TARBIYYAR HALITTA DA MUSLUNCI 9
WANENE MAI TARBIYA ? 10
KASHE KASHEN TARBIYA 12
ABUBUWAN DA SUKA RATAYU DA ITA 13
IYALI CIKIN MA'ANAR LUGGA DA ISDILAHI 13
IYALI A LUGGANCE : 14
■ AUREN DABI'A 24
KASHE KASHEN AURE: 41
ADADIN MAZAJE: 44
HANYOYIN TABBATAR AURE : 46
5 - KASANTUWAR MIJI DAYA RAK MACE DAYA RAK: 46
SAMUN CIKAR KAMALA CIKIN AURE 54
DALILAN YIN AURE CIKIN SUNNA MAI DARAJA 60
1 TAUHIDI: 61
2-TAQAWA : 62
3- MAFI SOYUWAR GINI WAJEN ALLAH: 62
4- SUNNAR ANNABI: 63
5 - QARUWAR ARZIQI : 65
6 – QARUWAR IMANI : 69
7- ALFAHARI : 70
8- QARUWAR IBADA : 71
9- GARKUWA : 71
10 – SADAR DA ZUMUNCI 72
11- ADDINI : 72
12- DEBE HASO: 73
1- ASALI 76
2- WATA CIKIN BURUJIN AQRABU : 76
HUKUNCIN ILIMIN BUGA QASA CIKIN SHARI'A MAI TSARKI 77
MAHALLIN DA MUTUM KE RAYUWA CIKI 84
SON MATA 84
MATA MASU MUTUNCI DA DARAJA 88
1 MATAYE MAFI KYAWUN FUSKOKI MAFI QARANCI SADAKI 90
2- QARANCIN BUQATU DA SAUQAQE HAIHUWA: 91
3- KASHE KASHEN MATA CIKIN KYAWAWAN HALINSU 91
TSARA CIKIN AURE 116
FAFUTIKA CIKIN AURE 133
AUREN WURI 134
HUDUBA 136
SADAKI 142
HADARIN TSADAR SADAKI : 148
AUREN SHARI'A 150
DAREN ANGONCI 150
AYYUKAN DAREN ANGONCI : 154
ZAMA TARE DA AMARYA HAR TSAWON KWANAKI BAKWAI : 155
WALIMA 155
RARRABA ALEWA KO DABINO 157
LADUBBAN SADUWA DA IYALI 158
1- MAFI DADIN DADADA 160
2- WASA DA MATA GABANIN JIMA'I : 160
4 – HUKUNCIN AZALO : 174
5 – ADDU'A YAYIN KUSANTAR IYALI 175
35 – daga abu rabi'i ashshami, ya ce 175
1 – HAQURI 178
2 – KAMEWA DAGA ZALUNCI DA CUATARWA 179
HAQQOQIN MATA 180
CIYARWA DA YALWATAWA 185
TAUSAYAWA DA KAMEWA DAGA ZALUNCI 187
KAMEWA DAGA BARIN DUKA MAI CUTARWA 187
UMARNI DA KYAKKYAWA DA HANI DA MUMMUNA 193
GARKUWA 196
8 – KYAUTATAWA : 196
9 - KYAWUNTA ZAMANTAKEWA 197
3 – TAUSAYAWA MIJI : 208
4 – HIMMATUWA DA KULA DA CIKIN GIDA DA KAYYAKINSA : 209
5 - HIMMATUWA CIKIN SAUKE HAQQOQI 209
6 – JIMA'I 210
7 - ADO 213
8 – KAMEWA CIKIN MAGANA : 219
SHUGABANTAR IYALI 225
DALILAI DA SUKE SANYA DAWWAMAR AURE 227
1 – SON JUNA 228
2 – YAWAITA AIKATA ALHERI: 228
4 – SANYA FARIN CIKI: 229
5 – BIYAYYA DA NEMAN YARDAR MIJI: 230
6 – KIYAYE MUTUNCI DA DUKIYA : 230
7 – TAIMAKO DA TALLAFAWA 230
8 – TARBAR MIJI DA KYAWUNTA BANKWANA DA SALLAMA : 231
9 – KALAMIN AQIDOJI MAI KYAWU DA QARFAFAFFEN FURUCI. 232
10 – KARBAR UZURI DA YIWA JUNA UZURI : 232
11 – BINSU SANNU SANNU CIKIN KOWANNE HALI : 233
12 – KYAWUNTA LAFAZI CIKN KOWANNE YANAYI : 233
13 – RASHIN SAURARON KYAUTATA AIKI DARI BISA DARI 233
14 – RASHIN IKON DAUKAR NAUYI A RAYUWANCE : 234
15 – RASHIN GORI KAN MIJI : 234
16 – RASHIN QAURACEWA AL'AMARIN SHIMFIDA: 235
17 - YIN SHAWARA DA MATA BANDA BIYE MUSU: 235
18 – TAKA TSAN TSAN DA KUMA FARKAWA : 238
19 – HANKALTA 239
20 - MIJI SHI NE MUTUNCIN MATARSA 240
21 – KISHI 240
22 – TAIMAKEKENIYYA 242
23 – DADADAWA IYALI 243
