■ DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN QAI
■ FASALI NA FARKO : MALHAMOMI NA FARI GAME DA
■ FASALI NA BIYU
KASHE-KASHEN DALILAN SHARI'A
SIRRIN IBADA DA HAJJI
ABUBUWA NA MUSAMMAN WADANDA SUKA KEBANTA GA KA'ABA DA AIKIN HAJJI.
SIRRIKAN HAJJI CIKIN TASFTACE ZUKATA
DAGA CIKIN SIRRAKAN AKWAI SIYASA DA ZAMANTAKEWA
DAGA CIKIN SIRRIKAN HAJJI NA IRFANI
Daga cikin muhimman sirrikan irfani a cikin hajji:
NAU'O'IN HAJJI DA BA'ARIN SIRRI CIKIN MUQADDIMARSA
■ DAGA FALSAFAR HAJJI CIKIN ALQUR'ANI
■ DAGA CIKIN SIRRIN AYAR HAJJI
■ KUFAIFAYIN HAJJI DA UMARA CIKIN DUNIYA DA LAHIRA KAMAR YADDA YA ZO CIKIN HADISAI
■ JIKKANTUWAR HAJJI GA ASALAN ADDINI
■ HAJJIN JAZZURU(RAQUMI) DA HAJJIN USFURI(TSATSTSEWALA
■ FASALI NA HUDU
■ DAGA SIRRIKAN HARAMIN MAKKA
■ Daga cikin sirrikan miqatai
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MAKKA MAI KARAMACI DA MASALLACIN HARAMI
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN DAKIN KA'ABA MAI DARAJA
■ DAGA SIRRIKAN DUTSEN HAJARUL ASWAD
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MUQAMU IBRAHIM
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN HADIMU DA WANDA AKE LAZIMTA
■ DAGA CIKIN SIRRKAN HAIMA (DAKIN) ISMA'IL(AS)
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MUSTAJAR DA RUKUNUL YAMANI
■ DALILIN SHAFAR RUKUNUL YAMANI
■ FALALAR MUSTAJAR DA LADUBBANSA
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN RIJIYAR ZAMZAM
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN DUTSEN SAFA DA DUTSEN MARWA
■ SIRRIKAN HAJJI WAJEN IMAMU SADIQ(AS)
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MIQATI
■ FASALI NA BIYAR
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN HAJJI
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN TALBIYYYA(FAXIN LABBAIKA
■ DAGA SIRRIKAN BARIN ABUBUWAN DA AKA HARAMTA
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN XAWAFI
■ DAGA CIKIN FALSAFAR XAWAFI
■ Daga cikin falsafar xawafin nisa'i
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN SALLAR XAWAFI
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN SA'AYI
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN SIRRIKAN SAISAYE DA ASKI
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN TARWIYYA
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN ARAFAT
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MAHS'ARUL HARAM
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN MINA
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN JIFAN JAMARAT
■ DAGA CIKIN SIRKAN HADAYA
■ DAGA CIKIN SIRRIKAN IBADUN CIKIN HAJJI
■ FASALI NA SHIDA
■ ku cika hajji da umara
■ XAWAFIN BANKWANA DA LADUBBANSA
■ KARBUWAR HAJJI DA HASKENSA
■ ADADIN HAJJIN DA ANNABI YA YI DA UMARARSA
■ HAJJIN ANNABAWA
■ TSUGUNARWAR DA IBRAHIM (AS) YA YIWA XANSA DA MATARSA A GARIN MAKKA
■ XAGA HARSASHIN GININ XAKIN KA'ABA DA HANNUN IBRAHIM DA ISMA'IL(AS)
■ QISSAR YANKAN IBRAHIM GA XANSA ISMA'IL{AS}
■ KHATMA
■ CIKIN ZIYARAR ANNABI MAFI GIRMA MUHAMMADU DA IYALANSA TSARKAKA.
■ DAGA CIKIN LADUBBAN BIRNIN MADINA HASKAKKA.
■ DAGA CIKIN FALALOLIN ZIYARA DA SIRRIKANTA
■ DANGANTAKAR MANZON ALLAH(S.A.W) DA AL'UMMA
- KIBIYOYIN RADDI KAN WUYAN WAHABIYAWA
- CIKIN HALLARAR ALHERI
- HUJJOJIN HALASCIN YIN TAKIYYA A MUSLUNCI DAGA MAHANGAR MANYAN MALAMAI GUDA BIYU
- FARKAR DA MAI BACCI CIKIN TABBATUWAR GANIN IMAM KA'IM A.S
- ALAMOMIN ANNABI CIIKIN KUR'ANI MAI GIRMA
- HAKURI DA FUSHI
- Bada'u tsakanin hakika da kagen makiya
- FALALAR DAREN LAILATUL KADRI
- WAHABIYANCI A TSAKANIN GUDUMA DA
- HASKEN SASANNI CIKIN SANIN ARZIKI
- AQIDUN MUMINAI
- FATIMA TAGAR HASKAYE
- SIRRIKAN AIKIN HAJJI DA ZIYARA
- TARBIYYAR IYALI A MAHANGAR ALKUR'ANI DA AHLULBAITI
da sunan Allah mai rahama mai jinqai
lallai garin makka na muqami da matsayi maxaukaki cikin isar saqon sama da yake zuwa daga Allah maxaukaki, daga xakin ka'abarta a ka shimfixa qasa shimfixawa, tarihinta na komawa ga adamu, haramin maka ya tattaro sirrika : haramin makka na da ladubba da hukunce-hukunce cikin addinin Allah madaidaici.
1 daga addu'ar Ibrahim(as) cikin faxinsa maxaukaki:
(وَإِذْ قالَ إِبْراهيüمُ رَبِّ اجْعَلْ هذا بَلَداً آمِناً)[1]
Sa'ilin da Ibrahim ya ce ya ubangiji ka sanya wannan gari ya kasance aminci.
Haramun ga mahajjaci ya xauki makami cikin amintaccen harami, lallai garin maka shi ne uwa ga alqaryu gari mai albarka, ana karkato da dukkanin nau'in `ya`yan itace gareshi wanda hakan arziqi ne daga wajen ubangijin talikai, lallai Allah ya gabatr da aminci cikin karkato da `ya`yan itace daga kayan marmari da makamantansu daga sinadarn tattalin arziqi, domin su san cewa aminci shi ne asasi cikin komai
(أَوَلَمْ نُمَكِّن لَهُمْ حَرَماً آمِناً يُجْبَى إِلَيْهِ ثَمَرَاتُ كُلِّ شَيْءٍ رِزْقاً مِن لَدُنَّا)[2]
Ashe ba mu hore musu harami amintacce ba da ake karkato da dukkanin kayan marmari gareshi arziqi daga garemu.
Aminci shi ne tushe da asasin tattalin arziqi da habbaka da cigaba, sannan ita addu'a Ibrahim ta kasance ga aminci harami, amma amincin xakin ka'aba a kankin kanta lallai shi ya kasance tun zamanin adamu.
(مَثابَةً لِلنّاسِ وَأَمْناً( [3]
Makoma ga mutane da aminci.
Amma amincin tsarin halitta haqiqa ya zo cikin faxinsa maxaukaki:
(وَمَن دَخَلَهُ كَانَ آمِناً) [4]
Duk wanda ya shiga cikinsa zai kasance cikin aminci.
(أَطْعَمَهُم مِن جُوعٍ وَآمَنَهُم مِنْ خَوْفٍ )[5]
Wanda ya ciyar da su daga yunwa ya amintar da su daga tsoro.
(أَوَلَمْ نُمَكِّن لَهُمْ حَرَماً آمِناً)[6]
Ashe bamu hore musu harami amintacce ba.
(أَنَّا جَعَلْنَا حَرَماً آمِنا)ً[7]
Lallai mu mun sanya harami amintacce.
2 amincin shari'a da amincin tsarin halitta na xabi'a:
Daga cikin amincin shari'a shi ne bayyanr da muslunci na gaskiya haqiqa ya zo cikin hadisi mai daraja cewa:
«من دخل الحرم من الناس مستجيراً به فهو آمن ، ومن دخل البيت مستجيراً به من المذنبين فهو آمن من سخط الله، ومن دخل الحرم من الوحش والسباع والطير فهو آمن من أن يُهاج أو يؤذى حتّى يخرج من الحرم » . [8]
Duk wanda cikin mutane ya shiga harami ya na neman mafaka da taimako da shi daga masu zunubai lallai shi zai amita daga fushin Allah, duk dabbar da ta shiga haram daga sakaye da tsuntsaye lallai suna cikin aminci daga afka musu ku cutar da su har lokacin da za su fita daga cikin haramin.
Wannan xaki Allah ya sanya amintacce a xabi'ane da shari'ance, sai dai idan mutane sun kafircewa ni'imar Allah to lallai zai kwace wannan aminci daga garesu:
(وَضَرَبَ آللهُ مَثَلاً قَرْيَةً كَانَتْ آمِنَةً مُّطْمَئِنَّةً يَأْتِيهَا رِزْقُهَا رَغَداً مِن كُلِّ مَكَانٍ فَكَفَرَتْ بِأَنْعُمِ آللهَ فَأَذَاقَهَا آللهُ لِبَاسَ آلْجُوعِ وَآلْخَوْفِ بِمَا كَانُوا يَصْنَعُونَ.( [9]
Allah ya buga misali da wata alqarya da ta kasance cikin aminci arziqinta a yalwace na zuwar mata ta kowanne waje sai ta kafirce da ni'imomin Allah sai Allah ya xanxana mata tufafin yunwa da tsoro bisa abin da suka kasance suna aikatawa.
3 cikin tawilin faxinsa maxaukaki
(وَمَنْ دَخَلهُ كانَ آمِناً) قال الامام الصادق 7: «ومن دخله وهو عارف بحقّنا كما هو عارف له خرج من ذنوبه ، وكفى همّه الدنيا والآخرة[10] » .
Duk wanda ya shiga ciknsa zai kasance cikin aminci, imam sadiq(as) duk wanda ya shiga ciknsa ya na halin sanin haqqinmukamar yadda ya kasance yana saninsa zai fita daga zunubinsa, zai ije damuwarsa duniya da lahira.
ـ (سِيرُوا فِيهَا لَيَالِيَ وَأَيَّاماً آمِنِينَ )[11] عند احتجاج
الامام الصادق 7 مع أبي حنيفة قال : «مع قائمنا أهل البيت
4 Cikin faxinsa maxaukaki: ku yi tafiya cikinta darare da amintattun kwanaki. Lokacin da imam sadiq(as) yake kafawa abu hanifa hujja, sai ya ce masa: ma'ana tare da mai tsayuwar mu ahlul baiti.
Amma cikin faxinsa maxaukaki:
(وَمَنْ دَخَلهُ كانَ آمِناً)
Duk wanda ya shiga ciknsa ya kasance amintacce.
Duk wanda ya yiwa imam mahadi mubaya'a ya shiga tare da shi ya shfa hannunsa ya shiga cikin qullar abokansa zai kasance cikin aminaci a xabi'ance ma'ana amincin shari'a da na tsarin halitta.
ـ (وَمَن يُرِدْ فِيهِ بِإِلْحَادٍ بِظُلْمٍ نُذِقْهُ مِنْ عَذَابٍ أَلِيمٍ )[12]
5 Duk wanda ya nui karkata ciknsa da zalunci zamu xanxana masa azaba mai raxaxi.
Ba'arin waliyyai sun kasance suna shinge da garkuwa da zaunar da shi cikin makka qaqqarfar garkuwa daga zalunci da munana ladabi, za a xanxanawa azzaluni azabar mai girma da xaukaka.
قال رسول الله 6: «إنّ مكّة بلد عظمة الله وعظم حرمته ، خلق مكّة وحفّها بالملائكة ، قبل أن يخلق شيئاً من الأرض يومئذ كلّها بألف عام».
6 Manozn Allah(s.a.w) ya ce: lallai makka gari ne da ke nuna girman Allah, kumalfarmar garin ta girmama, Allah ya halicci makka ya kewayeta da mala'iku gabanin halittar wani abu a ban qasa da shekara dubu.
قال الامام الباقر 7: «النائم ببكّة كالمتهجّد في البلدان »
7 Imam baqir(as) ya ce: wanda yay i bacci makka kamar misalign wanda ya raya darensa ne da ibada a ragowar garin da bakkatu ba (makka).
Ma'ana misalinsa kamar misalign wanda yay i tayin sallah da daddare ma'ana yana da ladan mai tsayuwar dare, ya kake tsammanin wanda kuma ya raya dararensa cikin makka?
ـ قال الامام الصادق 7: «أحبّ الأرض إلى الله تعالى مكّة ، وما تربة أحبّ إلى الله عزّوجلّ من تربتها، ولا حجر أحبّ إلى الله عزّوجلّ من حجرها، ولا شجر أحبّ إلى الله عزّوجلّ من شجرها، ولا جبال أحبّ إلى الله عزّوجلّ من جبالها، ولا ماء أحبّ إلى الله عزّوجلّ من مائها.
Imam sadiq(as) ya ce: mafi soyuwar qasa zuwa ga Allah garin makka, babu wata turbaya da tafi soyuwa ga Allah daga turbayar makka, babu wani dutse da yafi soyuwa ga Allah maxaukaki daga dutsen makka, babu wata bishiya da ta fi soyuwa ya zuwa Allah maxaukaki daga bishiyar garin makka, babu wani babban dutse da yafi soyuwa ga Allah maxaukaki daga dutsen makka, babu wani ruwa da yafi soyuwa ga Allah maxaukaki daga ruwan garin makka.
9- sunan yanka na garin makka mai karamci ya zo a wuri xaya cikin qur'ani mai girma, sai dai kuma makka da zo a qur'ani da sunaye daban daban da laqubba kamar misalin: bakka, ummul qura, balad, baladul amin, baldatu, alharam, alqarya, wadi gairu zi zar'in, haka Karin kan waxannan sunaye ya zo cikin hadisai masu daraja kamar: basasatu, ummu Rahim.
10 sunan makka a luggance na nufin yalwar qasa, sannan an tsagota daga fito da tafi da masu ziyartarta suke a jahiliya.
11- daga cikin sunayenta, ma'adu, salah, kausar, haximatu, ra'asu, qadis da sauransu wanda adadin ya kai sunaye talatin me yiwa yawaitar wannan sunaye gareta na da dangantaka da muhimmancinta wajen qabilun larabawa.
ـ عن الامام الصادق 7: «إنّما سمّيت مكّة بكّة لأنّ الناس يتباكون فيها».
12 imam sadiq(as) kaxai dai abin da ya sanya ake kiran makka da sunan bakka saboda mutane suna koke koke cikinta.
ـ عن الامام الكاظم 7: «لأنّ الناس يبکّ بعضهم بعضاً بالأيدي ولا يكون إلّا في المسجد حول الكعبة ».
Daga imam kazim(as) saboda lallai mutane suna tunkuxe ba'arinsu da ba'ari da hannuwa face cikin masallacin ka'aba.
ـ وسئل أميرالمؤمنين 7 لم سمّيت مكّة اُمّ القرى ؟ قال : «لأنّ الأرض دُحيت من تحتها[13]
14 an tambayi sarkin muminai Ali(as) me yasa ake kiran makka da sunan uwar alqaryu? Sai ya ce: saboda an shimfixa qasa daga qarqashinta.
ـ وعنه 7 :«سمّيت بكّة لأنّها أبكت عيون الجبّارين والمذنبين».
Daga gareshi(as) an kira maka da bakkatu saboda ta sanya idanuwa jabberai da masu zunubai kuka
ـ وعن الباقر 7: «إن بكّة موضع البيت وإنّ مكّة الحرم وذلک قوله تعالى : (مَنْ دَخَلَهُ كانَ آمِناً).
16 Daga imam baqir(as) lallai bakka shi ne wurin da ginin ka'aba ya ke, sannan makka iat ce harami saboda faxinsa maxaukaki: duk wanda ya shiga cikinsa ya kasance cikin aminci.
17 Allah ya sanya xaki mai alfarma makoma ga mutane ma'ana mafaka wurin tuba shingen bakin gaba mabubbuga wajen sha, waxannan ma'anoni suna gasgatuwa cikin ziayartar xakin Allah mai alfarma domin aikin hajji. Kamar yadda manufar xakin mai alfarma wanda ya ke makka shi ne ya kasance tsari da shiriya da albarka ga mutane, sannan manufar dukkanin waxannan abubuwa shiu ne tarbiyantar da mutum da tsarkake shi da kamalarsa cikin sanin kansa da ubangijinsa, wannan ya tattro dukkanin mutane b atre da ware wasu ba, abin da ake nufi da tsanin hajji shi ne kaiwa ga hadafin da ake cigiya da nema, ita ka'aba it ace xaki kwaya xaya rak da dukkanin mutane ke nufarta suyi xawafi daura da ita domin su halarci alfanun duniya da lahira su ambaci sunan Allah cikin sanannun kwanaki qididdigaggu domin su runu da rinin Allah, me ya kyawu daga rinin Allah, sai mhajjaci ya kasance na Allah a dukkanin fagen rayuwarsa, mai koyo domin tsira, masanin Allah wanda ke koyawa mutane Alheri.
الكافي بسنده عن حسان بن مهران قال : سمعت أبا عبدالله 7 يقول : «قال أميرالمؤمنين صلوات الله عليه : مكّة حرم الله، والمدينة حرم رسول الله 6، والكوفة حرمي لا يريدها جبّار بحادثة إلّا قصمه الله[14] .
18 alkafi da isnadinsa daga Hassan ibn mihran ya ce: naji baban Abdullah(as) yana cewa: sarkin muminai ali(as) ya ce: garin makka haramin Allah ne garin madina kuma haramin manzon Allah ne, garin kufa haramina ne, babu wani jabberi da zai nufeta da wata musiba face Allah ya karya shi.
مكّة مقصد الموحّدين : فمن أحبّ الله يهوى مكّة وزيارة بيته الحرام ، كما يهوي ويأنس الطفل بثدي اُمّه
19- makka wurin nufin masu tauhidi: duk wanda ya ke son Allah zai yi begen makka kamar yadda yaro ke bege da xebe haso da nonon mahaifiyarsa.
قال الامام الرضا 7: «سمّيت مكّة مكّة لأنّ الناس كانوا يمكّون فيها، وكان يقال لمن يقصدها قد مكا».
Imam rida(as) an kira makka da sunan makka saboda mutane suna fito da ihu cikinta, ana cewa wanda ya nufeta da haqiqa shi ya yi ihu.
20- makka matsallaka da hanya don ketaerawa a kai ga haxuwa da ubangiji, ba wuri ne na zaman duniya ba, lallai zama cikin makka na qeqasar da zuciya kamar yadda ya zo cikin hadisi daga imam sadiq(as)
قال الامام الباقر 7: «لا ينبغي للرجل أن يقيم بمكّة سنة » قلت : كيف يصنع ؟ قال : «يتحوّل عنها . [15]
21 Daga imam baqir(as) bai kamata wani mutum ya zauna cikn garin makka ba har ts.a.won shekara guda, sai ta qaqa zai yi kenan? Sai imam ya ce ya juya ya barta.
