNCIN MATARSA 240
21 – KISHI 240
22 – TAIMAKEKENIYYA 242
23 – DADADAWA IYALI 243
27 – WATSI DA BOAKANCI DA TSAFE TSAFE : 244
28 - HIDIMA MADAWWAMIYA 245
29 – GODIYA 246
29 – QAUNAR JUNA 247
TSINTUWA GUDA BIYU GIDAN ALI DA FATIMA (AS) 248
SON `YA`YA DA QANAN YARA 252
MUQAMI NA 2 254
MUQAMI NA 3 260
NEMAN HAIHUWAR DA NAMIJI 260
MUQAMI NA 4 266
RAINON CIKI DA LADUBBNSA 266
TASIRIN ABINCI KAN MATA MASU CIKI DA YARA DA JIMA'I 267
MUQAMI NA 6 269
HAIHUWA 269
MUQAMI NA 7 270
SHAYARWA 270
MUQAMI NA 8 273
RAINON YARO 273
MUQAMI NA TARA 279
TAYA MURNA DA SAMUN DA 279
MUQAMI NA 10 281
AQIQA 281
WASU AYYUKAN MUSTAHABBAN NA DABAN 286
MUQAMI NA 11 287
KACIYA 287
MUQAMI NA 12 290
KAMANCECENIYAR DA DA MAHAIFINSA 290
MUQAMI NA 13 292
MATAKAN TARBIYYYAR YARA 292
MUQAMI NA 14 298
ADALCI TSAKANIN `YA`YA 298
MUQAMI NA 15 300
SUMBATA NA DAGA ALAMOMIN SO 300
FASALI NA 9 302
FASALI NA 10 317
BATUTUWA DABAN DABAN 317
FASALI NA 11 325
SAKI 325
GABATARWA 327
HAQIQANIN LADABI KAN HASKEN MAZHABAR IYALN GIDAN ANNABI ( AS ) 329
WAYE ME LADABTARWA ? 336
MEYE LADABI ? 338
ASALAN LADUBBA 341
MASADIR CIKIN LADUBBA 347
MASADIR DIN LARABCI 349
TABLE OF CONTENTS 355
- CIKIN HALLARAR ALHERI
- HUJJOJIN HALASCIN YIN TAKIYYA A MUSLUNCI DAGA MAHANGAR MANYAN MALAMAI GUDA BIYU
- FARKAR DA MAI BACCI CIKIN TABBATUWAR GANIN IMAM KA'IM A.S
- ALAMOMIN ANNABI CIIKIN KUR'ANI MAI GIRMA
- HAKURI DA FUSHI
- Bada'u tsakanin hakika da kagen makiya
- FALALAR DAREN LAILATUL KADRI
- WAHABIYANCI A TSAKANIN GUDUMA DA
- HASKEN SASANNI CIKIN SANIN ARZIKI
- AQIDUN MUMINAI
- FATIMA TAGAR HASKAYE
- SIRRIKAN AIKIN HAJJI DA ZIYARA
- TARBIYYAR IYALI A MAHANGAR ALKUR'ANI DA AHLULBAITI
daga cikin dokoki da sunnar dabi'a da ikon kan dukkanin halitta bari ma dai kan dukkanin wani abu koma bayan Allah matsarkaki shi ne dokar nau'i don ya zama dalili kan dayantakar Allah da dabantakarshi shi ne kasantuwarsa daya rak wanda bai da kishiya babu misalinsa babu wani irinsa bai da nau'i.
dukkanin wani mai da'awa dole ne ya zo da shaida ba a karbar da'awa ba tareda ita ba kamar yadda ya kasance cikin shari'ar Allah da dokoki dan adam, ana kiranta a shari'ar islama da shaida ta shari'a tana kasancewa shaidu biyu adalai, da ita da'awa ke tabbata ta zama gaskiya.
Allah matsarkaki yana da shaida a dabi'ance da ke shaida kan dabantakarsa da dayantakarsa, shi ne dokar kasantuwar komai nau'i haqiqa shi ya halicci kowanni abu tagwai nau'i bibiyu don ya zama daga cikin ayoyinsa bisa cewa shi dayane rak tal bai da kishiya. domin nau'i na tilasta cudanya da wani wanda hakan na bayyana buqatuwa da talautuwa, kuma hakan na korewa kasantuwa da wanda samuwarsa take ba wajibi ba a kankin kansa da zatinsa, bari ma dai ita buqatuwa na daga kebantacce abu da ya kebanta cikin wanda samuwarsu bata zama wajibi ba, shi Allah matasarkaki mawadaci ne abin godiya, babu cudanya cikinsa, bai da kishiya, shi samuwa ne tsantsa dayanda bai da na biyu, kwaya daya tal da ba cudanya cikinsa ya na nuni game da dokokin nau'i cikin littafi mai karamci da hikima:
[1] أوَ لَمْ يَرَوْا إلَى الأرْضِ كَمْ أ نْبَـتْنَا فِيهَا مِنْ كُلِّ زَوْج كَرِيم
shin ba zasu yi duba zuwa ga qasa ba da yawa muqa tsirar cikinta daga dukkan nau'i me kyawu.