27 – WATSI DA BOAKANCI DA TSAFE TSAFE : 244
28 - HIDIMA MADAWWAMIYA 245
29 – GODIYA 246
29 – QAUNAR JUNA 247
TSINTUWA GUDA BIYU GIDAN ALI DA FATIMA (AS) 248
SON `YA`YA DA QANAN YARA 252
MUQAMI NA 2 254
MUQAMI NA 3 260
NEMAN HAIHUWAR DA NAMIJI 260
MUQAMI NA 4 266
RAINON CIKI DA LADUBBNSA 266
TASIRIN ABINCI KAN MATA MASU CIKI DA YARA DA JIMA'I 267
MUQAMI NA 6 269
HAIHUWA 269
MUQAMI NA 7 270
SHAYARWA 270
MUQAMI NA 8 273
RAINON YARO 273
MUQAMI NA TARA 279
TAYA MURNA DA SAMUN DA 279
MUQAMI NA 10 281
AQIQA 281
WASU AYYUKAN MUSTAHABBAN NA DABAN 286
MUQAMI NA 11 287
KACIYA 287
MUQAMI NA 12 290
KAMANCECENIYAR DA DA MAHAIFINSA 290
MUQAMI NA 13 292
MATAKAN TARBIYYYAR YARA 292
MUQAMI NA 14 298
ADALCI TSAKANIN `YA`YA 298
MUQAMI NA 15 300
SUMBATA NA DAGA ALAMOMIN SO 300
FASALI NA 9 302
FASALI NA 10 317
BATUTUWA DABAN DABAN 317
FASALI NA 11 325
SAKI 325
GABATARWA 327
HAQIQANIN LADABI KAN HASKEN MAZHABAR IYALN GIDAN ANNABI ( AS ) 329
WAYE ME LADABTARWA ? 336
MEYE LADABI ? 338
ASALAN LADUBBA 341
MASADIR CIKIN LADUBBA 347
MASADIR DIN LARABCI 349
TABLE OF CONTENTS 355
- CIKIN HALLARAR ALHERI
- HUJJOJIN HALASCIN YIN TAKIYYA A MUSLUNCI DAGA MAHANGAR MANYAN MALAMAI GUDA BIYU
- FARKAR DA MAI BACCI CIKIN TABBATUWAR GANIN IMAM KA'IM A.S
- ALAMOMIN ANNABI CIIKIN KUR'ANI MAI GIRMA
- HAKURI DA FUSHI
- Bada'u tsakanin hakika da kagen makiya
- FALALAR DAREN LAILATUL KADRI
- WAHABIYANCI A TSAKANIN GUDUMA DA
- HASKEN SASANNI CIKIN SANIN ARZIKI
- AQIDUN MUMINAI
- FATIMA TAGAR HASKAYE
- SIRRIKAN AIKIN HAJJI DA ZIYARA
- TARBIYYAR IYALI A MAHANGAR ALKUR'ANI DA AHLULBAITI
وقال (صلى الله عليه وآله) : « التمسوا الرزق بالنكاح
9-Manzon Allah (saw) ya ce: ku nemi arziqi ta hanyar yin aure.
عَنْ أَبِي عَبْدِ اللَّهِ ع قَالَ: جَاءَ رَجُلٌ إِلَى أَبِي عَبْدِ اللَّهِ ع فَقَالَ لَهُ هَلْ لَكَ مِنْ زَوْجَةٍ فَقَالَ لَا فَقَالَ أَبِي وَ مَا أُحِبُّ أَنَّ لِيَ الدُّنْيَا وَ مَا فِيهَا وَ أَنِّي بِتُّ لَيْلَةً وَ لَيْسَتْ لِي زَوْجَةٌ ثُمَّ قَالَ الرَّكْعَتَانِ يُصَلِّيهِمَا رَجُلٌ مُتَزَوِّجٌ أَفْضَلُ مِنْ رَجُلٍ أَعْزَبَ يَقُومُ لَيْلَهُ وَ يَصُومُ نَهَارَهُ ثُمَّ أَعْطَاهُ أَبِي سَبْعَةَ دَنَانِيرَ ثُمَّ قَالَ لَهُ تَزَوَّجْ بِهَذِهِ ثُمَّ قَالَ أَبِي قَالَ رَسُولُ اللَّهِ ص اتَّخِذُوا الْأَهْلَ فَإِنَّهُ أَرْزَقُ لَكُم[1]
10-Alkafi da isnadinsa daga baban Abdullah (as) wani mutum ya je wajen baban Abdullah (as) sai babana ya ce masa shin kana da aure sai mutum ya ce: a'a, babana ya ce: bana son duniya da dukkanin abin da ke cikinta ya kasance ni na kwana dare daya alhalin banda mata, sannan ya qara cewa raka'a biyu da mai aure zai sallaceta tafi falala daga tsayuwar daren tuzuru da azumce rana, sai ya bashi dinare bakwai ya ce : ka yi aure da wannan, ya ce: manzon Allah (saw) ya ce ku riqi iyali haqiqa su arziqinku ne.