Makka tsuhe da asalin alherai aban qasa, lallai an shimfixa qasa adaga qarqashinta uwar alqaryu. Ana amfani da sunan uwa ga dukkanin abin da ke da asali wanda me nufa ke nufarsa, idan alqaryu da birane suka kasance masdarin alheri da albarka, uwar alqaryu makka it ace asalin duk wani alheri.
22 makka matattara masu tauhdi masu xanyta Allah cikin mafi kyawun sura, lallai ita an kira da sunan{bakka} saboda mutane suna ingiza ba'arin da ba'ari da hannuwa su tura sashensu da sashe domin kaiwa ga tushen tauhidi jagabansa.
23 makka mabayyanar qasqantar azzalumai, duk wanda ya nufeta da zalunci da qiyayya Allah zai wulaqanta shi ya kunyata shi ya tanadar masa azaba mai raxaxi, kamar yadda ya kasance cikin hikayar mutane abrahata najjashi.
عن الامام الصادق 7: «أسماء مكّة خمسة : اُمّ القرى ومكّة وبكّة والبساسة كانوا اذا ظلموا بها بسّتهم ، أي اخرجتهم وأهلكتهم ، واُمّ رحم كانوا اذا الزموها رحموا[16] .
An karbo daga imam sadiq{as} sunayen ka'aba biyar ne: ummul qura,makka, bakka, albasasatu sun kasance idan suka aikata zalunci cikinta sai ta fito da su ta halakar da su, ummul Rahim, idan suka lazimceta sai ya yi musu rahama.
وفي الحديث : «وكانت تسمّى بكّة لأنّها تبکّ أعناق الباغين اذا بغوا فيها».
Ya zo cikin hadisi{ana kiran makka da bakka saboda ta na ragargaje wuyan azzalumai cikinta.
24 makka qasar hatta wanda ke hutawa cikinta daga ibada ana rubuta masa ladan ibada.
عن الامام الصادق 7: «إنّما سمّيت مكّة بكّة لبكاء الناس حولها وفيها».
25 an karbo daga imam sadiq{as} kaxai dai ana kiran makka da sunan bakka saboda kukan da mutane keyi daura da ita
عن الامام الباقر 7: «الساجد بمكّة كالمتشحّط بدمه في سبيل الله».
An karbo daga imam baqir{as} mai sujjada cikin makka kamar wanda ya jike da jininsa ne cikin tafarkin Allah.
عن الامام السجّاد 7: «من ختم القرآن بمكّة لم يمت حتّى يرى رسول الله6 ويرى منزله في الجنّة
An karbo daga imam sajjad{as} duk wanda ya sake qur'ani a garin makka ba zai mutu har sai ya yi ido biyu da manzon Allah kuma zai ga masaukinsa na aljanna tuna nan duniya.
وقال 7: «النائم بمكّة كالمتشحّط في البلدان ».
Ya ce: mai barci a garin makka kamar mai rarrauwane cikin garuruwa.
25 makka na gina mutum da tarbiyantar da zukata, lall tsananin rayuwa na sirikantar mutum domin kubuta daga datti sai ainahin zinariyarsa ta bayyyana, lallai su mutane ma'adanai ne kamar ma'adanan zinariya da azurfa.
قال رسول الله 6: «من مرض يوماً بمكّة كتب الله من العمل الصالح الذي كان يعمله عبادة ستين سنة ، ومن صبر على حرّ مكّة ساعة تباعدت عنه النار مسيرة مأة عام ، وتقرّبت منه الجنّة مسيرة مأة عام[17]
Manzon Allah{s.a.w} ya ce: duk wanda ya yi rashin lafiyar kwana xaya a garin makka Allah zai rubuta masa aladan aiki nagari wanda zaiyi cikin ibadar shekaru sittin, duk wanda yay i haquri ya jurewa zafin ranar garin makka ts.a.won xan qanqanin lokaci wuta za ta nesanta daga gareshi ts.a.won tafiyar shekaru xari.
26 makka garin tsarkaka: Allah ya yi Magana daa Ibrahim da isma'il yana ma ice musu:
(طَهِّرَا بَيْتِيَ لِلطَّائِفِينَ وَآلْعَاكِفِينَ وَآلرُّكَّعِ آلسُّجُودِ)[18]
Ku tsarkake xakina ga masu xawafi da zama ciki da masu ruku'I da sujjada.
Ya kamata ga mahaajjaci mumini da mahajjaciya mumuina da ka da su kuskura su shigaa garin makka face suna cikin tsarki na zahiri da baxini
قال الامام الصادق 7: «فينبغي للعبد أن لا يدخل مكّة إلّا وهو طاهر قد غسل عرقه والأذى وتطهّر»
Imam sadiq{as} ya ce: ya kamata ga bawa ka da ya kuskura ya shiga makka face ya na cikin tsarki haqiqa ya wanke gumunsa da ciwo ya kuma tsarkaka.
Saboda mustahabbi ne mutum yay i wanka domin shiga haramin makka kamar yadda ya kamata ya tsarkake ruhinsu daga dukkanin qazantar munanan halaye kamar girma kai da jiji da kai da riya.
قال الصادق 7: «من دخلها بسكينة غفر له ذنبه » قلت : كيف يدخل بسكينة ؟ قال : «يدخلها غير متكبّر ولا متجبّر».
Imam sadiq{as} ya ce: duk wanda ya shiga garin makka cikin nutsuwa Allah zai gafarta masa zunubansa, sai aka tambayi imam qaqa zai shiga ckinta da nutsuwa? Sai ya ce: ya shigeta ba tare da yana mai girma kai ko jabberi.
27 garin makka nada kebantacciyar alfarma, lallai ita makka haramin Allah ne duk wanda ya cutar cikinta lallai ya aikata babban laifi kuma Allah ya tanadar masa azaba mai raxaxi
(وَمَن يُرِدْ فِيهِ بِإِلْحَادٍ بِظُلْمٍ نُذِقْهُ مِنْ عَذَابٍ أَلِيمٍ )[19] .
Duk wanda ya nufeta da karkata da zalunci zamu xanxana masa azaba mai raxaxi.
28 makka garin kowa da kowa, garin `yanci ga dukkanin musulmi da xaketa matsayi gida babu wanda ke da haqqin hana shi.
قال رسول الله 6: «مكّة مناخ لاتباع رباعها ولا تؤاجر بيوتها» . [20]
Manzon Allah{s.a.w}ya ce: makka madurqusa ce ga raquman baqi gidan kowa da kowa ce ba 'a bada hayar gidajen cikinta.
Sarkin muminai aliyu{as} ya rubuta wasiqa ga gwamnansa na garin makka mai karamci:
«مُرّ أهل مكّة إلّا يأخذوا من ساكن أجراً، فان الله سبحانه يقول : (سَوَاءً آلْعَاكِفُ فِيهِ وَآلْبَادِ)[21] فالعاكف
المقيم والبادي الذي يحجّ إليه من غير أهله ، وفقنا الله وإيّاكم لمحابّه والسلام[22]
Ka umarci muatanen makka da ka da su karbi lada ga wanda ke zama cikinta, lallai Allah matsarkaki yana cewa: babu banbanci cikinsa tsakanin mazauni da baqauye.
Baqauye shi ne wanda zai zo hajji makka wanda shi ba xan asalin garin bane, Allah ya datar dani da ku ga soyayyarsa wassalam.
Qasar makka na daga dukiyar da kowa da kowa ke da haqqi ciki sai al'amarinta na hannun imamin musulmi zai gabatr da abin da ke ciknta daga maslahar musulmai, alfanun makka na komawa ga dukkanin musulmi.
Bai halasta ga wanda zai yi aikin hajji ya shiga garin makka mai karamci ba tare da ya xaura harami ba daga xaya daga cikin wuraren xaura harami shida (miqatai) guda biyar cikin miqatan tuni manzon Allah(s.a.w) ya bayyana su, kamar yadda ya zo cikin hadisin imam sadiq(as)
«الإحرام من مواقيت خمسة وقّتها رسول الله 6 لا ينبغي لحاج ولا لمعتمر أن يحرم قبلها ولا بعدها، ووقّت لأهل المدينة (ذا الحليفة ) وهو (مسجد الشجرة )، يصلّي فيه ويعرض الحجّ ، ووقّت لأهل الشام (الجُحفة )، ووقّت لأهل النجد وادي العقيق ووقّت لأهل الطائف (قرن المنازل ) ووقّت لأهل اليمن (يلملم[23]
Ihrami na daga cikin miqatai biyar da manzon Allah ya yi bayaninsu.bai kamata mahajjaci ko mai umara ba ya sanya ihrami gabanin isa garesu ko bayansu, ya bayyana zu hulaifa a matsayin miqatin mutanen madina wan shi ake kira da sunan masjidul shajara mahajjaci zai sallah cinsa sannan ya nufi hajji. Na biyu: ya bayyana juhufa a matsayin miqatin mutane sham, na uku ya bayyana wadi aqiqqu ga mutanen najad. Na huxu: ya bayyana qarnul manazil ga mutanen xa'if, na biyar ya bayyana yalamlam ga mutanen yaman.
Sannan an sanyawa mutanen makka miqatinsu a kebance
. فعن الامام الصادق 7 : «من أراد أن يخرج من مكّة ليعتمر أحرم من الجعرانة والحديبيّة أو ما أشبهها
An karbo daga imam sadiq(as) duk wanda yay i nufin fitowa daga garin makka domin yin umara to ya xaura ihrami daga ja'aranatu da haudaibiyya ko makamantansu.
Ga wanda yay i nufin ihramin hajji tamattu'I daga makka mai karamci, lallai hadisi mai daraja ya zo:
قلت لأبي عبدالله 7 من أين أهلّ بالحجّ ؟ فقال : «إن شئت من رحلک ، وإن شئت من الكعبة ، وإن شئت من الطريق وتحت الميزاب وفي حجر إسماعيل أفضل ».
Na tambayi baban Abdullah(as) daga ina hajji zai fara? Sai imam ya ce: idan kaso daga sirdinka, ko kuma daga ka'aba, ko kuma idan kaso daga kan hanya qarqashin indararo cikin dutesn isma'il ya fi falala
وفي الحديث الشريف عن الامام 7: «من تمام الحجّ والعمرة أن تحرم من المواقيت [24]
Ya zo cikin hadisi mai daraja daga imam(as) cewa: daga cikin cikar hajji da umara shi ne xaura harami daga miqatai.
Y6a kasance miqati ga mutanen Iraqi gabanin kasantuwar Iraqi qasar musulmai.
قال الصادق 7 : «فانّه وقت لأهل العراق ولم يكن يومئذ عراق[25]
Imam sadiq(as) ya ce: lallai shi ya bayyana Iraqi miqatin mutanen Iraqi tun gabanin kasantuwar Iraqi.
Wannan na daga mu'ujizar addini yin ishara ga abu gabanin samuwar ahalinsa, bai halasata ketara miqati face cikin ihrami ga waxanda suka nufi shiga harami mai daraja.
Sannan shi miqati a luggance: suna ne na lokacin aiki ko suan ga wuri bigire, sannan ma'anarsu ta ayyanu cikin isxilahi da hannun mai shari'antawa matsarkaki.
Kowanne miqati na da sirri da ke komawa ga Allah matsarkaki kamar yadda hakan ya zo cikin miqatin masijidil shajara(zil hulaifa) lallai lokacin da annabi ya je isra'I daren mi'iraji daga masallacin harami zuwa masallacin aqsa ya yin da ya giftawa ta zil hulaifa Allah ya kira shi ya ce ya muhammadu, sai annabi ya ce: labbaika, sai Allah matsarkaki ya ce: ashe ban sameka maraya ba sai ya kusanto da kai, ya sam,eka mai batan hanya ya shiryar da kai, sai annabi ya ce: lallai dukkanin godiya da ni'ima ta tabbata gareka mulki gareka ya u abokin tarayya gareka.[26]
Sannan asalin miqati na komawa ga adamu(as) lallai shi ya yin saukarsa tare da hauwa'u ya zuwa ban qasa zuciyarsa ta yi begen aljanna, sai Allah ya aiko masa da dutsen yaqutul hamra'au da farar lu'ulu'u daga aljanna sai ta haskaka adamu da hauwa'u da dukkanin abin da ked aura da shi, haskneta ya fantsama ya yaxu zuwa ga kwazazzabai da kurmi, sai Allah ya bashi labari cewa wannan lu'ulu'u na da alfarama, ba mai shigarta sai wanda xaura mata harami sannan alfarmarta gwargwadon haskenta, daga nan miqatai suka sassaba ta yanayin nisan hanya bisa sassabawar haskakarta ya yaxuwarsa da fantsamarsa daga tudun qasa da kwari ba'ari ya kusanta ga ka'aba ba'ari ya nesanta da ita kamar yadda tsakanin makka da madina.
عن الامام الرضا 7: «إنّ الله عزّوجلّ لمّا اهبط آدم من الجنّة هبط على أبي قبيس ، فشكا إلى ربّه الوحشة ، وأنّه لا يسمع ما كان يسمعه في الجنّة ، فاهبط الله عزّوجلّ عليه ياقوتة حمراء فوضعها في موضع البيت فكان يطوف بها آدم ، فكان ضوءها يبلغ موضع الاعلام ، فيعلم الأعلام على ضوئها وجعله الله حرماً.
An karbo daga imam rida(as) lallai Allah mai girma da xaukaka yayain da ya sauko da admu daga aljanna ya sauka kan dutsen abu qabisu sai ya kai kukan kaxaita ga ubangijinsa ya bayyaa cewa shi bai jin sautin da ya kasance yana jinsa a aljanna, sai Allah ya saukar masa yaqutul hamra'I ya sanya matsugunin xakin ka'aba adamu ya kasance yana xawafi daura da ita, haskenta ya kasance yana kaiwa ga manya manyan duwatsu sais u sanar da haskenta sai Allah ya sanya shi harami.
Daga cikin sirrikan miqatai:
1 – mahalli da waje ga amsa kiran Allah matsarkaki da kaiwa ga kebantacciyar rahamarsa.
Lallai ahajjci da mahajjaciya cikin tsayuwarsu a miqati da xaura haraminsu suna shiri da xaura xamara don amsa kiran Allah domin su isa ga kebantacciyar rahamarsa.
Kamar yadda miqati ya kasance shiri da xaura xamara ga annabi musa(as) domin zabensa da saqon Allah da kamalarsa,
(يا موسى إنّي آصْطَفَيْتُکَ بِرِسالاتِي وبِكَلامي )[27]
Ya musa lallai ni na zabeka da saqona da kalamina.
To haka miqati yake ga mahajjaci.
2- mashiga ta farko domin shiga da gangara hajji da haramin Allah
Sakamaon kasantuwar mahajjata baqin liyafar Allah mai rahama, lallai duk mutumi da ya je umara ko hajji ya halarci liyafar Allah. Dukkkanin liayafa na da ladubbanta da sunnoninta, daga cikin ladubban liyafar uabangiji mai rahama shi ne mahalrata liayafa liyafar su shiga liayafa ta qofar da aka umarce su.
(لَيْسَ آلْبِرُّ بِأَن تَأْتُوا آلْبُيُوتَ مِنْ ظُهُورِهَا وَلَكِنَّ آلْبِرِّ مَنِ آتَّقَى وَأْتُوا آلْبُيُوتَ مِن أَبْوَابِهِا)[28]
Bai cikin addini ku jema qofa daga bayansa, sai dai addini nag a wanda ya yi taqawa, ku jema gidaje daga qofofinsa.
Ya kasance wajibi kan dukkanin mai halartar liyafa ya tsaya a miqati don neman izinin shiga liyafa, faxin labbaika ba komai bace face sallama don shiga liyafa, xaura ihrami ba komai bane face tufafin shiga liyafar ma'anawiyya, haka lamarin yake cikin ragowar ayyukan mustahabbi a miqati ababen da aka haramta cikin ihrami, ka ka ce yana koyar mai halartar liyafa yaya zai fusaknci wanda ya shirya liyafa, hakan lamarin yake cikin kowacce daula yn ziyarar shugabanta mai mulkarta, alle akwai wasu ladubba kebantattu ga dukkanin wanda zai ziayrci sarki da shugaba dole ne ya kiyaye dokoki da ladubba da ala'adu da suka kebantu da wannan shugaba.
3 kiyaye alfarmar harami da girmama haramin ubangiji.
عن الامام الصادق 7: «وجب الاحرام لعلّة الحرم ».
Daga sadiq(as) girmamawa ta wajabta ne sakamokn haramin.
وقال 7: «من تمام الحجّ والعمرة أن تُحرم من المواقيت »
A wani gurin imam(as) ya ce: daga cikin cikar hajji da umara shi ne xaura harami daga miqati.
Miqati zai qara sanya maka shauki cikin zuciyarka da begen saduwa da ubangijin talikai cikin xakinsa mai alfarma maxaukaki wanda ya fifita da karama da tsarkaka da tsaftar ruhi, ya kamat ga dukkanin wanda ya nufe shi ya ziyarci xakinsa da yay i wanka gabanin xaura ihrami sanan ya xaura ihramin daga miqati bayan ya idar da sallar xaura ihrami raka'a shida idan xaura ihraminsa bai kasance bayan sallar wajibi ba, ya xaura ihrami daga farin tufafi tsarkakakke tsaftatacce na halal, bayan yak wabe tufafinsa sai ya quduri niyyar fita daga dukkanin zunubi da sabo.
4 – miqati mahalli ne na tattunawa tsakanin bawa da ubangijinsa.
Ubangiji matsarkaki bayan tattaunawarsa tare da musa ya na cewa:
(وَلَمَّا جَاءَ مُوسَى لِمِيقَاتِنَا وَكَلَّمَهُ رَبُّهُ ) [29]
Ya yin da musa ya je miqatinmu ubangijinsa ya tattauna da shi.
Miqati ya kasance mahallin tattaunawa tsakanin mai gida da bawa tsakanin xan aike da wanda ya aiko shi, tsakanin masoyi da wanda yake so, tsakanin mai bege da wanda yake bege da qauna
(عجلت ربّي لكي ترضى ).
Na gaggauta gareka ubangijina domin neman yardarka.
Cikin miqati tafiye tafiyen kyawawan xabi'u da irfani ke tajalli.
Lallai shi matafiyi ya zama dole ya farka duk wanda ya kasance cikin barci da gafala da rafkana, lallai shi an xauke masa alqalami ba da shi ake Magana ba, saboda ya zama tilas a farka a waye , wannan shi e abin da ke tabbatuwa a miqati, da cewa mutum zai tambayi kansa ina nake ne yanzu? Me ya kawo ni nan? Ina zan je? Me yasa zan je , me ake nufi daga gareni? Yaya qarshen lamarina zai kasance, idan ya farka ya san abin da ake nufi daga tafiyarsa da hajjinsa, lallai shi zai taka tattaki na biyu wanda(takliyatu) ma'ana kwabe zuciya da ruhi da tsarkakesu daga dukkanin abin da Allah bai yarda da shi ba daga siffofi da ayyuka. Sai ya tuba ya koma ga Allah daga dukanin zunubi da sabo daga dukanin mummunar xabi'a ya tuna da faxinsa maxaukaki:
(فَاخْلَعْ نَعْلَيْکَ إِنَّکَ بِالْوَادِ آلْمُقَدَّسِ طُوىً )[30]
Ka cire faxenka lallai kai kana cikin tsarkakakken kwazazzabo xuwa.