اهْتَزَّتْ وَرَبَتْ وَأ نْبَـتَتْ مِنْ كُلِّ زَوْج بَهِيج[2]
sai ta girgiza kuma ta kumbura ta tsirar daga dukkanin nau'i mai ban sha'awa.
وَمِنْ كُلِّ شَيْء خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ[3]
kuma daga kowanne abu mun halicci nau'i biyu tsammaninku zakuyi tunani.
[4]وَأ نَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَـيْنِ الذَّكَرَ وَالاُ نْثَى
haqiqa shi ya halicci nau'i biyu sune mace da namiji.
[5] سُبْحَانَ الَّذِي خَلَقَ الأزْوَاجَ كُلَّهَا مِمَّا تُنْبِتُ الأرْضُ
tsarki ya tabbata ga wanda ya halicci nau'uka dukkaninsu daga abinda qasa ke tsirarwa.
وَاللهُ جَعَلَ لَكُمْ مِنْ أنفُسِكُمْ أزْوَاجا[6]
Allah ya sanya muku matayen aure daga kawukanku.
وَمِنْ آيَاتِهِ أنْ خَلَقَ لَكُمْ مِنْ أنفُسِكُمْ أزْوَاجاً لِتَسْكُـنُوا إلَيْهَ[7]ا
yana daga ayarsa ya hilttar muku mataye daga kawukanku do ku samu natsuwa ya zuwa garesu.
وَاللهُ خَلَقَكُمْ مِنْ تُرَاب ثُمَّ مِنْ نُطْفَة ثُمَّ جَعَلَكُمْ أزْوَاجا[8]
Allah ya halicce ku daga qasa sannan daga digon maniyi sannan ya sanya ku surkin maza da mata.
وَمِنَ الأ نْعَامِ أزْوَاجا[9]ً
(daga dabbobi maza da mata )
[10] هُوَ الَّذِي خَلَقَكُمْ مِنْ نَفْس وَاحِدَة وَجَعَلَ مِنْهَا زَوْجَهَا
shi ne wanda ya halicce ku daga rai guda ya sanya ma'aurata daga gareta.
خَلَقَكُمْ مِنْ نَفْس وَاحِدَة ثُمَّ جَعَلَ مِنْهَا زَوْجَهَ[11]ا
ya halicce ku daga rai guda sannan ya sanya ma'uarata daga gareta.
يَا أ يُّهَا النَّاسُ اتَّقُوا رَبَّكُمُ الَّذِي خَلَقَكُمْ مِنْ نَفْس وَاحِدَة وَخَلَقَ مِنْهاَ
زَوْجَهَ[12]ا
ya ku wadanda sukayi imani kuji tsoron Allah wanda ya halicce daga rai guda ya halicci ma'aurata daga gareta ).
daga cikin ayoyinsa da a ke qafa dalili da dasu kan dayantuwar Allah da kasantuwarsa daya rak tal kuma shi bai da na biyu shi ne kasantuwar kowanne wanne abu nau'i biyu, haqiqa ubangiji duk da cewa ya halicci mutum daga rai guda sai dai cewa ya halittar masa mace, ya halicci adamu (as) ya halicci hauwa'u daga ragowar yinbun halittar adamu ta kuma kasance mata gareshi.
daga abubuwan ke qara tabbatarda abubuwa nau'i biyu ne mace da miji, kasantuwar qasa da sama nau'i , dare da rana , kasantuwar duk wani tamata da maza daga tsirrai da dabbobi mutane kai hatta ruhi wanda ya kasance daga digon maniyyin namiji da jiki wanda ya kasance daga digon maniyyin mace dukkansu daga nau'ine.