المصدر بسنده عن جعفر بن محمّد عن أبيه عن آبائه (عليه السلام) قال : قال رسول الله (صلى الله عليه وآله) : من ترك التزويج مخافة العيلة فقد أساء ظنّه بالله . إنّ الله عزّ وجلّ يقول : ( إنْ يَكُونُوا فُقَرَاءَ يُغْنِهِمُ اللهُ مِنْ فَضْلِهِ[2]
11-daga baban jafar (as) daga babanninsa ya ce : manzon Allah (saw) ya ce : duk mutumim da yaqi yin aure saboda tsoron talauci lalle ya munanta zatonsa ga Allah, haqiqa Allah mai girma da daukaka ya na cewa: idan suka kasance talakawa Allah zai wadatasu daga falalarsa.
ـ الفقيه ، بسنده ، قال النبيّ (صلى الله عليه وآله) : من سرّه أن يلقى الله طاهراً مطهّراً فليلقه بزوجة ، ومن ترك التزويج مخافة العيلة فقد أساء الظنّ بربّه عزّ وجل[3] .
12-Daga littafin alfaqihu da isnadinsa manzon Allah (saw) na cewa: dukkanin wanda ya ke faranta masa ace ya hadu da ubangiji ya na tsarkakakke mai tsarkakewa to ya hadu da shi yana mai aure, dukkanin wanda ya bar aure saboda tsoron talauci lalle ya muzanta zatonsa da ubangijinsa mai girma da daukaka.
عَنْ أَبِي عَبْدِ اللَّهِ ع قَالَ: جَاءَ رَجُلٌ إِلَى النَّبِيِّ ص فَشَكَا إِلَيْهِ الْحَاجَةَ فَقَالَ تَزَوَّجْ فَتَزَوَّجَ فَوُسِّعَ عَلَيْه.وقال:اتخذوا الأهل فانه أرزق لكم,وقال:تزوجوا للرزق فان لهن البركة.[4]
13-.Alkafi da isnadinsa daga baban Abdullah (as) ya ce : wani mutum ya zo wajen annabi (saw) sai ya kai kukan buqatarsa ga annabi, sai annabi (saw) ya ce masa kayi aure, sai mutum ya yi aure Allah ya yalwata masa arziqi a wani fadin manzon Allah (saw) yace : kuyi aure don neman arziqi haqiqa albarka na tare da mata.
duk wanda ya kasance talaka daga cikin tasirin canjin yanayi cikin aure shi ne samun qarin arziqi, kamar yadda ubangiji ke fadi ( idan sun kasance talakawa Allah zai wadatasu daga falalarsa ) yayin da saurayi ya yi aure da farko zai ga cewa an dora nauyi kan wuyansa to anan nefa zaka ga ya daura damara da dagewa wajen yin aiki tukuru, sai kaga arziqinsa na ta qaruwa, Allah na azurta wanda ya so ba tare da lissafi ba ya sanya albarka cikin wanda ke yin aiki da tsarkakakkiyar niyya da dogaro da shi, baya tsoron talauci da yawan iyali haqiqa arziqin kowa na hannun Allah, kamar yadda ya zo cikin Karin Magana cewa: dukkanin wanda aka azurta shi da haqora to za a azurta da gurasar da zai tauna.
قال رسول الله (صلى الله عليه وآله) : « من ترك التزويج مخافة العيلة فقد أساء الظنّ بربّه ، لقوله سبحانه وتعالى : إنْ يَكُونُوا فُقَرَاءَ يُغْنِهِمُ اللهُ مِنْ فَضْلِه
14-manzon Allah(saw):duk wanda ya qi yin aure saboda tsoron talauci lalle ya munana zato ga Allah, saboda fadin Allah: idan sun kasance talakawa Allah zai wadata su daga falalarsa.
Lalle mumini ya kyawunta zato ga ubangijinsa, haqiqa Allah matsarkaki na cewa: ni ina wajen zaton bawana mumini, kuma Allah na son masu tawakkali, shi motsi da fita nema suna kan bawa albarka kuma na wajen ubangiji kamar yadda ya zo cikin karin magana.