Wajibi kwabe faxe cikin wannan miqati mai tsarki, ma'ana son duniya da abin da ke cikinta waxanda suke katange mutum daga barin Allah matsarkaki, ya cire tufafin sabo da barna da suka hijabance daga barin mahaliccinsa sakamakon abin da hannunsa suka aikata. Sannan ya tattaka tattaki na uku(tahliya) yay i ado da kyawawan ayyuka da siffofo nagargaru da kyawawan halaye, domin ya kasance fdaga rinin Allah ya xaura tufafin biyu na ihrami da xa'a da taqawa da bautantaka.
sannan ya tattaka tattki na huxu(tajliyatu) zai yi fafutika da kai kawo wajen tajallin abin da yay i ado da shi daga ayyuka da siffofi, sai sunayen Allah kyawawa su yi tajalli cikinsa ya kasance alama da mudubi ga ubangijinsa cikin siffofinsa da sunayensa, idan har dutse ya kasance mahallin tajallin ubangiji ga musa(sai ubangijinsa ya yi tajalli gareshi) haka ma matsarkaki yana tajalli cikin zuciyar mahajjaci, lallai ita zuciyar mumini haramin Allah ce al'arshin mai rahama.
Ya zo cikin hadisi mai daraja cewa: sa'ilin da ka sauka miqati to ka quduri kwabe tufafin sabo ka sanya tufafin xa'a, lokacin da kacire xinkakkun tufafinka to kayi niyyar cire riya da munafunci daga zuciyarka da shubuha, sa'ilin da kayi wanka to kayi niyya wanke kurakure da zunubai.
وعن الامام الصادق 7: «اذا أردت الحجّ فجرّد قلبک لله تعالى من كلّ شاغل ... وفوض اُمورک كلّها إلى خالقک ... ثمّ إغسل بماء التوبة الخالصة ذنوبک وألبس كسوة الصدق والصفاء والخضوع والخشوع ، وأحرم من كلّ شيء يمنعک عن ذكر الله... ولبّ ... متمسّكاً بعروته الوثقى[31]
Daga imam sadiq(as): idan ka quduri hajji to ka karkaxe zuciyarka domin Allah daga dukkanin mai shagaltarwa, ka fawwala dukkanin lamarinka ga mahaliccinka, sannan kayi wanka da ruwan tuba da zai tsarkake zunubanka ka sanya tufafin gaskiya da tacewa da miqa wuya da qanqan da kai, ka haramtu daga dukkanin abin da zai hanaka ambaton Allah, ka amsa kira kana mai riqo da qarfafaffiyar igiya.
Barbarar mi'iraji da miqati:
Wajibi kan mahajjaci ya ji cikin zuciyarsa cewa miqati wata nukta ce domin fara mi'iraji cikin daren isra'I, sai ya tashi da shimixar barci zuwa al'arshi, daga turbaya zuwa ubangijin iyayen giji, shi hajji wata shimfixa ce da gabatarwa ga mi'iraji zuwa sama, mhallin fara mi'iraji shi ne miqati, sai ya karkaxe duk wasu alamomin shirka da son duniya daga zuciyarsa domin ganin kyawun ubangijinsa, sai ya gode masa cikakkiyar godiya,.
(إنّ الحمد والنّعمة والملک لک لا شريک لک لبّيک)[32]
Lallai godiya da ni'ima da mulki ya tabbata gareka babu abokin tarayya gareka mun amsa kiranka.
ـ عن رسول الله 6: «لمّا اُسري بي إلى السماء وصرت بحذاء الشجرة ... فلما كان في الموضع الذي بحذاء الشجرة نودي يا محمّد قال : لبّيک ، قال سبحانه : ألم أجدک يتيماً فآويتک ووجدتک ضالاً فهديتک ؟ قال النبي 6 : إنّ الحمد والنعمة والملک لک لا شريک لک لبّيک » .
Daga manzon Allah(s.a.w): sa'ilin da aka kaini isra'I zuwa sama na kasance dab da bishiya, ya yin da ya kasance a mhallin dab da bishiya sai akai kira ya muhammadu sai ya ce labbaika, sai matsarkaki ya ce: ashe ban sameka maraya na kusanto da kai na yi maka makoma, na sameka batacce sai na shiryar da kai, sai annabi ya ce: lallai gidiya da ni'ima da mulki sun tabbta gareka babu abokin tarayya gareka.
8- miqatin mala'iku domin kewaya xaki rayayye a sama ta huxu:
Miqati bai taqaitu da miqatin mutane a ban qasa cikin wanann duniya ba kaxai bari dais hi miqati ga duniyar mala'iku ga mala'ikun Allah, lallai mala'iku daura da miqatin qasa suna miqatai duniyar sama wadda mala'iku ke halarta wajen xaki rayayye.
قال الامام الصادق 7: «لمّا اسري بالنبي إلى السماء وصار بحذاء الشجرة وطافت الملائكة تأتي إلى البيت المعمور بحذاء الموضع التي هي مواقيت سوى الشجرة ، فلذلک أحرم من الشجرة دون المواضع كلّها
Imam sadiq(as) ya ce: sa'ilin da aka tafi da annabi isra'I zuwa sama ya kai ga kusa da bishiya mala'iku suka yi xawafi suna zuwa xaki rayayye kusa da wajen da sune miqatan bishiya, saboda haka ya xaura harami daga bishiya sabanin dukkanin ragowar miqatan.
Mala'iku suka riski miqatin zi hulaifa biye da manzon Allah(s.a.w) shi ne farkon wanda ya buxe musu haka.
9 – tunawa da ranar qiyama:
Lallai ibadun hajji sunfi komai kama da duniyoyin lahira, da abin da ya zo cikin qur'ani da hadisi daga yanayin ranar qiyama, daga ciki shi ne tarasu ranar taro
(يَوْمَ يَقُومُ آلنَّاسُ لِرَبِّ آلْعَالَمِينَ )[33]
Ranar mutane za su tashi ga ubangijin talikai.
Zasu tashi cikin likkafaninsu haka mahajjata suke kasance cikin farraen tufafi a miqatinsu suna suranta waxancan wuraren tsayuwa na qiyama, saboda sai suyi tanadi don waxancan wuarare masu tsanani da hanyoyi masu hatsari.
10- shiga wajen Allah daga kowanne waje: miqatin mazauna
harami daga wajen harami, miqatin waninsu daga gefan makka mai karamci. Haka na
nufin lallai shiga a ma'aunin gaskiya da magudanarta yana kasancewa daga kowanne
waje, dukkanin mutane bai xaya suke cikin hajji, idan miqatin hajjin tamattu'I
ya kasance daga cikin makka to lallai ya shiryarwa kan cewa shi kansa harami
miqati ne, lallai tafiya ce daga harami zuwa harami har mahajjaci ya risiki
failolin Allah tun tasowarsa daga harami har zuwa qarshen aikin hajjinsa, bayan
ya naxe etare dukkanin marhalolin irfani cin Arafat da mash'arul haram ya kai
ga tsololuwar burinsa a mina.
DAGA CIKIN SIRRIKAN MAKKA MAI KARAMACI DA MASALLACIN HARAMI
Lallai makka maiamci na dahga cikin garuruwa yankin hijaz wadda cikinta xakin ka'aba ke zaune, ka'aba xaki ne wanda ke yada kyawu da haske, Allah ya karramata matuqar karramawa, ya sanya ladubba ga masu ziyartarta.
1 – cikin garin makka akwai ayoyi mabayyanani muqamu Ibrahim da dutsen isma'il da zamzam da xakin ka'aba mai daraja, daga cikin ayoyi babu wani tsuntsu da ke tashi daga kan xaki ka'aba kuma babu wani tsuntsu da ke sanya mata qazanta, lallai dabbobi na rayuwa cikin aminci, babu wani jabberi da zai nufi xakin ka'aba da mummuna nufi face take ya halaka, kamar misalign abrahata najjashi da giwayensa da rundunarsa.
Mahajjaci ko mahajjaciya basu jin gajiya kowahala lokacin ibadun hajji ko da kuwa ya maimaita zuwa hajjin lokaci da dama daga wani yankin duniya mai nisa.
2- iyakar masallaci:
الكافي بسنده عن الحسن بن نعمان قال : سألت أبا عبدالله7 عمّا زادوا في المسجد الحرام فقال : ان إبراهيم وإسماعيل 8 حدّا المسجد الحرام بين الصفا والمروة[34] .
Alkafi da isnadinsa daga Hassan ibn nu'umanu ya ce: na tambayi baban Abdullah(as) daga abin da suka qara cikin masallacin harami, sai ya ce: lallai Ibrahim da isma'il(as) sun iyaknce masallacin harami tsakanin safa da marwa.
3- ka rubuta na 139 daga shafi na 90.
4- makka makomar maus tauhidi da masoyan ubangiji.
Lallai rayuka na bege da shauqin haxuwa da ubangijinsu a garin makka mai karamci da kewaya ka'aba a masallacin harami, lallai rayuka na nutsuwa da xebe haso da makka kamar yadda jinjiri nutsuwa da xebe haso da nonon mahaifiyarsa.
قال الامام الرضا 7: «سمّيت مكّة مكّة لأنّ الناس كانوا يمكّون فيها، وكان يقال لمن قصدها قد مكا[35]
Imam rida(as) ya ce: an kira makka da sunan makka saboda mutane na ihu cikinta, ya kasance ana kiran wanda ya ziyarceta haqiqa wane ya yi fito da qara ko ihu.
5- makka gida ne maketara ba tabbatacce ba:
Lallai mai sanye da harami da ihraminsa da hajjinsa yana qudurar ketare zunubansa da laifukansa cikin ketara gari amintacce ya zuwa gidan dawwama a masauki na gaskiya wajen sarki mai iko, dukkanin wanda yay i tafiya da guzurin taqawa da taimakon ubangiji daga ababen halitta ya zuwa mahalicci, hakan na tabbatuwa da wurgi da watsi da aikata dukkanin sabo da kuma yin aado da tufafin ihrami, ya amsa kira ya naxe dajijjika da qauyuka domain ya samu shiga
rahamar Allah, sannan ka da ya riqi makka mazauni na dindin.
الامام الصادق 7 قال «المقام بمكّة يقسي القلوب ».
Imam sadiq(as) ya ce: zama a garin makka yana qeqasar da zuciya.
قال الامام الباقر 7: «لا ينبغي للرجل أن يقيم بمكّة سنة ، قلت : كيف يصنع ؟ قال : يتحوّل عنها فيخرج منها ليدخلها محرماً، ويكون في صفّ ضيوف الرحمن .
Imam baqir(as) ya ce: bai kamata ga mutum ya zauna a garin makka har ts.a.won shekara guda, sai nace yaya zai yi to? Sai ya ce: zai juya baya daga gareta ya fita ya je ya sanyo harami ya dawo ya shigeta sanye da ihrami, sai ya kasance cikin sahun masu halartar liyafar Allah.
6- makka tushen alherai da ni'imomi:
dukkanin abin da yake da asali da jijiya larabawa na kiransa da uwa, mai nufi yana nufarsa, alqaryoyi da birane sun kasance tushen alherai da ni'imomi kuma ba za su gushe ba cikin wannan hali, sai dai cewa ita makka it ace uwar alqaryu da asalinsu, haqiqa an shimfixa qasa daga qarqashin xakin ka'aba, saboda haka dukkanin abin da ke kan qasa daga albarkatu da alherai makka ce asalinsu.
7- makka mahallin haxin kan masu xayanta Allah:
Lallai makka ana kiranta da bakka sakamakon mutane ba'arinsu na bugun ba'ari cikinta da hannuwa sakamakon tsananin turmutsutsi da tsananin taron da tajallin haxin kai cikin xayanta sahu sahu da da ibadu da wuraren ibada, duk da kasantuwa sassabawa cikin sashen juzu'ai sakamakon banbancin mazhabobinsu sai dai abu guda a bayyane yana nuni da haxin kan masu tauhidi musulmai, kamar yadda da sannu zamani zai zo dukkanin mazhabobi zasu kau hukunci xaya rak ya tabbata banbance banbance yak au lokacin bayyanar imam mahadi(af).
8- makka na daga mahallan qasqantar azzalumai ja'irai da yan danniya:
Lallai ts.a.won tarihi wani jabberi bai ta nufarta da sharri ba face Allah ya halakar da shi ya wulaqanta shi kamar misalin abarahata
قال الامام الصادق 7: «أسماء مكّة خمسة : اُمّ القرى ومكّة وبكّة والبساسة ، كانوا اذا ظلموا بها بستهم أي أخرجتهم وأهلكتهم ، واُم رحم كانوا إذا الزموها رحموا[36] .
Imam sadiq(as) ya ce: sunaye makka biyar ne: uwar alqaryu, makka, bakkatu, basasatu, sun kasance idan suka aikata zalunci sai ragargajesu ma'ana ta fiti da su ta halakar da su. Sai kuma sunanta cikon na biyar shi ne ummu Rahim, sun kasance idan suka lazimce ta sais u samu rahama.
وفي خبر آخر: «وكانت تسمّى بكّة لأنّها تبک أعناق الباعثين اذا بغوا فيها» .
A wani hadisin kuma: ta kasance ana kiranta da bakkatu sakamakon ta raga raga da wuyayen azzalumai idan suka aikata zalunci cikinta.
9 makka qasa ibada mashimfixar bauta:
Daga cikin mafi yawaita qasashen da kuka da qanqan da kai da ibada ya fi yawaita cikinta ita ce makka mai karamci.
قال الامام الصادق 7: «إنّما سمّيت مكّة بكّة لبكاء الناس حولها وفيها».[37]
Imam sadiq(as) : kaxai dai ankira makka da sunan bakkatu saboda kukan da muatne ke yi daura da ita da cikinta:
Wannan ma'anoni da sunan bakka ke babu karo juna ciki, wani lokaci bakkatu na da ma'anar tunkuxe abu, wani lokacin kuka, wani lokaci halakar da abu kamar yadda ya gabata cikin hadisan da mu ka ambata a baya.
قال الامام الباقر 7: «الساجد بمكّة كالمتشحّط بدمه في سبيل الله».
Imam baqir(as) ya ce: wanda ya yi sujjada a garin makka kamar misalign wanda yaji rauni ya jike da jinni a tafarkin Allah.
قال الامام السجاد 7: «من ختم القرآن بمكّة لم يمت حتّى يرى رسول الله 6 ويرى منزله في الجنّة ».
Imam sajjad(as) ya ce: duk wanda ya yi saukar qur'ani cikin garin makka ba zai mutu ba har sai ya yi ido biyu da manzon Allah, ya kuma masaukinsa cikin aljanna.
وقال 7: «النائم بمكّة كالمتشحّط في البلدان
A wani wajen kuma ya ce: mai barci cikin garin makka kamar misalign maikai kawo da nesanta cikin garuruwa.
10 – makka garin tsarkake ruhi da zukata:
Lallai cikin makka a na ba da dama mai yawa ga wanda ke son tsarkake zuciyarsa da haskakata da tsaftace ruhinsa, duk mai son surukantuwa da igiyar kyawu da girmama to cikin gaggawa haka zai sai a garin makka mai karamci.
قال رسول الله 6: «من مرض يوماً بمكّة كتب الله له من العمل الصالح الذي كان يعمله عباده ستين سنة ، ومن صبر على حرّ مكّة ساعة تباعدت عنه النار مسيرة مأة عام ، وتقربت منه الجنّة مسيرة مأة عام [38] .
Manzon Allah(s.a.w) ya ce: duk wanda ya yi rashin lafiya a makka Allah zai rubuta masa ladan aiki nagari wanda yake yinsa ts.a.won shekaru biyu, duk wanda yay i haquri da zafin ranar garin makka wuta zata nesanta daga barinsa gwargwadon nisan tafiyar shekaru xari, sannan aljanna za ta kusanto gareshi da tafiyar shekaru xari.
11- makka garin tsaftatattu tsarkaka:
Allah ya umarci Ibrahim da isma'il
(طَهِّرَا بَيْتِيَ لِلطَّائِفِينَ وَآلْعَاكِفِينَ وَآلرُّكَّعِ آلسُّجُودِ( [39]
Ku tsarkake xakina ga masu xawafi da mazauna da masu ruku'I da sujjada.
قال الامام الصادق 7: «فينبغي للعبد أن لا يدخل مكّة إلّا وهو طاهر، قد غسل عرقه والأذى وتطهر».
Imam sadiq(as) ya kamata ga bawa ka da ya shiga garin makka face yana cikin tsarki, ya tsarkake guminsa da ciwo ya kuma tsarkaka.
وقال 7: «من دخلها بسكينة غفر له ذنبه »، قلت : كيف يدخل بسكينة ، قال : «يدخلها غير متكبّر ولا متجبّر[40] .
Ya ce: duk wanda ya shiga garin makka cikin nutsuwa Allah ya yafe masa zunubansa, sai n ace: ta qaqa zai shiga tare da nutsuwa, ka da ya shige ta yana jin girman kai ko yana jabberi.
12- sallacin harami ya kasance tare da ginin xakin ka'aba tun zamanin annabi Ibrahim(as), lallai wannan masallaci yana da ladubba da hukunce-hukunce kebantattu da suka qara masa girmama da karamci har sallah ta kasance cikinsa daidai da raka'a dubu goma a waninsa, masallacin harami ya kasance fatan wusuli zuwa ga Allah matsarkaki.
عن الامام الصادق 7 يقول عند دخوله : «اللهم إني عبدک ، والبلد بلدک والبيت بيتک ، جئت أطلب رحمتک ، وأؤم طاعتک ، مطيعاً لأمرک ، راضياً بقدرک ، أسألک مسألة المضطرّ إليک الخائف لعقوبتک ، اللّهمّ إفتح لي أبواب رحمتک ، وإستعملني بطاعتک ومرضاتک [41] .
Daga imam sadiq(as) ya yin shigarsa zai ce: Allah ni bawanka ne xaki kuma xakinka ne, na zo ina neman rahamarka, ina nufar xa'arka, ina miqa wuya ga umarninka, ina mai yarda da qaddararka, ina roqonka wata buqata na larurantu gareka ina mai tsoron azabarka, Allah ka buxa mini qofofin rahamarka kayi amfani da ni cikin xa'arka da yardarka.
13-an hana mushrikai shiga masallacin harami harami saboda tsarkinsa da kasantuwarsa xakin tsarkaka, babu masu shafarsa face tsarkaka da tsarkin zahiri da na baxini,
(ثُمَّ لْيَقْضُوا تَفَثَهُمْ وَلْيُوفُوا نُذُورَهُمْ وَلْيَطَّوَّفُوا بِالْبَيْتِ آلْعَتِيقِ )[42]
Sannan kuma su sauke ibadunsu su cika alqawarukansu su kewaya `yantaccen xaki.
(مَا كَانَ لِلْمُشْرِكِينَ أَن يَعْمُرُوا مَسَاجِدَ آللهِ) [43].
Bai halsata ga mushrikai su raya masallatan Allah.
14- masallacin harami lama ce gas hinge da garkuwar tauhidi:
Ya zo cikin ingantaccen hadisi daga imam rida(as) yana cewa:
«لا إله إلّا الله حصني فمن دخل حصني أمن مِن عذابي »
Kalmar shahada garkuwa ta ce duk wanda ya shiga garkuwa ta ya aminta daga azaba ta.