dokar kasantuwar kowanne abu nau'i biyu mace da namiji ta gudana hatta kan sassan jikin dan adam misali jijiyoyin da suke cikin kwakwalwa sun kasance daga nau'in mace da namiji, barbarar halitta shi ma na gudana kan dokokin nau'i mace da namiji, daga gareshi yake haifar da duniyoyin badini da na ruhi da zuciya misaliyya da hisssiya, a duniyar jikkuna dab'ia da sinadarai abubuwa uku ke haifuwa da kasantuwa sune: ma'adanai tsirrai da dabbobi daga cikinsu kwai mutum, daga barbara akwai abin da ke kebanta da kammalallen mutum da duniyar dabi'a, sannnan cikakken mutum babu banbanci cikin kasantuwar mace ko namiji shi `ya`yan bishiyar samuwa ne, shi hadafi ne na harka guda biyu samuwa da samarwa, mace ta na da matsayin wajen halittar ubangiji ita kamar bishiya ce da jijiyarta ta tabbata reshenta ya daga sama tana ba da kayan marmarinta kowanne lokaci, kammalallen mutum cikakke idan ya kasance daga namiji matsayin mabayyanar hankalin game gari ne idan kuma ya kasance mace mabayyana ce ta surar ruhi game gari ragib isfahani cikin littafin mufradatul qur'ani ya na cewa: ana amfani da Kalmar زوج kan dukkanin dayan cikin biyun nau'in masu abokantakar juna namiji da mace, haka cikin dabbobi da wasunsu kamar huffi da takalmi fade da dukkanin abin da ya cudanya da wani da yake kama da shi ko kishiyar nau'in [13]
ubangiji madaukakin sarki na cewa :
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَـيْنِ الذَّكَرَ وَالاُنثَى[14]
sai ya sanya daga gareshi nau'i biyu mace da namiji
[15] وَزَوْجُكَ الجَنَّةَ
ka zauna aljanna da matarka.
[16] هُمْ وَأزْوَاجُهُمْ
su da matayensu.
[17] احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأزْوَاجَهُمْ
ku tara wadanda suka yi zalunci da abokan hadinsu.
إلَى مَا مَتَّعْنَا بِهِ أزْوَاجاً مِنْهُم[18]
ya zuwa abinda muka jiyar dasu dadi nau'i nau'i daga garesu.
سُبْحَانَ الَّذِي خَلَقَ الأزْوَاجَ[19]
tsarki ya tabbata ga wanda ya halicci nau'i nau'i.
وَمِنْ كُلِّ شَيْء خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ[20]
daga dukkanin wani abu mun halicci nau'uka biyu.
saboda haka Allah madaukaki shi kadai ne bai da abokin cudanya sannan dukkanin halittun da suke duniya nau'uka ne saboda suna da kishiya ko akwai wanda ke kamanceceniya dasu da cudanya ba zasu gushe da cudanya ta wani fuska ba. Abin da ya sa mu kawo nau'uka don ya zama tunatarwa da cewa dukkanin wani abu ko da kuwa bai da abin da ke kishiyantarsa da kamanceccniya da shi to bai kubuta daga daga jauhari da aradi da wadancan nau'uka biyu cikin fadinsa:
أزْوَاجاً مِنْ نَبَات شَتَّى[21]
nau'i nau'i daga tsirrai daban daban..
ma'ana nau'o'i masu kamanceceniya da juna , haka cikin fadinsa:
مِنْ كُلِّ زَوْج كَرِيم[22]
daga dukkanin nau'i mai karamci
[23] ثَمَانِيَةَ أزْوَاج
nau'o'i guda takwas.
وَكُـنتُمْ أزْوَاجاً ثَلاثَة[24]
( kuma kun kasance nau'i uku )
ai abokanan cudanya uku sune wanda Allah ya fassara su cikin fadinsa :
وَإذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ[25]
(kuma idan rayuka aka cudanya su da jikkunansu )
Ance an cudanya kowa da tareda wadanda suka yiwa biyayya ko dai wuta ko aljanna, misalin fadinsa madaukaki:
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأزْوَاجَهُم[26]
Ku tara wadanda suka yi zalunci da abokanan cudanyansu
saboda kwanne irin abu cikin duniyar dabi'a bai gushewa daga nau'i dokar auratayya ko kuma ace nau'antaka zartacciya ce kan duniyar dabi'a .
[1] Shu'ara:7
[2] Hajji:5
[3] Azzariyat:49
[4] Annajajamu:45
[5] Yasin:36
[6] Annahli:72
[7] Rum:21
[8] Fadir:11
[9] Shura:11
[10] A'araf:189
[11] Zumar:6
[12] Nisa'i:1
[14] Alqiyamat:39
[15] Baqara:35
[16] Yasin:56
[17] Assafat:22
[18] Alhijir:88
[19] Yasin:36
[20] Azzariyat:8
[21] Azzariyat:49
[22] Shu'ara:7
[23] An'am:8
[24] Waqi'a:7
[25] Takwir:7
[26] Assafat:22