قال (صلى الله عليه وآله) : تزوّجوا النساء ، فإنّهنّ يأتين بالمال
15-manzon Allah (saw)ya na cewa : ku auri mataye haqiqa su suna kawo dukiya.
Allah ma'abocin albarka ya na albarkantakar ma'aurata masu miqa al'marinsu gareshi da tawakkali, matar da ka aura takan zama sanadin samun dukiya da kudade na halaliya da arziqi tsaftatacce mai amfani.
عَنْ إِسْحَاقَ بْنِ عَمَّارٍ قَالَ: قُلْتُ لِأَبِي عَبْدِ اللَّهِ ع الْحَدِيثُ الَّذِي يَرْوِيهِ النَّاسُ حَقٌّ أَنَّ رَجُلًا أَتَى النَّبِيَّ ص فَشَكَا إِلَيْهِ الْحَاجَةَ فَأَمَرَهُ بِالتَّزْوِيجِ فَفَعَلَ ثُمَّ أَتَاهُ فَشَكَا إِلَيْهِ الْحَاجَةَ فَأَمَرَهُ بِالتَّزْوِيجِ حَتَّى أَمَرَهُ ثَلَاثَ مَرَّاتٍ فَقَالَ أَبُو عَبْدِ اللَّهِ ع [نَعَمْ] هُوَ حَقٌّ ثُمَّ قَالَ الرِّزْقُ مَعَ النِّسَاءِ وَ الْعِيَال[5]
16-Alkafi da isnadinsa daga is'haq dan ammar ya ce: na cewa baban Abdullah (as) shin hadisin da mutane keta rawaitowa gaskiya ne cewa wani mutum ya zo wajen annabi ya kai kukan buqatarsa sai annabi ya umarce shi da yin aure, mutumin ya aikata, ya qara dawowa wajen annabi karo na biyu ya qara kai kukan buqatarsa annabi ya qara umartarsa da yin aure, ya maimaita hakan har karo na uku annabi dai yana qara umartarsa da aure ? sai baban Abdullah (as) ya ce: na'am gaskiya ne, sai ya ce: arziqi na tareda da mata da iyali.
Galibi cikin al'amarin aure shi ne daduwar arziqi, sai dai cewa a wasu kadan daga cikin lokuta wanda bai fiye afkuwa ba qaruwar arziqi kan kasance cikin rabuwar aure da saki, cikin misalin wannan sai akomar da al'amari ya zuwa annabi ko imami masana ga haqiqanin al'amurra, bai halasata ga wani mutum idan ya riski kunci cikin farkon rayuwarsa ta aure ya fara tunanin yin saki saboda wani nassi da ya ke da shi daga wani hadisi kwaya daya rak, saboda wannan hadisi bai iya jayayya da hadisai masu tarin yawa da suka zo suna ishara kan cewa aure yana qara arziq , saboda haka sai a lura.
عَنِ ابْنِ أَبِي لَيْلَى قَالَ حَدَّثَنِي عَاصِمُ بْنُ حُمَيْدٍ قَالَ: كُنْتُ عِنْدَ أَبِي عَبْدِ اللَّهِ ع فَأَتَاهُ رَجُلٌ فَشَكَا إِلَيْهِ الْحَاجَةَ فَأَمَرَهُ بِالتَّزْوِيجِ قَالَ فَاشْتَدَّتْ بِهِ الْحَاجَةُ فَأَتَى أَبَا عَبْدِ اللَّهِ ع فَسَأَلَهُ عَنْ حَالِهِ فَقَالَ لَهُ اشْتَدَّتْ بِيَ الْحَاجَةُ فَقَالَ فَفَارِق.[6]
17-Alkafi da isnadinsa daga baban laila ya ce : asim dan hamidu ya bani labari ya ce : na kasance wajen baban Abdullah (as) sai wani mutum ya zo wajensa ya gaya masa buqutarsa, sai ya umarce shi da yin aure, yace sai buqatar ta qara tsananta, ya qara zuwa wajen baban Abdullah(as) ya tambaye shi halin da ya ke ciki sai mutumin ya ce : buqatar ta tsananta kaina, sai imam ya ce: ka saketa.
18-daga baya mutumin ya zo wajen imam (as) imam ya tambayeshi halin da ya ke ciki, sai ya ce : nayi kudi halin da na ke ciki ya kyawunta, imam ya ce : haqiqa na umarce ka da al'amura biyu da Allah ya yi umarni da suوَأنكِحُوا الأيَامَى مِنْكُمْ (ku auri mata marasa miji daga gareku ) ya zuwa[7]وَاللهُ وَاسِعٌ عَلِيمٌ
Allah mayalwaci ne masani.
wata ayar kuma ya ce: وَإنْ يَتَفَرَّقَا يُغْنِ اللهُ كُلاّ مِنْ سَعَتِه[8]ِ (idan suka rabu Allah zai wadata kowannensu daga yalwarsa.