Sannan shi masallacin harami alama ne ga haxin kai:
(وَمَن يُرِدْ فِيهِ بِإِلْحَادٍ بِظُلْمٍ نُذِقْهُ مِنْ عَذَابٍ أَلِيمٍ )[44]
Duk wanda ya nufe shi da karkata da zalunci zamu xanxana masa azaba mai raxaxi.
(وَلاَ تُقَاتِلُوهُمْ عِندَ آلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ حَتَّى يُقَاتِلُوكُمْ فِيهِ ) .[45]
Kada ku fara yaqarsu a masallacin harami har sai sun fara yaqarku cikinsa.
Kowa da kowa yana cikin aminci a cikin masallacin harami( duk wanda ya shihge shi ya aminta daga azaba ta), masallacin harami na daga cikin amintaccen shingen Allah.
15- masallacin harami mafarar jihadi tare da shirka duk duniya:
Manufa ga masallacin harami bai taqaitu da ibada ba kaxai, bari dai tsuhen tauhidi ya bayyana ta hanyar kore shirka da dukkanin siffofinta tun daga adamu har zuwa cika makin annabawa(as) dukkanin annabawa da manazannida wasiyyansu da duk wanda ke hanya da suke kai daga malamai masu tsarkin niyya masu aikata abin da suke faxi magada annabawa, sun ihu da sauti xaya:
(لبّيک اللّهمّ لبّيک لا شريک لک لبّيک )
Mun amsa kiranka babu abokin tarayya gareka mun amsa kiranka.
Sai miqa al'amrin wannan masallaci ga wanda yake mai xayanta Allah cikin aqidarsa da sulukinsa,
(إِنَّمَا يَعْمُرُ مَسَاجِدَ آللهِ مَنْ آمَنَ بِاللهِ وَآلْيَوْمِ آلآخِرِ وَأَقَامَ آلصَّلاَةَ وَآتَى آلزَّكَاةَ وَلَمْ يَخْشَ إِلاَّ آللهَ)[46]
Kaxai dai wanda yake raya masallatan Allah shi ne wanda ya yi imani da Allah da ranar qiyama ya tsayar da sallah ya bada zakka bai ji tsoron komai face Allah
(وَمَا لَهُمْ أَلاَّ يُعَذِّبَهُمُ آللهُ وَهُمْ يَصُدُّونَ عَنِ آلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ وَمَا كَانُوا أَوْلِيَاءَهُ إِنْ أَوْلِياؤُهُ إِلاَّ آلْمُتَّقُونَ )[47]
Menene da su da Allah ba zai yi musu azaba ba, alhalin su suna kore mutane gabarin masallacin harami kuma ba su kasance majibantansa ba, babu majibantansa face masu taqawa.
Saboda haka tafiyar da masallacin ba ya ga waxanda suke sanya abayar qarya ta boge suna wasa da kalmomi da lafuzza yana da'awar abin da ba haqqinsa na cewa wai shi ne hadimin haramai biyu masu daraja. Da karyar cewa wai shi ne hadimin mahajjata.
Mustahabbi ne a shiga ta qofar banu shaiba, lale lokacin da sarkin muminai Ali(as) ya rugurguza gumaka quraishawa ya binne hubal babban gunki a qofarn banu shaiba, saboda mustahabbi ne shiga ta wannan qofa don gunki da bautar gumaka ta kasance tattake qarqashin qafafuwa.
16- masallacin harami wata alamace da ke nuna kore qabilanci da tsarin fifita:
Lallai kai ya yin shigarka masallacin harami za ka ga dukkanin kowacce rinin al'umma da qabilu daban daban dukkaninsu bai xaya babu banbanci cikin ayyukan ibadun hajji.
(وَآلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ آلَّذِي جَعَلْنَاهُ لِلنَّاسِ سَوَاءً آلْعَاكِفُ فِيهِ وَآلْبَادِ .( [48]
Masallacin harami wanda muka sanya shi daidaito ga mutane tsakanin mazauni da baqauye cikinsa.
Dukkanin mutane maza da mata bai xaya suke cikinsa babu banbanci.
عن الامام الصادق 7: يابن رسول الله أقوم أُصلّي والمرأة جالسة بين يديّ أو مارّة ؟ قال 7: لا بأس إنّما سمّيت بكّة ، لأنّه يبک فيها الرجال والنساء.
Daga Imam sadiq(as): ya xan manzon Allah iana tashi inyi sallah mace na zaune gabana ko kuma ta na ketarawa? Sai imam ya ce: babu laifi, kaxai daian kirayi makka da sunan bakkatu saboda maza da mata suna tunkuxe junansu cikinta saboda turmutsutsi.
Ba wajibi ba ne mata su halarci masallatan juma'a face masallacin harami lallai shi wajibi ne su halarce shi don yin ibadun hajji kamar xawafi da sallarsa, dukkanin qofofin arziqi an buxe su ga kowa da kowa, babu banbantawa tsakanin balarabae da ba'ajame, babu banbanci tsakanin farar fata da baqar fata, babu banbanci tsakanini namiji da mace.
17- masallacin harami mafarar tafiya da suluki zuwa ga Allah:
(سُبْحَانَ آلَّذِي أَسْرَى بِعَبْدِهِ لَيْلاً مِنَ آلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ إِلَى آلْمَسْجِدِ آلاْقْصَى آلَّذِي بَارَكْنَا حَوْلَهُ لِنُرِيَهُ مِنْ آيَاتِنَا( [49]
Tsarki ya tabbata ga wanda ya tafi bawansa daga masallacin harami zuwa masallacin aqsa wanda muka albarkaci daura da shi domin mu nuna masa daga ayoyin mu.
18- masallacin harami alqibala masu tauhidi:
(قَدْ نَرَى تَقَلُّبَ وَجْهِکَ فِي آلسَّماءِ فَلَنُوَلِّيَنَّکَ قِبْلَةً تَرْضَاهَا فَوَلِّ وَجْهَکَ شَطْرَ آلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ.( [50]
Haqiqa muna ganin jujjuyar fuskarka cikin sama, da sannu zamu juyar da kai ga alqibala da zaka yarda da ita , sai ka juyar da fuskarka wajen masallacin harami.
Kowa zai fuskantar zuwa wannan quxubi da maganaxisun ruhinsa da hankali, kai hatta cikin sallah ya na fuskantar ka'aba ga wanada ke cikin masallaci, wanda kuma ke waje yana fuskantar masallacin harami, wanda kuma ke wajen makka yana fuskantar makka.
(وَحَيْثُ مَا كُنْتُمْ فَوَلُّوا وُجُوهَكُمْ شَطْرَهُ )[51]
Duk inda kuka kasance ku juyar da fuskokinku wajensa.
Mustahabbi ne yin alwala da zama fuskar alqibla, kamar yadda ke wajabta fuskantarta yayain sallah da yanka, haka ma yana haramta fuskantarta ko ba ta baya lokacin shiga banxaki don biyan buqata.
19- masallacin harami mabayyana ne na godiya da saka aiaki alheri:
Lallai mustahabbi ne ga wanda shiga cikinsa ya karanta addu'o'I daga cikinsu akwai:
(السّلام عليک أيُّها النبي ورحمة الله وبركاته ، بسم الله وبالله ومن الله وما شاء الله، والسّلام على أنبياء الله ورسله ، والسّلام على رسول الله والسّلام على ابراهيم ، والحمد لله ربّ العالمين )
Amincin Allah da rahamarsa da albarkatu su tabbata gareka ya kai annabi, ina faraway da sunan Allah da Allah daga Allah masha' Allah, aminci ya tabbata ga annabawan Allah da manzanninsa, aminic ya tabbata manzon Allah, aminci ya tabbata ga Ibrahim, dukkanin godiya ta tabbata ga Allah.
Wannan na daga cikin godiya ga masu ni'imtawa cikin shiriya da tarbiya da sallamawa.
20- tabbatarwa da zurfafar imani:
Daga cikin ladubban masallacin harami xawafi sallah da tilawar qur'ani da kallon ka'aba da ambaton Allah matsarkaki daga abin da ya keke taimakawa cikin tabbatar imani da zurafafarsa ciki zukata.
عن رسول الله 6: «أعظم المساجد حرمةً ، وأحبّها إلى الله وأكرمها على الله تعالى المسجد الحرام .
Daga manzon Allah(s.a.w): mafi girman alfarmar masallatai da mafi soyuwarsu zuwa ga Allah da mafi karamcinsu gareshi shi ne masallacin harami.
Ya zo cikin sharhin ma'azimaini; lallai mahallin da akai bautar gunki cikinsa, tare da shi dutse wanda aka sassaqa gunki hubal daga gareshi wanda ali(as) ya hau gadon bayan annabi(s.a.w) ya wurgo gunkin daga saman ka'aba,sai manzo ya umarce shi ya bizne wannan gunki mai suna hubal bakin qofar banu shaiba, sai shiga masallaci ta qofar banu shaiba ya zamanto sunna sakamakon faruwar haka.
قال الله تعالى : (رَبَّنَا إِنِّي أَسْكَنتُ مِن ذُرِّيَّتي بِوَادٍ غَيْرِ ذِي زَرْعٍ عِندَ بَيْتِکَ آلْمحَرَّمِ رَبَّنَا لِيُقِيمُوا آلصَّلاَةَ فَاجْعَلْ أَفْئِدَةً مِنَ آلنَّاسِ تَهْوِي إِلَيْهِمْ وَآرْزُقْهُم مِنَ آلَّثمَرَاتِ لَعَلَّهُمْ يَشْكُرُونَ[52].
Allah maxaukaki yana cewa: ya ubangijin mu lallai ni na zaunar zurriyata a wani kwazazzabo da bai da shuka wajen xakinka mai alfarma, ubangijina domin su tsayar da sallah, ka sanya zukata muatane su karkata da bege garesu ka zaurta su ya`yan it ace tsammaninsu suyi godiya.
1- 1- Ka'abaalqibla ce ga wanda ke yin sallah cikin masallacin harami, shi kuma masallaci shi ne alqibala ga mutanen makka, sannan jihhohin ka'aba alqibla ne ga musulmi daga ragowar qasashe da garuruwa.
(فَوَلِّ وَجْهَکَ شَطْرَ آلْمَسْجِدِ آلْحَرَامِ )[53]
Ka juyar da fuskarka wajen masallacin harami.
2 ka'aba alqiblar musulmi cikin faxinta, kamar yadda ta kasance alqibla cikin amudinta, lallai ita alqibla daga mahallinta, tun daga tolon qasa ya zuwa tozon samaniya.
3 ka'aba xakin Allah mai alfarma
(إِنَّ أَوَّلَ بَيْتٍ وُضِعَ لِلنَّاسِ لَلَّذِي بِبَكَّةَ مُبَارَكاً وَهُدىً لِلْعَالَمین)[54]
Lallai xaki na farko da aka sanya domin mutane shi ne wanda yake bakkatu mai albarka da shiriya ga talikai.
4- ka'aba xaki ma'abocin zawiyoyi da shakali da ke tare da amudai huxu.
روى عن الامام الصادق 7 انّه سُئل لِمَ سمّيت الكعبة بالكعبة ؟ فقال 7 : إنّها مربعة ، فقيل له ولم صارت مربعة ؟ قال : لأنّها بحذاء العرش وهو مربع ـ في السماء السابعة يطوف حولها الملائكة المقرّبون كجبرئيل ـ فقيل له ولِمَ صار العرش مربعاً؟ قال : لأن الكلمات التي بني عليها الاسلام أربع : سبحان الله والحمد لله ولا إله إلّا الله والله أكبر . [55]
An rawaito daga imam sadiq(as) cewa an tambaye shi menene ya sanya ake kiran ka'aba da ka'aba? Sai ya ce: lallai ita ka'aba nada amudai huxu, sai aka ce masa menene ya sanya ta kasance ma'abociyar amudai huxu? Sai ya ce: saboda tana saitin ala'arshi, shi kuma al'arshi amudai huxu gareshi a sama ta bakwai mala'iku makusnata kamar misalign jabra'ilu suna xawafi daura da ita, sai aka qara tambayarsa menene ya sanya al'arshi ta kasance ma'abociyar amudai huxu? Sai ya ce: saboda kalmomin da ka ginata da su kalmomi ne guda huxu: subhanallah walhamdu lillah wala ilaha illahu wallahu akbar.
Sharhi da bayanin wannan hadisi mai daraja a taqaice: shi ne tafiya da suluki zuwa ga Allah maxaukaki haka ma wannan hadisi yay i bayanin ainahin rukunan muslunci a taqaice cikin ginin xakin ka'aba maxaukaki, kaxai dai bayani ne kan kalmomi huxu tsarkaka sune: tasbihi, thamidi, tahlili, takbir.
Lallai daga mafi girman hanyar ya zuwa sanin Allah matsarkaki shi ne asasin muslunci kaxai dai hakan atbbatuwa da duba ya zuwa ayoyin kawuka, lallai kawukanku ana qidaya su daga cikin hayoyin zuwa ga Allah.
(من عرف نفسه فقد عرف ربّه)
Dukkanin wanda ya san kansa haqiqa ya san ubangijinsa.
Daga cikin bayyanan lamari shi ne yayain da mutum ke duban kansa tabbas zai ga tawaya da naqasa cikinsa, lallai shi ya kasance tun zamanin da yake kwance cikin mahaifiyarsa bai san komai ba, lallai mutum bai da ikon korar quad daga fuskarsa lokacin da yake jinjiri kwance kan shimfixar haihuwa yaa bain shayarwa, lallai shi mutum halittacce ne jahili gajiyayye, saboda sai ya tsarkake ubangijinsa daga jahilci da gajiyawa yana mai raya Allah matsarakaki wanda shi hakan rukuni ne na fari cikin tafiya da suluki ya zuwa ga Allah kamar matsayin rukunin hajarul aswad a cikin farkon xawafi.
Sannan ya dubi kyawu daga daura da shi sai ya danganta shi saki babu qaidi ya zuwa kyawu tsantsa wanda shi ne Allah matsarkaki, lallai shi yafi komai cacanta da a gode masa da yaba masa sai ya ce: alhamdu lillah, wnada shi ne rukuni na biyu cikin suluki da sanin Allah matsarkaki wanda daidai yake da matsayin rukunul Iraqi daga ka'aba ma daraja.
Sannan ya dubi cewa Allah shi ne tsantsar kamala da kyawu kuma ya cancanci haiba kwarjini da girma, lallai shi ne mafi cancanta da bauta da soyayya da qanqan da kai gabansa, sai ya ce cikin hailala da annuri:
(لا إله إلّا الله)
Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.
Ita Kalmar ilahu ta samu asali da Kalmar walahu ma'ana soyayya da bege ma'ana ta biyu kuma da take da ita shi ne abin bautawa abin so na haqiqa, wannan shi ne rukuni na uku wanda yake dadai da matsayin rukunul shami daga xakin Allah mai alfarma.
Sannan ka duba shin zai yiwu ga wani ya siffanta Allah ya sanya masa abokin tarayya? A a sam sam baa zai yiwu ba, lallai shi Allah matsarkaki ya girmama daga siffantuwa, lallai bamu bauta maka haqiqanin bauta ba, lallai bamu sanka haqiqanin sani(ALLAHU AKBAR) wannan shi ne rukuni na huxu wanda muslunci ya ginu kai, lale shi daidai yake da matsayin rukunul yamani daga ka'aba mai tsarki.
5- ka'aba ma'abociyar rukunai huxu: 1 rukunul sharqi kokum aka kira shi da rukunl hajarul aswad shi ne mafara da qarshe rufewa cikin keawayar ka'aba da xawafi bakwai 2 rukunul Iraqi shi ya fuskanci Iraqi shi yasa ake kiaransa da haka 3 rukunul shami fuskanin sham 4 rukunul yamani ana kiransa da sunan rukunul alawi haka ana kiransa da rukunul ahlul baiti: mustahabbi ne shafarsa yayain xawafi, haqiqa shi ne rukunin da ya tsage lokacin da naquda ta kawo Fatima bintu asad xakin ka'aba, sai ta haifi sarkin muminai Ali(as) a cikin xakin ka'aba mai alfarma.
6- cikin ka'aba akwai qofar zinariya wanda ake lazimta mahajjata suna lazimtarta da qasqantar da kai da kuka domin Allah ya karbi tubansu, tsakanin ka'aba da rukunl hajarul aswad da muqamu Ibrahim akwai(alhaximu) lallai mutane sna rusa dukkanin zunubansu sakamakon turmutsitsinsu, sannan cikin ka'aba akwai indararon zinariya(indararon rahama) ya na kwarara kan hajarul isma'il.
Hajaru isma'il mahallin da isma'il ya kafa haimarsa tare da mahaifiyarsa hajara, hajaru an xauko Kalmar ne daga hujuratu da ma'anar xaki da falo ko kuma daga rabin shakalin da'ira, ka kuma daga hijaratu dag abin da ake shingewa da shi kamar bango wanda ya tsayu da duwatsu, hajaru isma'il ya zamanto mahalli ne da a ka binne shi da mahaifiyarsa da annabawa saba'in, sai xawafi ya shiga ya kasance girmamawa gareshi da qaburburan salihai da mata salihai.
7- ka'aba mahallin xawafi muminai saboda kaxaituwar ruhinsu kamar misalign mala'iku masu xawafi daura da baitul ma'amur a sama ta bakwai.
Sannan mutum yana da sasanni biyu , na ruhikamar misalign mala'iku, da na gangar jiki kamar misalign dabbobi, lallai wanda ya tsarkaka ya rabauta,
(قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّاهَا * وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّاهَا)[56]
Haqiqa wanda ya tsarkake shi ya rabauta, haqiqa wanda ya turbude shi ya tabe.
Mutum da tsarin zirin jikinsa zai kewaya ka'aba da duwatsu, sai dai cewa da zuciyarsa ta ruhi yana xawafi ne daura da ka'abar tsarkaka.
8- ka'aba alama ce ta wahada da xayantuwa kamar qur'ani mai daraja da mutum kammalallai tadwini da kamar mutum kammalle aini, ma'ana annabi da imami(as) lallai iata ka'aba kwaya xaya ce rak a ban qasa, addini kwaya xaya ne cikin halittu, ubangijin taliaki xaya ne, dukkaninsu suna kira zuwa ga xayanta da har abadantaka da xawafi da fana'i(narkewa) da Allah da wanzuwa tare da shi ne ma'anar da'awar tasowa daga yawaita ya zuwa xayanta kamar yadda yake ciki tafiyar irfani.
8- ka'aba alama ce dalilin haxin kan musulmi cikin dukkanin daurorin rayuwarsu daga shekaru da watanni da mintuna, tun daga ranar haihuwa har zuwa mutuwa da shiga kabari, daga sallah wadda it ace amudin addini ya zuwa yanka hadaya tsakanin musulmai, cikin dukkaninsu muna cewa:
(والكعبة قبلتي )
Ka'aba alqibala ta.
Iata ce alama ga wahadata tare da `yan'uwa na daga musulmai cikin kowanne bigiren duniya.
10- ka'aba tsuhen tsarakaka alamar ibada
(أَن طَهِّرَا بَيْتِيَ لِلطَّائِفِينَ وَآلْعَاكِفِينَ وَآلرُّكَّعِ آلسُّجُودِ)[57] .
