sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Labarun da ba tsammani

    Ubangiji ya azurta kwanakinku cikin tunawa da ranar da aka aiko annabi(s.a.w)

    Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

    Wasu `ya tsirarun abubuwa da ka gutsiro daga littafin(sima`u rasulil a`azam fil `kur`an)

    Tareda da alkalami sayyid adil alawi

    Manzon mafi girma cikin motsin al`umma:

    Idan manzon mafi karamci ya fuskanci wahalhalu daga jama’arsa sakamakon jahiltarsa da jahiltar matsayinsa madaukaki  cikin dukanin marhaloli da daurori  wadanda harkar muslunci ta gifta ta, babu banbanci ciin kasantuwarta gabanin aiko annabi ko bayan aiko shi ko kuma kafin hijra ko bayanta lokacin da yake araye ne ko bayan wafatinsa(s.a.w) lalle daga cikin abubuwan da suka biyo bayan wannan fakuwar saninsa ko ace gazawa ko kasawa wanda ya kai ga jahiltar girman matsayin annabin rahama da mtumtaka (s.a.w) da saninsa kamar yadda yake, musulmi sun koma baya sunci baya daga girmansu mai tushe da wayewarsu ta mutumtaka  wadda ta game duniya baki daya da falaloli da karamci da ilimi da fannoni, sai gaba da kiyayya da rigimgimun mazhabobi da kabilanci wanda suke da tushe na jahiliyar farko suka maye gurbi, sai ya zamanto karfinsu ya kau sun gaza samu nasara sun fadi jarrabawa  a fagagen cigaba da gabata har ta kai gab akin haure  da karnukansu masu yi musu aiki daga sarakuna da shugabanni sun samu iko kan wuyayensu, sai su kasnce suna kwashe dukiyarsu  suna shan jinanansu suna ci da guminsu su koma su raya kasashensu, su riketa matsayin taguwar da za ta kaisu ga manufofinsu da bukatunsu da maslahohinsu  da shirye shiryensu na mallake raunana cikin duniya baki daya  da kowanne irin yanayi ta kama.

    Babu wata al`umma da `daga ta kai ga gano martaba da matsayin manzo mafi girma a tsawon marhaloli da zamanunnuka da suka shude da gabata ballantana ace sun ka ga siffantuwa da dabi`unsa da sasanninsa  da dabakokinsa, wajibi kan kowanne musulmi ya san yadda annabi(s.a.w) ya rayu  da kuma tarihinsa  mai cike da haske da ayoyin rahama da da tausayi da soyayya da `kauna lalle ya kamata ya san mu’ujizarsa dawwamammiya wato `kur’ani mai girma, kai ya kamata ace ay san sahabbansa  wadanda sukai ma annabi(s.a.w) rakiya cikin halartuwarsa da tafiye-tafiyensa  kai cikin dukkanin marhalolin rayuwarsa, sun kasance batattun da ya shiryar da su cikinsu  akwai kunne da yake kiyayewa wanda shine sarkin muminai ali(as) lalle shi kamar yadda sukace shi aya ne daga ayoyin annabta annabi(s.a.w) alle shi ya kasance mu`ujiza ta biyu bayan kur’ani  mai girma wanda ke nuni zuwa ga gasgatar annabtarsa  da girman sakonsa ta yadda kimomi suka taso daga tarbiyarsa kamar misalign sarkin muminai ali(as).

    Mai karatu cikin rayuwar manzon rahama da sannu zai ga akwai wasu manyan mutane da suke kusa da manzon rahama kamar misalin ali(as) abu zar gifari da ammar ibn yasir da mikdadu kai hatta hadisi ya zo daga manzon Allah(s.a.w) yana cewa salmanu daga cikinmu yake mu ahlul –baiti . haka manzon rahama yana cewa lalle Allah yana shaukinsu  lalle aljanna ma tana shaukinsu, kadai dai sun samu wannan daukaka mai girma sabon sanin da sukaiwa manzon Allah(s.a.w) da sanin akamalrsa da kyawunsa basu taba yi masa jayayya ba kamar yadda wasu sukai cikin matsayarsa da hukuncinsa, su sun tsaya kyam tareda shi sakamkon karfafar imaninsu da shi  dakuma kasantuwarsa wajen shi bai Magana da son zuciya face abinda akai masa wahayi. Dayansu bait aba fadi kamar yadda wancan mutumin ya fadi lokacin da annabi(s.a.w) zai yi wafati da yace akawo mas alkalami dan tawada  da takarda domin ya rubuta musu wani abu da ba zasu bata a bayansa ba sai wannan mutum ya gane cewa annabi(s.a.w) yana ishara zuwa ga hadisin saklaini littafin Allah da tsatsonsa daga ahlul baiti wanda jagoransu ya kasnce sarki muminai ali(as) lalle manzon Allah(s.a.w)  ya furta wannan hadisi a wurare da daman gaske

    (إني تارک فيكم الثقلين كتاب الله وعترتي أهل بيتي ما ان تمسّكتم بهما لن تضلّوا بعدي أبداً وانهما لن يفترقا حتّى يردا عليّ الحوض

              Lalle ni mai barku muku nauyaya guda biyu ne littafin Allah tsatsona ahlul baiti matukar kunyi riko da su ba zaku taba bat aba bayana har abada lalle su biyun basu taba rabuwa da juna har sai sun gangaro wurina a tafki.

    Wannan ingantaccen hadisi ne mutawatiri daga dukkanin bangarori biyun shi’a da sunna. A wannan loakci sai wani mutum ya cewa manzon Allah(s.a.w) wai wannan mutumin ya zautu baya cikin hankalinsa wa’iyazubillahi daga wannan mumuna kalami nasa. Ina wannan mutumin za a hada shi da salmanu da misalsalinsa  daga zababbun sahabban annabi(s.a.w) masu girman daraja yardadddun Allah.

    Babu shakka cikin kasntuwar nesantarwa da kusantarwa cikin matsayin manzon Allah(s.a.w) sun rukunantar da gurabe bayyanannu  cikin mutanen da suka rayu da shi a kebance, haka da al`umma cikin gamewa duk wanda ya kasance mai adalci bai makantar da kansa cikin makauniyar biyayyar iyaye da sannan kuma zargin mai zargi bai da meshi ba lalle zai fuskanci wannan abubuwa da muka fadi zai dauketa a matsayin sako da nauyi dake rataye a wuyansa.

    Sai ta banbanta wurinsa da yanayin amsar da ya samu da sakamako bisa akidu da ka`idoji ingantattu da suka samu ingancins kan hsken kur’ani da ahlul baiti