Ku tsarkake xakina ga masu xawafi da mazauna da masu ruku'I da sujjada.
11- ka'aba alqiblar musulmi, masallacin harami uwa ga masallatai, haqiqa alqiblar dukkanin masallatai shi ne fuskanin ka'aba da jihharta. Makka iata ce uwar alqaryu duukanin alqaryu suna kallonta ya yin sallah, cikin masallatai Allah ya yi izini da a xaukaka a ambaci sunansa cikinsu
(رجال يحبّون أن يتطهّروا)
Mazaje masu nufin tsarkaka.
Dukkanin wanda ya tsarkake kansa zai kasance abin so wajen Allah
(إن الله يحبّ المتطهّرين )
Lallai Allah na son masu tsarkaka.
Tsarkakakken gida wanda ke da tsarkin gangar jiki da ruhi ke kewaya shi. Duk wanda ya tsakaka zai kasance abin so wajen ubangijinsa zai kasance madubi ga sunayen Allah kyawawa, mahalinn tajallin siffofinsa maxaukaka, sai ganinsa ya zamanto ganin Allah, jinsa jin Allah, lallai tsarkakakke na haqiqa ya na shafar ma'anoni da sirrikan ka'aba, kamar yadda zai shafi ma'anonin qur'ani da baxinansa
(لاَ يَمَسُّهُ إِلاَّ آلْمُطَهَّرُونَ )[58]
Babu masu shafarsa face tsarkaka.
Duk wanda ya kasance jahili mara tsarki
(وَمَا كَانَ صَلاَتُهُمْ عِندَ آلْبَيْتِ إِلاّ مُكَاءً وَتَصْدِيَةً )[59]
Sallarsu ba ta kasance bakin komai wajen masallaci face iface iaface da tafi.
Ma'ana suna fito da ihu da tafa hannuwansu sun kasance kamar dabbobi kai sun fi dabbobi bata.
12- ka'aba tushen haxin kai da motsi da juyin juya hali da tsayuwa ta xaixaiko da jama'a
(إِنَّمَا أَعِظُكُم بِوَاحِدَةٍ أَن تَقُومُوا للهِ مَثْنَى وَفُرَادَى ) [60]
Kaxai dai ina yi muku wa'azi domin ku tsaya domin Allah kuna bibiyu da xaixaiko.
وقد (جَعَلَ آللهُ آلْكَعْبَةَ آلْبَيْتَ آلْحَرَامَ قِيَاماً لِلنَّاسِ( [61]
Haqiqa Allah ya sanya ka'aba xaki tsararre ma'aunin addini ga mutane.
Dole ne da farko a zage dantse ayi gwagwamarya da xauki ba daxi da sha'awe sha'awen zuciya, lallai babban maqiyinka ita zuciayraka da take tsakankanin geffanka. Sannan kuma a tsallaka ga yaqar maqiya addini da shaixanu da maqiaya falaloli da kyawawan halaye(domin mutane su tsaye kan adalci) (addini ba zai gushe a tsayayye matuqar ka'aba na tsaye) lallai ita rayuwa ka'aba rayuwar addini ce, sannan rayuwar mutane ta dogara da rayuwar addini.
قال أميرالمؤمنين علي 7: «الله الله في بيت ربّكم ، لا تخلوه ما بقيتم فانّه إن ترک لم تناظروا
Sarkin muminai Ali(as) ya ce: ina haxaku da Allah ina haxaku da Allah ku kiyaye xakin ubangijinku, ka da ku wofantar da shi matuqar kuna raye. Lallai idan kuka yi watsi da xakin Allah ba za ai muku jinikirin azaba ba.
Ma'ana maqiyanku ba za su jinkirta muku da kai muku hare hare ba domin kawar da addini da gogec dukkanin kufaifayinsa.
قال رسول الله 6: «من أراد دنيا وآخرة فليؤم هذا البيت »
Manzon Allah(s.a.w) ya ce: duk mai neman duniya to ya nufi wannan xaki mai alfarma.
Ma'ana ya nufi ya ziyaraci wannan xaki mai alfarma mai albarka, sannan bayyanar mahadi a qarshen zamani za ta fara ne daga garin makka daga ka'aba wanda gwagawarmayarsa za ta kasance gwagawarmaya ta aqida da tattalin arziqi
(ليشهدوا منافع لهم )
Domin su halarci abubuwa masu alfanu garesu.
Lallai shi ya reshenta kan tsayuwar aqida
(وَلاَ تُؤْتُوا آلسُّفَهَاءَ أَمْوَالَكُمُ آلَّتِي جَعَلَ آللهُ لَكُمْ قِيَاماً)[62]
Ka da ku baiwa wawaye dukiyoyinku wxanada Allah ya sanya ta gareku kuna masu tsayuwa.
Idan tsayuwa biyu suaki karo da juna to za a gabatar da asali kan reshe, saboda sai tsayuwar aqida ta gabata.
13- ka'aba tushen mafarar `yanci da tushensa:
(وليطوّفوا بالبيت العتيق )
Su kewaya `yantaccen xaki.
Lallai shi xakin ka'aba ya `yantu daga ya kasance qarqashin ikon wani, kamar yadda ya `yantu daga ruwan xufana, kamar yadda ya kasance xaki na farko da aka sanya a ban qasa domin mutane, shi ne mafi daxewar xakuna.
قال الامام الباقر 7: «هو بيت حرّ عتيق من الناس لم يملكه أحد»
Imam baqir(as)ya ce: xakin ka'aba `yantacce, `yantacce daga mutane wani bai taba mallakarsa ba.
Shi xakin Allah ne mai girma da xaukaka kamar yadda ya ce( ku tsarkake xakina) ( wajen xakinka mai alfarma) saboda haka mahajjaci ya ke kewaya xakin ka'aba domi ya kubuta daga bautan wanin Allah.
Qaqa ga wanda ya kasance bawan cikinsa da farjinsa ya biyewa son zuciyarsa, ko kuma mulki da alfarma suka mallake shi duniyar ta maishe his bawa, ko kuma ya bi hanyar shaixani, ko kuma mataimakn shaixan suka hallaka shi daga aljanu da mutane, saboda haka ya kewaya xakin Allah haqiqanin kewayawa.
قال أميرالمؤمنين 7: «لا تكن عبد غيرک وقد جعلک الله حُرّاً
Sarkin muminai Ali(as) ya ce: ka da ka sake ka yard aka zama bawan waninka alhalin Allah ya halicceka `yantacce xa.
14- ka'aba tushen daidaito da adalci: dukkanin mutane na nesa da na kusa namiji da mace talaka da mawadaci malami da jahili balarabe da ba'ajame qungiyoyi da qabilu da wasunsu dukkaninsu bai xaya suke gaban xakin ka'aba
(سواء العاكف فيه والباد)
Cikinta baqauye da xan gari bai xaya suke.
(إن أكرمكم عند الله أتقاكم(
Mafi karamcinku gun Allah shi ne wanda yafi tsoransa.
15- ka'aba tushen gamammiyar marja'iyya ga mutane:
(وَإِذْ جَعَلْنَا آلْبَيْتَ مَثَابَةً لِلنَّاسِ وَأَمْنا)ً [63]
Sa'ilin da muka sanya xaki makoma ga mutane da aminci.
Daga cikin ma'anonin (masabatu)makoma shi ne marja'iyya, lallai (taba) ya tuba na da ma'anar ya koma ya dawo sannan harafin ta'u cikin Kalmar masabatu ya da ma'anar mubalaga kamar allamatu, lallai shi wannan xaki mai tsarki makoma ne mai maimaito ga dukkanin mutane, ka'aba makomar al'ummu da jama'a cikin dukkanin motsinsu da sha'aninsu.
16- ka'aba it ace mafi tsufan wuraren bauta ts.a.won zamani
(إِنَّ أَوَّلَ بَيْتٍ وُضِعَ لِلنَّاسِ لَلَّذِي بِبَكَّةَ مُبَارَكاً وَهُدىً لِلْعَالَمِينَ[64](
Lallai xaki na farko da aka sanyawa mutane shi ne wanda yake bakkatu mai albarka da shiriya ga talikai.
Da wannan ne ka'aba ta fifita kan baitul muqaddas, ka'aba ta kasance xakin Allah mai daraja da darajar tsofaffin kufaifayi. Sannan darajar ka'aba abu ne da ya bijiro mata saboda haka ta xaukaka sakamonon danganewarta da Allah matsarakaki sarki(ku tsarkake xakina) ka'aba ta kasance mahallin ibadar Allah masaukin saukar wahayi ga cika makin anabwa da manzanni muhammadu(s.a.w)
() 17 ـ عن أبي حمزة الثمالي قال : قلت لأبي جعفر 7 في المسجد الحرام لأيّ شيء سمّاه الله العتيق ؟ فقال : انّه ليس من بيت وصفه الله على وجه الأرض إلّا له ربّ وسكّان يسكنونه غير هذا البيت ، فانّه لا ربّ له إلّا الله عزّوجلّ وهو الحرّ، ثمّ قال : إن الله عزّوجلّ خلقه قبل الأرض ـ وهذا وجه آخر لتسميته بالعتيق فان العتيق يقال للقديم أيضاً ـ ثمّ خلق الأرض من هذه فدحاها من تحته[65] .
An karbo daga abu hamza sumali ya ce: na cewa baban Abdullah(as) saboda me Allah ya kira xakin ka'aba da sunan `yantacce? Sai ya ce: babu wani xaki da Allah ya siffanta shi a kan qasa face yana da iyayengiji da mazauna cikinsa in banda wannan xaki, lallai babu iyayen giji gareshi face Allah mai girma da xaukaka shi wannan xaki `yantacce ne, sannan ya ce: lallai Allah mai girma da xaukaka ya halicci wannan xaki gabanin halittar qasa , wanna na daga wata fuskar ta kiransa da atiku saboda ana kiran dukkanin abin da ya tsufa da sunan atiku, sannan ya halicci qasa ya shimfixa ta daga qarqashin xakin ka'aba.
A wata riwayar kuma: an kira wannan xaki da sunan atiku saboda kasantuwarsa ya `yantu daga nutsewa daga ruwan xufana, haka an `yanta harami tare da shi, an tsare ruwan xufana an hana shi halakar da shi.
18- ka'aba zababben xaki Allah a ban qasa, kamar yadda ubangiji ya tace ya zaba daga annabawa.
عن الامام الصادق 7 إن الله اختار من كلّ شيء شيئاً وإختار من الأرض موضع الكعبة . وقال 7: ما خلق الله عزّوجلّ بقعة في الأرض أحب إليه منها، ولا أكرم على الله منها.
Daga imam sadiq(as) lallai Allah ya zabi wani abu daga cikin kowanne abu, ya zabi mahallin ka'aba daga ban qasa. Ya ce Allah mai girma da xaukaka bai halicci wani bigire cikin qasa mafi syuwa wajensa daga ka'aba, haka bai halicci mafi karamci daga gareta ba.
19- ka'aba tushen albarkun Allah abn bauta, albarka shi ne alheri matabbaci wanda bai yankewa,
(إِنَّ أَوَّلَ بَيْتٍ وُضِعَ لِلنَّاسِ لَلَّذِي بِبَكَّةَ مُبَارَكاً وَهُدىً لِلْعَالَمِينَ.( [66]
Lallai xaki na farko da aka sanyawa mutane shi ne wanda ke bakkatu mai albarka shiriya ga talikai.
20 ka'aba tushen shiriya(shiriya ga talikai) cikinsa akwai ayoyi mabayyanu da suke shiryar da halittu ga zuwa abin da yafi daidaito.
21- ka'aba mahallin tuba kamar yadda ya kasance cikin qissar anabi adamu(as) kamar yadda zai kasance bayan haka: ( sannan ya sanya xaki mai alfarma swun baitul ma'amur ya zama tuba ga masu zunubi daga `ya`yan adamu da kuma zama tsarki garesu.
22- hajji ta wajabta dogaro da faxinsa maxaukaki:
(وَللهِ عَلَى آلنَّاسِ حِجُّ آلْبَيْتِ مَنِ آسْتَطَاعَ إِلَيْهِ سَبِيلاً( [67]
Allah ya wajabta ibadar hajji ga waxanda suka samu dama gareshi.
23- maziyarta xakin ka'aba suna daga cikin alamomin da ke sanyawa a tuna da Allah, saboda bai halsata a halasta abin da Allah ya haramta,
(يَا أَيُّهَا آلَّذِينَ آمَنُوا لاَ تُحِلُّوا شَعَائِرَ آللهِ وَلاَ آلشَّهْرَ آلْحَرَامَ وَلاَ آلْهَدْىَ وَلاَ آلْقَلاَئِدَ وَلاَ آمِّينَ آلْبَيْتَ آلْحَرَامَ.( [68]
Ya ku waxanda sukai imani ka da ku halasta ibadar Allah da wata mai alfarma da hadaya da rataya raquman hadaya da masu nufin xaki mai alfarma.
24- ka'aba xakin Allah wanda ya sanya domin mutane baki xaya sai dai cewa babu mai jibantarsa face mai taqawa
(أَوْلِياؤُهُ إِلاَّ آلْمُتَّقُونَ )
majibantansa face masu taqawa.
Kamar misalign annabawa da wasiyai da malamai da salihai da muminai sashensu masoya ga sashe duk wanda ya jibancei al'amrin ka'aba koma bayansu lallai shi ya daga barayin ka'aba, za a yanke hannuwansu lokacin bayyanar imam mahadi(af)
25- ka'aba alqibla(ka'aba alqiblata) daga doron qasa ya zuwa tozon samaniya, hukuncinta na banbanta da ragowar masallatai, wanda ya kasance cikin janaba ko haila bai halasta su ketara ta kanta ba ko da kuwa ka'aba ta rushe, wannan sabaini masallatai ya yin da suka rushe ba kiyaye filinsu da sama da abin da yake samansa.
26- lallai alfarmar xakin ka'aba ya kasance tun gabanin Ibrahim(as) saboda faxinsa maxaukaki: wajen xakinka mai alfarma haqiqa ya jibanci al'amuran ka'aba(ku bautawa ubangijin wannan xaki)[69] lallai xakin na da ubangida da zai kare shi.
عن أبي عبدالله 7 قال : إنّ الله عزّوجلّ دحى الأرض من تحت الكعبة إلى منى ، ثمّ دحاها من منى إلى عرفات ، ثمّ دحاها من عرفات إلى منى ، فالأرض من عرفات ، وعرفات من منى ، ومنى من الكعبة .[70]
27- daga baban Abdullah(as)ya ce: lallai Allah mai girma da xaukaka ya shimfixa qasa qarqashin xakin ka'aba ya zuwa mina sannan ya shimfixata daga mina zuwa Arafat, sannan ya shimfixata daga Arafat zuwa mina, saboda haka qasa daga Arafat take sannan Arafat daga mina take sannan mina daga ka'aba take.
ـ عن أبي عبدالله 7 قال : كان موضع الكعبة ربوة من الأرض ـ الربوة ما إرتفع من الأرض ـ بيضاء تضيء كضوء الشمس والقمر حتّى قتل إبنا آدم أحدهما صاحبه ، فإسودت ، فلمّا نزل آدم رفع الله له الأرض كلّها حتّى رآها، ثمّ قال هذه لک كلها، قال : يا رب ما هذه الأرض البيضاء المنيرة (قال : هي في أرض وقد جعلت عليک ان تطوف بها كل يوم سبعمأة طواف . [71]
28- an karbo daga baban Abdullah(as)ya ce: mahallin ka'aba ya kasance jiga daga qasa- jiga shi ne tudun qasa- fara tas tana haskaka kamar hasken rana da wata har zuwa lokacin xaya daga `ya`yan adamu(as) ya kashe xan'uwansa sai ta koma baqin qirin, lokacin da adamu Allah ya sauko da adamu ya xaga masa qasa sama har ya ganta, sannan ya ce masa : wannan dukkaninta ta kace, sai adamu ya ce: ya ubangijina wannan fafar qasar fa mai haskaka, sai ya ce masa ita qasa da na sanya maka kayi xawafi xari bakwai kowacce rana.
29- ubangijin ka'aba shi ne Allah matsarkaki, adamu da matarsa hauwa'u(as) su suka gina ta da fasahar ginin mala'ika jibrilu(as) lokacin da ya zana iyakokin xakin daga jihhohi huxu da fuffukensa, kamar yadda ya zo cikin hadisi mai daraja cikin yadda fasahar ginin xakain ka'aba ya kasance a wasu riyoyin na daban.
29-ibrahimbadaxin Allah da isma'il sun xaga harsashin ginin xakin ka'aba bayan ruwan xufana na annabi nuhu(as) xakin ka'aba ya `yantu daga nutewa a xufana, sannan da shuxewa zamani amaliqa sun ginata sannan ta qara rugujewa sanna ta qara rushewa jurhumu suka ginata sai quraishwa suka sake ginata a zamanin manzon Allah(s.a.w) bayan sabanin mai tsanani ya gudana tsakaninsu kan wanda zai sanya dutsen hajarul aswad a mahallinsa, sai suka yadda annabi yay i musu hukunci tsakani, sai ya cire abayarsa ya ajiye hajarul aswad cikinta ya umarce quraishawa da kowanne ya kama gefan abayar sai suka kama suka xaga sai manzon Allah ya ajiye shi a a matsuguninsa. Sai hukunci manzon ya qayatar da su ya kuma yardarm da su daga sabaninsu, hajjaju xan yusuf saqafi ya ruguza ka'aba da majaujawa, imam sajjad(as) ya qara dawo da gininta, qissar hajjaju da ruguja xakin ka'aba bayanin haka ya zo filla-filla cikin littafin biharul anwar: juz 96 sh 52 mai son qaramin bayani sai ya koma ya duba.
31- matar isma'il daga qabilar himyarawa take ta tufatantar da ka'aba, shi kuma isma'il yay i mata rufi, xakin ka'aba ya a qofa biyu xaya ta shiga xaya ta fita, aka bashi hadaya daga dabbobin ni'ima, hadaya a daga sunnonin hajji[72]
32- sarkin muminai ali(as) ya aika da tufafin ka'aba duk shekara daga Iraqi.
() 33 ـ عن أبي عبدالله 7: إن لله عزّوجلّ حرمات ثلاث ليس مثلهنّ شيء: كتابه وهو حُكمه ، ونوره ، وبيته الذي جعله قبلة للناس لا يقبل من أحد توجهاً إلى غيره ، وعترة
نبيّكم :
33-Daga baban Abdullah(as) lallai Allahmai girma da xaukaka yana da alfarmomi uku da babu wani abu misalinsu: littafinsa wanda shi ne hukuncinsa da haskensa, xakinsa wanda ya sanya shi alqibla ga mutane bai karbar aiki face wanda ya fuskance ta, da zuriyar annabinku.
34 Allah ya mabata xakinsa mai alfarma cikin littafinsa wuarare goma sha'shida, wurare biyu daga ciki ya danganta xakin ga kansa(ku tsarkake xakina) ( ka tsarkake xakina) ma'ana xaixaiko da jama'a a wani wurin kuma annabi Ibrahim (as) ya ce: (wajen xakinka) a wurare uku kuma aka danganta xakin ga mutane(xaki na farko da aka sanyawa mutane) (tsararre domin mutane) (makoma ga mutane).
35- wasu mutane daga yahudawa sun zo wajen manzon Allah(s.a.w) sai suka tambaye shi game dawasu abubuwa daga cikin abubuwa akwai cewa: manene ya sanya ake kiran xakin ka'aba da sunan ka'aba? Sai ya ce musu: saboda ita ka'aba taa tsakiyar duniya.
عن الامام الرضا 7: علّة وضع البيت وسط الأرض انّه الموضع الذي من تحته دحيت الأرض يوم 27 ذي القعدة ـ ليكون الفرض أي الحجّ لأهل المشرق والمغرب سواء [73]
36- daga imam rida(as) dalilin da ya sanya aka sanya xakin ka'aba tsakiyar qasa saboda ita ka'aba daga qarqashinta ne a ka shimfixa qasa ranar 27 ga watan zil qa'ada domin hajji ya kasance bai xaya ga mutanen gabas da na yamma.
عن أميرالمؤمنين علي 7 قال : اذا خرجتم حجاجاً إلى بيت الله عزّوجلّ ، فاكثروا النظر إلى بيت الله، فان لله عزّوجلّ مأة وعشرين رحمة عند بيته الحرام ، ستون منها للطائفين ، وأربعون للمصلّين ، وعشرون للناظرين [74].
37 an karbo daga sarkin muminai Ali(as) ya ce: idan kun fito domin ziyartar xakin Allah mai girma da xaukaka, to yawaita kallon xakin Allah, lallai Allah na da rahama 120 wajen xakinsa mai alfarma.
عن رسول الله 6: النظر إلى الكعبة حيالها (حبّاً لها) يهدم الخطايا هدماً.
38- daga manzon Allah(s.a.w) : kallon xakin ka'aba domin soyayya gareta ya na ruguza kurakurai matuqar ruguzawa.
عن الامام الصادق 7: من أيسر ما ينظر إلى الكعبة أن يعطيه الله بكلّ نظرة حسنة ، ويمحي عنه سيئة ، ويرفع له درجة
39 an karbo daga imam sadiq(as) : mafi qarancin ladan da za a baiwa wanda ya ke kallon xakin ka'aba shi ne abashi lada kyakkyawa aiki kan dukkannin kallon guda da ya yi.
ـ في فروع الكافي بسنده عن أبي عبدالله 7 قال : إن الله عزّوجلّ دحى الأرض من تحت الكعبة إلى منى ، ثمّ دحاها من منى إلى عرفات ، ثمّ دحاها من عرفات إلى منى ، فالأرض من عرفات وعرفات من منى ومنى من الكعبة[75]
40- an karbo daga baba nab dullah(as) ya ce: lallai Allah maxaukaki mai girama ya shimfixa qasa daga qarqashin xakin ka'aba ya zuwa mina, sannan ya shimfixata daga Arafat zuwa mina, saboda qasa daga Arafat take, Arafat kuma daga mina
عن أبي جعفر 7 عن آبائه : إن الله تبارک وتعالى أوحى إلى جبرئيل 7: انا الله الرحمن الرحيم ، واني قد رحمت آدم وحوّاء لمّا شكيا إليّ ما شكيا، فاهبط عليهما بخيمة من خيم الجنّة ، وعزّهما عنّي بفراق الجنّة ، وأجمع بينهما في الخيمة ، فاني قد رحمتهما لبكائهما ووحشتهما في وحدتهما، وانصب الخيمة على الترعة التي بين جبال مكّة ، قال : والترعة مكان البيت وقواعده التي رفعتها الملائكة قبل آدم 7، فهبط جبرئيل 7 على آدم بالخيمة على مقدار أركان البيت وقواعده فنصبهما.
41 Daga baban jafar daga babanninsa(as) : Allah maxaukaki da albarka ya yi wahayi ga jibrilu(as) nine Allah mai rahama mai jin qai, lallai haqiqa ni na yi rahama ga adam da hauwa'u ya yin da suka kai kuka sai saukar musu da haima daga aljanna, da tsananin baqin ciki kan rabuwa da aljanna, iana haxa tsakaninus a cikin haima, alle haqiqa ni na yi rahama garesu sakamkon kuka da suka yi da kaxaitar da suka shiga cikin xayantarsu, in kafa haima kan magudanar ruwa wadda ke tsakanin manya duwatsun makka, tar'atu shi mhallin xaki da harsashin gininsa wanda mala'iku suka xaga tun gabanin adamu(as) sai jibrilu(as) ya saukowa adamu da haima gwargwadon rukunan xakin ka'aba da harsashensa sai ya qafa su.
قال : وأنزل جبرئيل آدم من الصفا، وأنزل حوّاء من المروة ، وجمع بينهما في الخيمة ، قال : وكان عمود الخيمة قضيب ياقوت أحمر فأضاء نوره وضوؤه جبال مكّة وما حولها، قال : وإمتدّ ضوء العمود قال : فهو موضع الحرم اليوم من كلّ ناحية من حيث بلغ ضوء العمود، قال : فجعله الله حرماً لحرمة الخيمة والعمود لانّهما من الجنّة قال : ولذلک جعل الله عزّوجلّ الحسنات في الحرم مضاعفة والسيّئات مضاعفة ، قال : ومُدّت أطناب الخيمة حولها فمنتهى أوتادها ما حول المسجد الحرام ، قال : وكانت أوتادها من عقيان الجنّة وأطنابها من ضفائر الأرجوان
Ya ce: sai ya sauko da adamu daga dutsen safa ya sauko da hauwa'u daga dutsen marwa, sai ya haxa su cikin haima, ya ce: amudin haimar ya kasance daga itacen yaqutu ahmar sai haskensa ya hasakaka manya manayn duwatsun garin makka da daura da ita, ya ce: sai hasken amudin ya miqe, ya ce: a wannan zamani shi ne mahallin harami daga kowacce nahiya ta inda hasken amudi ya kai, ya ce: sai ya sanya shi harami saboda alfarmar haima domin ita daga aljanna aka kawota, saboda haka ne Allah ya sanya kyawawan ayyuka ckin harami ababen ninkawa cikin ladansu, haka zabar munana ayyuka an ninninka su a cikin harami, ya ce: an miqar da igiyar haima keawaye da xakin ka'aba tuqewar turakunta shi ne daura da masallaci harami, ya ce turakunta sun kasance daga zinariyar aljanna. Igiyar ta kuma daga bishiyar arjuwan.
قال : وأوحى الله عزّوجلّ إلى جبرئيل 7: إهبط على الخيمة بسبعين ألف
ملک يحرسونها من مردة الشياطين ويؤنسون آدم ، ويطوفون حول الخيمة تعظيماً للبيت والخيمة ، قال : فهبط بالملائكة فكانوا بحضرة الخيمة يحرسونها من مردة الشياطين العتادة ، ويطوفون حول أركان البيت والخيمة كلّ يوم وليلة ، كما كانوا يطوفون في السماء حول البيت المعمور، قال : «وما أركان البيت الحرام في الأرض» حيال البيت المعمور الذي في السماء.
Ya ce: sai Allah mai girma da xaukaka yay i wahayi ga jibrilu(as) ya ce mas aka sauka kan haima tare da mala'iku dubu saba'in da za suyi gadinta daga shaixaanu su kuma xebewa adamu hasu da sanya masa nutsuwa, suyi xawafi daura da ka'aba domin girmamawa ga xakin da haima, ya ce: sai mala'iku suka sauko suka kasance cikin hallarar haima suna gadinsa daga sharrin shaixanu masu tsaurin kai, suna xawafi daura da xakin ka'aba kamar yadda suka kasance suna xawafi a baitul ma'amur, ya ce: menene rukunan xakin mai alfarma cikin qasa, saitin baitul ma'amur wanda yake samaniya
ثمّ قال : انّ الله عزّوجلّ أوحى إلى جبرئيل 7: بعد ذلک أن إهبط إلى آدم وحوّاء فنحّهما عن مواضع قواعد بيتي ، وإرفع قواعد بيتي لملائكتي ثمّ لوُلد آدم 7، فهبط جبرئيل على آدم وحوّاء، فأخرجهما من الخيمة ، ونحّاهما عن ترعة البيت ، ونحّى الخيمة عن موضع الترعة ، قال : ووضع آدم على الصفا، وحوّاء على المروة ، فقال آدم 7: يا جبرئيل أبسخط من الله عزّوجلّ حوّلتنا وفرّقت بيننا أم برضاً وتقدير علينا؟ فقال لهما: لم يكن بسخط من الله عليكما، ولكن الله لا يسأل عمّا يفعل ، يا آدم إن السبعين ألف ملک الذين أنزلهم الله إلى الأرض ليؤنسوک ويطوفوا حول أركان البيت المعمور والخيمة ، سألوا الله أن يبني لهم مكان الخيمة بيتاً على موضع الترعة المباركة حيال البيت المعمور، فيطوفون حوله كما كانوا يطوفون في السماء حول البيت المعمور فأوحى الله عزّوجلّ إليّ أن أُنحّيک وأرفع الخيمة ، فقال آدم 7: قد رضينا بتقدير الله ونافذ أمره فينا، فرفع قواعد البيت الحرام بحجر من الصفا، وحجر من المروة ، وحجر من طور سيناء، وحجر من جبل السلام ، وهو ظهر الكوفة ، وأوحى الله عزّوجلّ إلى جبرئيل أن إبنه وأتمّه ، فاقتلع جبرئيل الأحجار الأربعة بأمر الله عزّوجلّ من مواضعهنّ بجناحه ، حيث أمر الله عزّوجلّ في أركان البيت على قواعده التي
Sannan ya ce: lallai Allah mai girma da xaukaka ya yi wahayi ga jibrilu (as) bayan haka ka sauka ka je wajen adamu da hauwa'u ka nisantar da su daga mahallan harsashin ginin xakina, ka xaga xakina ga mala'iku sannan ga `ya`yan adamu(as) sai take mala'ika jibrilu (as) ya sauka wajen adamu da hauwa'u ya fitar da su daga haima, ya nesanta su daga magudanar ruawan xakin, ya xauke haima daga mahallin magudana, ya ce: sai ya xora adamu kan dutsen safa, ya xora hauwa'u kan marwa, sai adamu(as) ya ce: ya jibrilu shin sakamakon fushi daga Allah ka xauke mu daga mahallinmu ka raba mu da junan mu ko kuma saboda yardarsa da girmamawarsa garemu kai mana haka? Sai jibrilu ya ce musu: ba saboda fushi daga Allah hakan ya kasance ba, sai dai cewa shi Allah ba'a tambayarsa abin da yake aikatawa, ya adamu lallai amala'iku dubu saba'in da Allah ya saukar zuwa ban qasa lallai za su dinga xebe muku haso da sanya muku nutsuwa za su yi xawafi daura da rukunan baitul ma'amur da haima, sun roqi Allah da ya gina musu wani xaki kusa da haima kan wajen magudana mai albarka sai tin baitul ma'amur sai su yi xawafi daura da shi kamar yadda suka kasance suanyi a sama a baitul ma'amur, sai Allah ya yi wahayi gareni da in xaukeka in nesantaka in xage haimar, sai adamu(as) ya ce: lallai mun yarda mun aminci da abin da Allah ya qaddara da zartaccen umarninsa cikin mu, sai ya xaga harsashin ginin xaki mai alfarma da dutse daga safa da wani dutsen daga marwa da wani dutsen daga xuru sina'I da wani daga jabalul salam wanda yake tsakiyar kufa, Allah ya yi wahayi ga jibrilu da cewa ya gina xakin ka'aba ya cika ginin, sai jibrilu ya xauko duwatsu huxu da muka ambata daga matsugunansu da fukafukansa biyu cikin umarnin Allah mai girma da xaukaka, ya ajiye su inda Allah ya umarce shi cikin rukunai huxu a kan harsashenta waxanda Allah ya qaddara su.
قدّرها الجبّار، ونصب أعلامها، ثمّ أوحى الله عزّوجلّ إلى جبرئيل 7 أن إبنه واتمّه بحجارة من أبي قبيس وإجعل له ما بين باباً شرقيّاً وباباً غربيّاً قال : فاتمّه جبرئيل 7 فلمّا أن فرغ طافت حوله الملائكة ، فلمّا نظر آدم 7 وحوّاء إلى الملائكة يطوفون حول البيت ، إنطلقا فطافا سبعة أشواط ، ثمّ خرجا يطلبان ما يأكلان[76]
ya qafa tutocinta. Sannan Allah mai girma da xaukaka ya yi wahayi ga jibrilu(as) ka gin aka kammala shi da dutse daga abu qabisu ka sanya mashi qofa tsakanin gabas da yamma, ya ce; sai jibrilu ya cika ya kammala shi, sai adamu suka yi xawafi suka kewaya xakin sau bakwai, sannan suka fito suna neman abincin da za su yi kalace da shi.
42- haqarquran ka'aba a duniya mada da xabi'a, yana misaltuwa da bayyana cikin duniyar misaltuwa, shi ne baitul ma'amur a sama ta huxu, lallai abin da yake duniyar misaltuwa ma'ana baitul ma'amur lallai shi ya ishara da nuna alama zuwa ga duniyar abubuwa marasa jikkuna wato al'arshi cikin sama ta bakwai, sannan su abubuwa marasa jikkuna tajallin sunayan ubangiji suke.
Tasarin ubangijintaka cikin baqan sauka da na hawa yana tajalli cikin martabobin samuwa ta hankali mara jiki ta xabi'a da misaltuwa, ya yi isharar wannan abubuwa cikin matabobi uku: al'arshi da baitul ma'amur da xakin ka'aba. Kowannne guda cikinsu yana kan saiti xayan yana fuskantarsa, da za a wurgo da wutse daga baitul ma'amur da ke sama ta huxu da kai tsaye zai faxi kan rufin xakin ka'aba, kamar yadda hakan ya zo cikin hadisi mai daraja:
43- Allah matsarkaki da kansa ya ba da umarnin gina xakin ka'aba, jibrilu shi ne ya tsara fasahar ginin shi kuma damu (as) ya zartar da gini, sannan Ibrahim da isma'il(as)
(وَإِذْ بَوَّأْنَا لاِبْرَاهِيمَ مَكَانَ آلْبَيْتِ أَن لاَّ تُشْرِکْ بِي شَيْئاً) [77]
Lokacin da muka iyakncewa Ibrahim mahalli xaki, ka da kai mini abokin tarayya.
Sai aka gina ka'aba kan tushen tauhidi tun farko farin gininta.
(وَإِذْ يَرْفَعُ إِبْرَاهِيمُ آلْقَوَاعِدَ مِنَ آلْبَيْتِ وَإِسْمَاعِيلُ رَبَّنَا تَقَبَّلْ مِنَّا إِنَّکَ أَنْتَ آلسَّمِيعُ آلْعَلِيمُ ) [78]
Yayain da Ibrahim ke xaga harsashin gini da isma'il ubangijin mu ka krba daga garemu lallai kai maiji masani.
Wannan xaki na Allah ya kasance alqiblar xukanan Allah a ban qasa.
(فِي بُيُوتٍ أَذِنَ آللهُ أَن تُرْفَعَ وَيُذْكَرَ فِيهَا آسْمُه)ُ.[79]
44- jagorancin addini da wilaya mai girma ga imam cikin duniyar xabi'a da kasantuwa na matsayin ka'aba
(مثل الامام مثل الكعبة اذ تُؤتى ولا تاتي )
misalin imami cikin mutane kamar misalin ka'aba ne ya yin da zuwar ma ake ba ita take zuwar mutane ba.
wajibi e ga mutane su tattaru wajen imamin zamaninsu su ziyarce shi su nufe shi suyi ta maimaita hakan ba yankewa, kamar yadda ka'aba ta kasance lallai ita ana ziyartatta bawai ita ke ziayrta ba, su karbi koyarwar addininsu daga imamin zamaninsu da wanda ya ke wakilinsa kebantaccen wakilinsa da game gari kamar misalin malaman fiqihu adalai da maraji'a na gaskiya.
ـ عن الصادق 7: من أتى الكعبة فعرف من حقّنا وحرمتنا مثل الذي عرف من حقّها وحرمتها لم يخرج من مكّة ، إلّا وقد غفر له ذنوبه ، وكفاه الله ما يهمّه من أمر دنياه وآخرته
45- an karbo daga imam sadiq(as): duk wanda ya je ma ya san haqqinumu da alfarmu misalin wanda ya haqqinta da alfarmarta ba zai fita daga makka ba face an yafe masa zunubansa, Allah ya ingije msa abin da yake damunsa daga lamarin duniyarsa da lahirarsa.
46- haqiqa Ibrahim da isma'il sun tsarkake xakin ka'aba kamar yadda manzon Allah(s.a.w) da sarkin muminai Ali(as) suka tsarkake ta daga bautar gumaka cikinta, ali(as) ya hau kan kafaxar manzon rahama ya wurgo gumakan dake kan saman xakin ka'aba, ya ce:
(فوالذي فلق الحبّة وبرء النسمة لو أردت أن أمسک السماء لمسكتها(
Na rantse da wanda ya halicci kwaya ya qagi xan adam da ina son damkar sama da na damketa.
() 47 ـ في العلل عن حنان قال : قلت لأبي عبدالله 7 لِمَ سمّي بيت الله الحرام ؟ قال : لأنّه حرم على المشركين أن يدخلوه[80] .
Ya zo cikin ilal daga hannanu ya ce: na cewa baban Abdullah me yasa ake ka'aba da sunan xaki mai alfarma? Sai ya ce: saboda Allah ya haramtwa mushrikai shiga cikinta.
Wannan xan cikin cokali ne daga kwararar faila cikin sirrikan xakin ka'aba
1 lallai dutsen hajarul aswad yana da tarsihi mai ts.a.wo da asali wanda yake komawa ga duniyar kwayar zarra da duniyar haske da abubuwa marasa jikkuna, lallai shi dutsen hajarul aswad mala'ika ne makusanci wajen Allah matsarkaki, ya kasance mai xebe haso da sanya nutsuwa ga annabi adamu(as) a cikin aljanna, lokacin da Allah ya riqi alqawali daga adamu a duniyar kwayar zarra kamar yadda Ambaton hakan ya gabata
(ألَسْتُ بِرَبِّكُمْ قالُوا بلى )
Ashe ba ni ne ubangijinku ba suka ce na'ma kai ne.
Allah ya wurga Kalmar na'am Kalmar tauhidi da annabta da imamanci cikin bakin adamu domin ya kafawa mutane hujja da ita ranar qiyama bisa iqirarinsu da ita a baya a duniyar kwayar zarra, da faxinsu na'am cikin amsarsu, lokaci da adamu ya sauko qasa Allah ya karbi tubansa yay i shauki da bege aljanna sai Allah ya sauko masa da wannan mala'ika da siiffar dutse da farar lu'ulu'u da ke farntawa masu kallonta, aka kira shi da sunan hajarul as'ad domin adamu(as) ya yaye baqin cikinsa da shi, domin ya yi shaida kan mutane ga wanda ya je hajji cikakke hajji da cikakke imani kammalle da ya surantu da tauhidi da annabta da imamnci, daga nan ne ya zama mustahabbi ga mhajjaci da mahajjaciya cikin xawifinsu su faxi:
(إشهد لي بالموافاة )
Ka shaida mini da cikawa.
Ma'ana na cika abin da nayi imani da shi a duniyar kwayar zarra daga xayanta Allah da imani da manzon Allah(s.a.w) cika makin annabawa sannanimani da halifofinsa gasgatattu imamai tsarkaka ma'asumai bayansa sune sarkin muminai aliyu da imamai sha'xaya daga `ya`yansa.
قال أبو جعفر الباقر 7: والحجر كالميثاق واستلامه كالبيعة ، وكان إذا استلمه قال : اللّهمّ أمانتي أدّيتها وميثاقي تعاهدته ليشهد لي عندک بالبلاغ .
Baban jafar(as)ya ce: shi dutse kamar misalin alqawali ne sumbatarsa kamar mubaya'a ce, ya kasance iadan ya sumbace shi ya na cewa: Allah amana ta da na sauke , alqawali na wanda na xauka domin ya mini shaida da isarwa a wurinka.
ونظر 7 إلى ناس يطوفون وينصرفون فقال : والله لقد أُمروا مع هذا بغيره ، قيل : وما اُمروا به يابن رسول الله؟ قال : اُمروا إذا فرغوا من طوافهم أن يعرضوا علينا أنفسهم .
Imam (as) ya kalli mutane ya yin da suke xawafi suke juyawa su tafi sai ya ce: wallahi an umarce da su haxa wannan da tare da waninsa, sai aka tambaye shi menene wanin nasa ya xan manzon Allah? sai ya ce: an umarce su idan suka gama xawafinsu su bijiro da kawukansu garemu.
Sannan cikin mutane akwai waxanda suka kafircewa Allah suka manta da abin da suka faxa a duniyar kwayar zarra, daga cikinsu akwai waxanda suka kafirta daga cika makin annabawa muhammadu(s.a.w) daga cikinsu akwai waxanda suka yi inkarin wasiyyin annabi bayansa.
Yana nuni da shiryawa kan saukowar adamu daga aljanna abubuwan da suka sauko daga cikinta kamarb misalin ragon da aka fanshi isma'il
(وَإِن مِّن شَيْءٍ إِلاَّ عِنْدَنَا خَزَائِنُهُ وَمَا نُنَزِّلُهُ إِلاَّ بِقَدَرٍ مَعْلُومٍ )[81]
Babu daga wani abu face wajen mu akwai taskarsa ba ma saukar da shi face da gwargwado sananne.
(خَلَقَكُم مِن نَفْسٍ وَاحِدَةٍ مَّ جَعَلَ مِنْهَا زَوْجَهَا وَأَنزَلَ لَكُم مِنَ آلانْعَامِ ثَمَانِيَةَ أَزْوَاجٍ )[82]
Ya halicce ku daga rai kwaya xaya sannan ya sanya ma'aurata daga gareta ya saukar muku daga dabbobi nau'I takwas.
(وَأَنزَلْنَا آلْحَدِيدَ فِيهِ بَأْسٌ شَدِيدٌ وَمَنَافِعُ لِلنَّاسِ ) [83]
Kuma muka saukar da baqin qarfe cikinsa akwai cutarwa ma tsanani da alfanu ga mutane.
Saukarwa bai da ma'anar halitta kamar yadda hakan yake a bayyane, lallai yana da ma'aar tajalli ba qauracewa.
(مَا عِندَكُمْ يَنفَدُ وَمَا عِندَ آللهِ بَاقٍ )[84]
Abin da ke gareku zai qre abin da ke wurin Allah shi ne mai wanzuwa.
Ka da a kore saukar dutsen hajarul aswad daga sama.
2 lallai hajarul as'ad dutse ne da yaksance fari tas qal, sai yay i baqin qirin sakamakon shafar da mushrikai da munafukai suke masa, sai sunansa ya canja daga farin dutse zuwa baqin dutse ya kuma shahara da haka.
عن الامام المعصوم 7: «ان الحجر كان درّة بيضاء في الجنّة وكان أشدّ بياضاً من اللبن فاسودّ من خطايا بني آدم ، ولو لا ما مسّته من أرجاس الجاهليّة ، ما مسّه ذو عاهة إلا برأ. [85]
An karbo daga imami ma'asumi(as) lallai shi hajarul aswad ya kasance farin lu'ulu'u mai haske cikin aljanna ya kasance yana da tsananin haske, sai yay i baqi saboda laifukan mutane, ba da ban najasar jahiliya ta shafe shi ba da babu wani ma'abocin cuta da zai shafe shi face ya samu waraka.
3 xaki na farko da kasa sanya domin mutane shi ne xakin ka'aba, sannan abu na fari cikin ka'aba shi ne dutsen hajarul aswada, nan ne mahalli na farko cikin fara xawafi kuma mahallin qarshe da ake hattama kewaye na qarshe cikin xawafi, cikin kowanne xawafi daga dutsen hajarul aswad ake farawa ya zuwa gareshi ake tuqewa, ma'ana daga Allah zuwa ga Allah, shi ne xigon qasa na harafin ba'un xin cikin bismillah, mamakin wannan xigo da yake qasan harafin ba'un.
4- imam mahadi(af) ya yin bayyanarsa zai jingina jikin dutsen hajarul aswad:
قال الامام الصادق 7: «وإلى ذلک المقام يستند القائم ظهره ، وهو الحجّة والدليل على القائم ، وهو الشاهد لمن واخاه في ذلک المكان ، والشاهد على من أدّى إليه الميثاق والعهد الذي أخذ الله عزّوجلّ على العباد[86]
Imam sadiq(as) ya ce: ya zuwa wancan muqami imam zai jingina bayansa, shi hujja ne dalili kan qa'im, shi shaida ne ga wanda ya `yan uwance shi a wannan waje, shaida kan wanda ya sauke alqawalin da ya xaukar ma Allah mai girma da xaukaka.
5- dutsen hajarul aswad daman Allah a ban qasarsa:
عن أبي عبدالله الصادق 7 قال : «مرّ عمر بن الخطاب على الحجر الأسود فقال: والله يا حجر انّا لنعلم انّک حجر لا تضرّ ولا تنفع ، إلّا إنّا رأينا رسول الله 6 يحبّک فنحن نحبّک ، فقال له أميرالمؤمنين 7: كيف يابن الخطّاب ؟! فوالله ليبعثنه يوم القيامة وله لسان وشفتان فيشهد لمن واخاه ، وهو يمين الله في أرضه ، يبايع بها خلقه ، فقال عمر: لا أبقانا الله في بلد لا يكون فيه علي بن أبي طالب[87] .
An karbo daga baban Abdullah sadiq(as) ya ce: umar ibn kaxxanb ya gigta ta gefan hajarul aswad sai ya ce: wallahi ya kai dutsen hajarul aswad lallai mu munsan cewa dutse bai cutarwa ko amfaarwa, sai dai cewa munga manzon Allah(s.a.w) yana sonka saboda haka muma muna sonka, sai sarkin muminai Ali(as) ya ce: ta qaqa ya ibn kaxxab? Wallah za a tashe shi ranar qiyama yana da harshe da lebba biyu zai shaida ga wanda ya je wajensa, alle shi daman Allah ne aban qasa da akewa Allah mubaya'a a da shi, sai umar ya ce: kada Allah ya wanzar damu cikin garin da babu aliyu ibn abu xalibi(as)
قال الامام 7 «هو يمين الله عزّوجلّ في أرضه يبايع بها خلقه » ويشهد كما يشهد الأرض والجوارح يوم القيامة على الانسان وللانسان ، فهو من حجج الله في الأرض .
Imam (as) ya ce: shi dutsen hajarul aswad shi ne daman Allah mai girma da xaukaka a ban qasa halittusan nay i masa mubaya'a da shi, yana yin shaida kamar yadda qasa da gabbai ke yin shaida kan mutum ranar qiyama, lallai shi yana daga cikin hujjojin Allah cikin qasa.
قال الامام الصادق 7 تكذيباً لمن قال إنّ الحجر لا ينفع : «كذب ثمّ كذب ثمّ كذب إنّ للحجر لساناً ذَلقاً يوم القيامة ليشهد لمن وافاه بالموافاة » ومن أجل
ذلک أمرتم أن تقولوا اذا استلمتم الحجر: أمانتي أدّيتها وميثاقي تعاهدته لتشهد لي بالموافاة يوم القيامة. [88]
Imam sadiq(as) domin qaryata wanda ya ce dutsen hajarul aswad bai amfanarwa, ya ce: qarya kake qarya kake lallai dutsen hajarul aswad na da harshe zai yi shaida ga wanda ya je gareshi ranar qiyama da cikawa, sabodahaka ne ma aka umarceku ya yin da kuka gama sumbatarsa da ku faxi: na sauke amanita da alqawalin da na xauka saboda haka kai mini shaida da cikawa ranar qiyama.
Wannan yana daga cikin abubuwan da dutsen hajarul aswad ya kebantu da su. Amma duwatsu xakin ka'aba sarkin muminai ali(as) game da su ya ce:
«أحجار لا تضرّ ولا تنفع ولا تبصر ولا تسمع ولكنّ جعلها الله إختباراً لعباده ، ليعلم من هو المسلم أمره ، أمر من دون أي إعتراض أو مناقشة وهل الدين إلّا التسليم لحكم الله والرضا بقضائه وقدره (إِنَّ آلدِّينَ عِندَ آللهِ آلاْسْلاَمُ ) [89] والاسلام هو التسليم .
Su duwatsu ne da basa cutarwa ko amfanarwa basa ji ko gani sai dai cewa Allah ya sanya su domin jarrabawa ga bayinsa, domin ya san wanene daga cikinsu mai sallamwa ga lamarinsa, umarnine ba tare da kowacce irin jayayya ba ko tattaunawa shin wai menene addini da ya wuce sallamawa ga hukuncin Allah da yarda da zartarwarsa da qaddararsa(lallai addini wajen Allah shi ne muslunci) sannan ba wani abu ne muslunci ba face sallamawa.
6- dutsen hajarul aswad da rukunul yamani suna da matsayin jihhar dama cikin al'arshin Allah duk wanda ya sumbace shi dadaidi yake da wanda ya sumbaci daman al'arshin Allah, dukkanin hannuwansa dama ne babu hagu ma'ana masu albarka.
ـ في فروع الكافي بسنده عن بكير بن أعين قال : سألت أبا عبدالله7 لأيّ علّة وضع الله الحجر في الركن الذي هو فيه ، ولم يوضع في غيره ؟ ولأيّ علّة يقبّل ؟ ولأيّ علّة اُخرج من الجنّة ؟ ولأيّ علّة وضع ميثاق العباد والعهد فيه ، ولم يوضع في غيره ؟ وكيف السبب في ذلک أتخبرني جعلني الله فداک فان تنكّري فيه لعجب قال : فقال : سألت وأعضلت في المسألة وإستقيصت ، فافهم الجواب ، وفرّغ قلبک ، وأضع سمعک اُخبرک ان شاء الله، ان الله تبارک وتعالى وضع الحجر الأسود وهي جوهرة اُخرجت من الجنّة إلى آدم 7.
Daga furu'ul alkafi da isnadinsa daga bukairu ibn a'ayuni ya ce: na tambayi baban Abdullah(as) saboda wanne dalili Allah ya sanya dutesn hajarul aswad cikin rukunul yamani wanda yake cikinsa kuma bai sanya a waninsa ba? saboda me ake sumbatarsa? Saboda me aka fito da shi daga aljanna? Da wanne dalili aka sanya alqawalin bayi cikinsaba a kuma sanya cikin waninsa ba? yaya sababin ya ke cikin haka shin z aka iya bani labari Allah ya sanya raina ya zama fansarka lallai inkarina cikinsa yana da ba da mamaki ya ce: sai ya ce: kayi tambaya ka tsananta cikin mas'ala ka zurfafa, saboda ka tsaya ka fuskaci jawabin da zai zo, ka karkaxe zuciyarka, ka buxe kunnuwa da sannu zan baka labari da yardarm Allah, lallai Allah mai albarka da xaukaka ya sanya dutsen hajarul aswad shi wata lu'ulu'a ce da aka fito da ita daga aljanna aka saukarwa adamu.
Ma buqata cikakken hadisin sai ya koma littafin(alhajji fil kitabu was sunna: sh 118
قال الامام أبو جعفر 7: والحجر كالميثاق ، واستلامه كالبيعة ، فكان إذا إستلمه قال : (اللّهمّ أمانتي أدّيتها وميثاقي تعاهدته ليشهد لي عندک بالبلاغ )
Imam baban jafar sadiq(as) ya ce: dutsen hajarul aswad misalin alqawali ne, sannan sumbatarsa kamar mubaya'a ne, imam ya kasance idan ya sumbace shi sai ya ce: Allah amanita da na sauke da alaqawalina da na xauka ya yi mini shaida wajenka da isarwa da cikawa.
Ai na cika abin da ka wajabta mini a duniyar kwayar zarra.
عن أبي عبدالله 7 قال : قال رسول الله 6: «استلموا الركن فانه يمين الله في خلقه يصافح بها خلقه مصافحة العبد أو الرجل ، يشهد لمن استلمه بالموافاة
An karbo daga baban Abdullah(as) ya ce: manzon Allah(s.a.w) ya ce: ku sumbaci rukuni lallai shi daman Allah ne cikin halittunsa da yake gais.a.wa da halittunsa irin gaisuwa bawa ko namiji.
قال 7 عند ما سئل عن تقبيل الحجر: «إنّ الحجر كان درّة بيضاء في الجنّة وكان آدم يراها، فلمّا أنزلها الله عزّوجلّ إلى الأرض نزل إليها آدم 7 فبادر فقبّلها عليه السلام فأجرى الله تبارک وتعالى بذلک السنّة[90]
10 -ya ce:lokace da aka tamabaye shi game dasumabatar dutsen hajarul aswad: lallai dutsen hajarul aswad ya kasance farin lu'ulu'u cikin aljanna adamu(as) ya kasance yaa kallonshi , lokacin da Allah mai girma da xaukaka ya sauko da shi qasa sai aka saukowa adamu da shi, sai adamu yay i gaggawa ya sumbace shi, sai Allah ya zartar da haka sunna cikin bayinsa.
() 11 ـ وفي العلل عن إبن العباس إنّ النبي 6 قال لعائشة وهي تطوف معه بالكعبة حين إستلما الركن وبلغا إلى الحجر: يا عائشة لو لا ما طبع الله على هذا الحجر من أرجاس الجاهليّة وأنجاسها، إذاً لاستشفى به من كلّ عاهة ، وإذن لالفي كهيئة يوم أنزله الله تعالى عزّوجلّ ، وليبعثهم الله على ما خلق عليه أوّل مرّة ، وإنه لياقوتة بيضاء من ياقوت الجنّة ، ولكن الله غيّر حسنه بمعصية العاصين وسترت بنيته عن الأئمّة والظلمة ، لأنّه لا ينبغي لهم أن ينظروا إلى شيء بدؤه من الجنّة ، لأن من نظر إلى شيء منها على جهته وجبت له الجنّة ، وان الركن يمين الله تعالى في الأرض ، وليبعثهم الله يوم القيامة وله لسان وشفتان وعينان ، ولينطقنّه الله يوم القيامة بلسان طلق ذلق يشهد لمن إستلمه بحق ، إستلامه اليوم بيعة لمن لم يدرک بيعة رسول الله 6
Cikin ilalu daga ibn abbas lallai annabi(s.a.w0 ya cewa a'isha tana halin [91]xawafi tare da shi daura da ka'aba lokacin da shi da ita suka sumbaci ruknil yamani suka kai ga dutsen hajarul aswad: ya a'isha ba da ban abin Allah ya rufe kan wannan dutse daga dattin jahiliya ba da idan aka nemi magani da waraka da shi daga dukkanin cuta da aka samu waraka, da kin same shi da surar da Allah ya saukar da shit un ranar da ya saukar da shi, lallai shi farin yaqutu ne daga yaqutun aljanna, sai dai cewa Allah ya canja kywaunsa sakamakon sabon masu sabo an suturce gininsa daga barin limamai da azzalumai, saboda bai dace suga abin da suka fara ganinsa ba tun a aljanna, saboda duk wanda ya kalli wani abu daga gareshi a jihharsa aljanna ta wajaba gareshi, alle rukuni daman Allah ne cikin qasa, Allah zai tashe su ranar qiyama yana da harshe da lebba biyu,lallai Allah zai sanya shi magana ranar qiyama da zazzakan harshensa zai yi shaida ga waxanda suka smbace shi da gaskiya.
Sumbatarsa a wannan zamani ga waxanda basu riski mubaya'ar manzon Allah(s.a.w) ba.
() 12 ـ في أمالي الطوسي : أخبرنا جماعة ، عن أبي المفضل ، قال : حدثنا أبونصر ليث بن محمد بن نصر بن الليث البلخي ، قال : حدثنا أحمد بن عبدالصمد بن مزاحم الهروي سنة احدى وسنتين ومأتين ، قال : حدثني خالي عبدالسلام صالح أبو الصلت الهروي ، قال : حدثني عبدالعزيز بن عبدالصمد القمي البصري ، قال : حدثنا أبوهارون العبدي ، عن أبي سعيد الخدري ، قال : حج عمر بن الخطاب في إمرته ، فلما افتتح الطواف حاذي الجَجَر الأسود ومرّ فاستلمه وقبله وقال : أقبلک واني لأعلم انک حَجَر لا تضر ولا تنفع ، ولكن كان رسول الله 6 بک حفيّاً ، ولولا أنّي رأيته يقبلک ما قبلتک
Cikin amali xusi: jama'a sun bamu labari daga abu mufaddal ya ce: abu nasru laisu ibn Muhammad ibn nasru ibn laisu balaki ya bamu labari ya ce: ahmad ibn abdul samad ibn muzahim alharawi ya bamu labari a shekara ta 261 ya ce: xan'uwan mahaifiyata abdus salam salihu abu salti alharawi ya bani labari ya ce: abdul aziz ibn abdul samad alqummi albasari ya bani labari, ya ce: abu haruna al'abadi daga abu sa'idu alquduri ya bani labari, ya ce: umar xan ibn kaxxabi ya yi hajji lokacin mulkinsa , lokacin da ya fara xawafi sai ya sahuntu da dutsen hajarul aswad ya gifta sai ya sumbaci hajarul aswad ya ce: ina sumbatarka lallai kuma ni nasan cewa kai dutse ne da baka cutarwa ko amfanarwa , sai dai cewa manzon Allah(s.a.w) ya kasance yana qaunarka da girmamaka ba da ban na ganshi yana sumbatarka da bazan taba sumbatarka ba.
قال : وكان في الحجيج علي بن أبي طالب 7 فقال : بلي والله انه ليضر وينفع . قال : فيم قلت ذلک يا أباالحسن ؟ قال : بكتاب الله تعالى . قال : أشهد أنّک لذو علم بكتاب الله تعالى ، فأين ذلک من الكتاب ؟ قال قوله تعالى : (وَإِذْ أَخَذَ رَبُّکَ مِنْ بَنيü آدَمَ مِنْ ظُهُورِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَأَشْهَدَهُمْ عَلى أَنْفُسِهِمْ أَ لَسْتُ بِرَبِّكُمْ قالُوا بَلى شَهِدْنا...)[92] وأخبرک ان الله تعالى لما
خلق آدم مسح ظهره فاستخرج ذريت ه من صلبه في هيئة الذر فألزمهم العقل وقرّرهم انه الرب وانهم العبيد، فأقروا له بالربوبية وشهدوا على أنفسهم بالعبودية ، والله عزوجل يعلم انهم في ذلک في منازل مختلفة ، فكتب أسماء عبيده في رقّ وكان لهذا الحَجَر يومئذ عينان حجه آدم ، ثم نوح من بعده ، ثم هدم البيت ودرست قواعده فاستودع الحَجَر من أبي قبيس ، فلما أعاد إبراهيم وإسماعيل بناء البيت وبناء قواعده واستخرجا الحَجَر من أبي قبيس بوحي من الله عزوجل فجعلاه بحيث هو اليوم من هذا الركن ، وهو من حجارة الجنة ، وكان لما انزل في مثل لون الدُّرَر بياضه وصفاء الياقوت ضيائه ، فسودته أيدي الكفار ومن كان يلمسه من أهل الشرک بغنائرهم ، قال : فقال عمر: لا عشت في اُمة لست فيها ياأباالحسن.[93]
Ya ce: ashe cikin mhajjatan akwai aliyu ibn abu xalibi(as) sai ya cewa umar lallai yana amfanarwa da cutarwa, sai umar ya ce a cikin me kake faxin haka ya baban Hassan? Ya ce cikin littafin Allah maxaukaki, sai umar ya ce ina shaida lallai kake ma'abocin ilimi ne daga littafin Allah maxaukaki amma ina kaga hakan cikin littafin Allah? Sai imam ya ce cikin faxinsa maxaukaki: (ya yin da ubangijinka ya riqi alqawali daga `ya`yan adamu daga bayayyakinsu a cikin zuriyarsu ya sanya su shaida a kn rayukansu ashe bani ne ubangijinku ba? sukace na'am mun shaida.) ina baka labari da cewa lokacin da Allah ya halicci adamu ya shafa bayansa sai ya fitar da zuriyarsa daga tsatsonsa cikin surar kwayar zarra sai ya sanya musu hankali ya tabbata musu cewa shi ubangiji ne su kuma bayinsa ne, sai sukayi iqirarin haka suka tabbatar da ubangijintaka gareshi suka yi shaida ga rayukansu bautantaka, Allah mai girma da xaukaka ya san cewa lallai su cikin masaukaine mabanbanta, sai ya rubuta sunayen bayainsa cikin takarda, a wannan lokaci dutsen hajarul aswad yana da idanu da harshe da laba biyu, sai ya ce masa buxe bakinka sai ya buxe bakinsa sai ubangiji ya wurga wannan takarda a bakinsa, sannan ya ce masa: ka yi shaida da cikawa ga waxanda ke bakinka ranar qiyama, lokacin da adamu(as) ya sauko, shi ma dutsen aka sauko da shi tare da adamu (as) sai ya sany shi a mahallin da kake daga wannan rukuni, mala'iku sun kasance suna yin hajji ga wannan xaki tu gabanin Allah ya halicci adamu, sannan daga baya shi ma adamu ya yi hajji sai nuhu, sannan xakin ya rushe harsashin gininsa ya bushe ya zama babu shi babu alamunsa sai aka aje wani dutse daga abu qabisu, lokacin da Ibrahim da isma'il suka sake dawo da ginin xakin da ginin harsashinsa sai suka fito da dutsen abu qabisu da wahayi daga Allah mai girma da xaukaka sai suka sanya shi a mahallin da yake yau daga wannan rukunilallai shi yana daga duwatsun aljanna, ya kasance lokacin da aka saukar da shi cikin misalin wannan launi na fararen lu'ulu'a da tacewar yaqutu cikin haskakarsa, sai hannayen kafirai da waxanda suka kasance suna shafarsa daga musrikai ya maida shi baqin qirin, sai umar ya ce: ka da Allah ya raya ni cikin wata al'umma da babau baban Hassan ckinta.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن ابن أبي عمير؛ ومحمّد بن إسماعيل ، عن الفضل بن شاذان ، عن صفوان بن يحيى ؛ وابن أبي عمير، عن عبدالرّحمن بن الحجّاج عن أبي عبدالله 7 قال : كنت أطوف وسفيان الثورىُّ قريب منّي فقال : يا أباعبدالله كيف كان رسول الله 6 يصنع بالحَجَر إذا إنتهى إليه ؟ فقلت : كان رسول الله 6 يستلمه في كلَّ طواف فريضة ونافلة ، قال : فتخلّف عني قليلاً فلمّا إنتهيت إلى الحَجَر جِزتُ ومشيت فلم أستلمه فلحقني فقال : ياأباعبدالله ألم تخبرني أنَّ رسول الله 6 كان يستلم الحَجَر في كلَّ طواف فريضة ونافلة ؟ قلت : بلى ، قال : فقد مررت به فلم تستلم ؟ فقلت : إنَّ الناس كانوا يرون لرسول الله6 مالا يرون لي وكان إذا انتهى إلى الحَجَر أفرجوا له حتّى يستلمه وإنّي أكره الزّحام .
13 -A cikin furu'ul alkafi daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga ibn abi umairu da muhammahdu ibn isma'il daga fadlu ibn shazan daga sufwanu ibn yahaya daga Abdur rahman ibn hajjaju daga baban Abdullah(as) ya ce: na kasance ina xawafi sufyanu sauri yana kusa dani sai ya ce: ya baban Abdullah yaya manzon Allah(s.a.w) yana yi da dutsen hajarul aswad idan isa inda yake? Sai nace: ya kasance yana sumbatarsa cikin kowanne xawafin farilla da na nafila, ya ce sai ya xan jan baya daga gareni kaxan, lokacin da kai ga dutsen hajarul aswad na gifta na wuce ban sumbace shi ba, ya riskeni ya ce: ya baban Abdullah ashe ba kai ne ka bani labari cewa lallai manzon Allah ya kasance yana sumbatarsa cikin kowanne xawafin wajibi da nafila? Sai n ace masa haka ne, sai ya ce haqiqa ka wuce ta gefansa ka gifta shi ka tafi ba tare da ka sumabce shi ba? sai nace masa: lallai mutane sun kasance suna ganin wani abu ga manzon Allah(s.a.w) wanda basa ganinsa gareni,ya kasance lokacin da yake xawafi idan ya tuqe wajen dutsen hajarul aswad sai mutane su buxa masa har ya samu damar sumbatarsa, lallai ni ina kyamar turmutsitsi da turmutsetseniya.
وفي التهذيب : موسى بن القاسم ، عن صفوان بن يحيى ، عن معاوية بن عمار، قال : سألت اباعبدالله 7 عن رجل حج ولم يستلم الحَجَر ولم يدخل الكعبة قال : هو من السنة فان لم يقدر فالله أولى بالعذر .
14-Ya zo cikin tahzib daga musa ibn qasim daga sufwanu ibn yahaya daga mu'awiya ibn ammar ya ce: na tambayi baban Abdullah(as) game damutumin da yay i hajji amma bai sumbaci dutsen hajarul aswad ba kuma bai shiga ka'aba ba, sai ya ce: lallai sumbatar na daga aiki na mustahabbi idan bai samu damar yi ba, lallai Allah shi ne mafi cancanta da ba da uzuri.
ـ في الفروع : عدَّةٌ من أصحابنا، عن أحمد بن محمّد، عن الحسين بن سعيد، عن صفوان ابن يحيى ، عن سيف التمار قال : قلت لأبي عبدالله 7 : أتتيت الحَجَر الأسود فوجدت عليه زحاماً فلم ألق إلّا رجلاً من أصحابنا فسألته فقال : لابدّ من استلامه فقال : إن وجدته خالياً وإلّا فسلّم من بعيد .
15- ya zo cikin furu'ul alkafi daga wasu adadi daga sahabban mu daga ahmad ibn Muhammad daga husaini ibn sa'id daga sufwanu ibn yahaya daga saifu ibn sammaru ya ce: na cewa baban Abdullah(as) na je wajen dutesn hajarul aswad sai na samu turmutsitsi kansa babu abin da haxu da shi sai wani mutum daga sahabbanmu sai na tambaye shi sai ya ce: ai dole ne ka sumbaci dutsen, sai ya ce: idan kasa me shi babu turmutsitsi idan ka samu turmutsitsi to kayi masa sallam daga nesa.
وفي الفروع : حميد بن زياد، عن ابن سماعة ، عن غير واحد، عن أبان بن عثمان ، عن محمّد الحلبيّ قال : سألت أباعبدالله 7 عن الحَجَر إذا لم أستطع مسّه وكثر الزّحام ؟ فقال : أمّا الشيخ الكبير والضعيف والمريض فمرخّص وما أحبُّ أن تدع مسّه إلّا أن لا تجد بدَّا .
16- ya zo cikin furu'ul alkafi daga hamidd ibn zayad ibn samma'atu daga wasu jama'a daga abbanu ibn usman daga muhammadu alhalabi ya ce: na tambayi baban Abdullah(as) game dadutsen hajarul aswad idan ban samuiko shafarsa sakamakon yawaitar turmutsitsi? Sai ya ce: amma tsoho da rarrauna da mara lafiya su an yafe musu, bana son ace ka bar shafarsa sai dai idan ba yadda za kai ka shafe shi.
وفي الفروع : عدَّة من أصحابنا، عن أحمد بن محمّد بن عيسى ، عن أحمد بن محمّد بن أبي نصر، عن محمّد بن عبيدالله قال : سئل الرّضا 7 عن الحَجَر الأسود وهل يقاتل عليه النّاس إذا كثروا؟ قال : إذا كان كذلک فأوم إليه إيماء بيدک .
17 -Ya zo cikin fru'ul alkafi daga wasu adadi daga sahabbanmu daga ahmad ibn muhammadu ibn abi nasru daga muhammadu ibn ubaidullah ya ce: rida (as) ya ce: dutsen hajarul aswad shin za'a iya yaqar mutane kansa idan suka yawaita? Sai ya ce: idan lamarin ya kai ga haka to taqaitu da yin ishara da hanunka.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن ابن أبي عمير، عن أبي أيّوب الخزّاز، عن أبي بصير، عن أبي عبدالله 7 قال : ليس على النساء جهر بالتلبية ولا استلام الحَجَر ولا دخول البيت ولا سعي بين الصّفا والمروة ـ يعني الهرولة ـ .
18- ya zo cikinfuru'ul alkafi daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga ibn umairu daga abu ayyubi alkazzaz daga abu basir daga baban Abdullah(as) ya ce: ba wajibi bane kan mata su bayyana karatun bismillah haka ma sumbatar dutsen hajarul aswad haka ma shiga xakin ka'aba da sassarfa tsakanin safa da marwa.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن ابن أبي عمير؛ ومحمّد بن إسماعيل ، عن الفضل بن شاذان ، عن ابن أبي عمير؛ وصفوان بن يحيى ، عن معاوية بن عمّار، عن أبي عبدالله 7 قال : إذا دنوت من الحجر الأسود فارقع يديک واحمد الله واثن عليه وصلّ على النبيّ 6 وأسأل الله أن يتقبّل منک ، ثم إستلم الحجر وقبّله فان لم تستطع أن تقبّله فاستلمه بيدک فان لم تستطع أن تستلمه بيدک فأشر إليه وقل : «اللّهمّ أمانتي أدَّيتها وميثاقي تعاهدته لتشهد لي بالموافاة ، اللّهمَّ تصديقاً بكتابک وعلى سنّة نبيّک أشهد أن لا إله إلّا الله وحده لا شريک له وأنَّ محمّداً عبده ورسوله آمنت بالله وكفرت بالجبت والطاغوت وباللّات والعزّى وعبادة الشيطان وعبادة كلَّ ندّ يدعى من دون
الله» فان لم تستطع أن تقول هذا كلّه فبعضه وقل : «اللّهمّ إليک بسطت يدي وفيما عندک عظمت رغبتي فاقبل سيحتي واغفر لي وارحمني ، اللّهمّ إنّي أعوذبک
من الكفر والفقر ومواقف الخزي في الدُّنيا والآخرة
19 – ya zo cikin furu'ul alkafi daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga ibn abi umairu daga muhammadu ibn isma'il daga falalau ibn shaxan daga ibn abi umairu daga sufwanu ibn yahaya daga mu'awiyatu ibn ammar adaga baban Abdullah(as) ya ce: idan ka kusanci dutsen hajarul aswad ka xaga hannayenka ka godewa Allah ka yaba maasa ka yi salati ga annabi(s.a.w) ka roqi Allah ya karba daga gareka, sannan ka sumbaci dutsen hajarul aswad ka rungumeshi, idan baka samu daman yin hakan ba to ka taba shi da hannunka idan baka samu dama ba to ka yi nuni da ishara zuwa gareshi, k ace: Allah na sauke amanita da alqawalina da na xauka domin kai mini shaida da cikawa, Allah saboda gasgata littafinka a kan sunnar annabinka ina shaidawa da babu abin bautawa da gaskiya sai Allah xaya babau abokin tarayya gareshi lallai muhammadu bawansa ne kuma manzonsa ne , nay i imani da Allah na kafircewa jibtu da xagutu da latu da uza da bautar shaixani da bautar dukkanin kishiya da ake bautawa koma bayan Allah, iadan ba z aka iya faxin haka ba to kace: Allah gareka na shimfixa hannuna cikin abin da ke gareka kwaxayina ya girmama ka karbi tafiyata, kai mini gafara kai mini rahama, Allah ina neman tsarinka daga kafirci da talauci da wuraren kunyata a duniya da lahira.
وفي الفروع : في رواية أبي بصير، عن أبي عبدالله 7 قال : إذا دخلت المسجد الحرام فامش حتّى تدنو من الحَجَر الأسود فتستقبله وتقول : «الحمد لله الذي هدانا لهذا وما كنا لنهتدي لولا أن هدانا الله سبحان الله والحمد لله ولا إله الّا الله والله اكبر، أكر من خلقه وأكبر ممّن أخشى وأحذر ولا إله الّا الله وحده لا شريک له ، له الملک وله الحمد يحيى ويميت ويميت ويحيي بيده الخير وهو على كل شيء قدير» وتصلّي على النبيّ وآل النبيّ صلّى الله عليه وعليهم وتسلّم على المرسلين كما فعلت حين دخلت المسجد، ثم تقول : «اللّهمّ إنّي أوْ من بوعدک وأوفي بعهدک » ثمّ ذكر كما ذكر معاوية .
20- ya zo cikin furu'ul alkafi cikin riwayar abu basir daga baban Abdullah(as) ya ce: idan ka shiga masallacin harami ka wuce har sai ka kaiga ka kusanci dutsen hajarul aswad sai ka fuskance shi kace: godiya ta tabbata ga Allah wanda ya shiryar da mu ga wannan bamu kasance masu shiriya ba badaban Allah ya shiryar damu ba, tsarki ya tabbata ga Allah godiya ta tabbata gareshi babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Allah shi ne mafi girma, daga halittunsa, mafi girma daga waxanda nake jin tsoro da razana, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai bai da abokin tarayya, mulki nasa ne godiya gareshi take yana raya ya kashewa hannunsa alheri yake, shi mai iko ne kan komai, ka yi salati kayi tsira ga annabi da iyalansa amincin Allah ya tabbata garesu, ka yi sallama ga manzanni kamar yadda ka aikata lokacin shigarka masallaci, sannan kace: Allah ni ina imani da alqawalina ina cika alqawalinka, sannan ya ambata kamar yadda mu'awiya ya ambata.
وفي الفروع : محمّد بن يحيى ؛ وغيره ، عن محمّد بن أحمد، عن موسى بن عمر، عن ابن سنان ، عن أبي سعيد القمّاط ، عن بكير بن أعين قال : سألت أباعبدالله 7 لأيّ علّة وضع الله الحجر في الرُّكن الّذي هو فيه ولم يوضع في غيره ؟ ولأيّ علّة يُقبّل ؟ ولأيّ علة اُخرج من الجنّة ؟ ولأيّ علّة وضع ميثاق العباد والعهد فيه ولم يوضع في غيره ؟ وكيف السبّب في ذلک ؟ تخبرني جعلني الله فداک فإنّ تفكّري فيه لعجب ، قال : فقال : سألت وأعضلت في المسألة
واشتقصيت فافهم الجواب وفرّغ قلبک واصغ سمعک أخبرک إن شاء الله إنّ الله تبارک وتعالى وضع الحَجَر الأسود وهي جوهرة أخرجت من الجنّة إلى آدم 7 فوضعت في ذلک الركن لعلّة الميثاق وذلک أنّه لمّا اُخذ من بني آدم من ظهورهم ذريّتهم حين أخذ الله عليهم الميثاق في ذلک المكان وفي ذلک المكان ترائي لهم
ومن ذلک المكان يهبط الطير على القائم 7 فأوّل من يبايعه ذلک الطائر وهو والله جبرائيل 7 وإلى ذلک المقام يسند القائم ظهره وهو الحجّة والدليل على القائم وهو الشاهد لمن وافا ]ه [ في ذلک المكان والشاهد على من أدّى إليه الميثاق والعهد الّذي أخذ الله عزّوجلّ على العباد.
وأمّا القبلة والاستلام فلعلّه العهد تجديداً لذلک العهد والميثاق وتجديداً للبيعة ليؤدُّوا إليه العهد الّذي أخذ الله عليهم في الميثاق فيأتوه في كلّ سنة ويؤدُّوا إليه ذلک العهد والأمانة اللّذين اُخذا عليهم ، ألا ترى أنک تقول : «أمانتي أدَّيتها وميثاقي تعاهدته لتشهد لي بالموافاة » ووالله ما يؤدّي ذلک أحد غير شيعتنا ولا حفظ ذلک العهد والميثاق أحدٌ غير شيعتنا، وإنّهم ليأتوه فيعرفهم ويصدقهم ويأتيه غيرهم فينكرهم ويكذّبهم ، وذلک أنّه لم يحفظ ذلک غيركم فلكم والله يشهد وعليهم والله يشهد بالخفر والجحود والكفر وهو الحجّة البالغة من الله عليهم
يوم القيامة يجيء وله لسان ناطق وعينان في صورته الاُولى يعرفه الخلق ولا ينكره ، يشهد لمن وافاه وجدّد العهد والميثاق عنده ، بحفظ العهد والميثاق وأداء الأمانة ويشهد على كلّ من أنكر وجحد ونسي الميثاق بالكفر والإنكار.
فأمّا علّة ما أخرجه الله من الجنّة فهل تدري ما كان الجَجَر؟ قلت : لا، قال : كان ملكاً من عظماء الملائكة عندالله فلمّا أخذ الله من الملائكة الميثاق كان أوّل من أمن به وأفرَّ ذلک الملک فاتّخذه الله أميناً على جميع خلقه فألقمه الميثاق وأودعه عنده واستعبد الخلق أن يجدّدوا عنده في كلّ سنة الإقرار بالميثاق والعهد الّذي أخذ الله عزّوجلّ عليهم ، ثم جعله الله مع آدم في الجنّة ، يذكّره الميثاق ويجدّد عنده الإقرار في كلّ سنة فلمّا عصى آدم واُخرج من الجنّة أنساه الله العهد والميثاق الّذي أخذ الله عليه وعلى ولده لمحمّد 6 ولوصيّه 7 وجعله تائهاً
حيراناً، فلمّا تاب الله على آدم حوَّل ذلک الملک في صورة درَّة بيضاء فرماه من الجنّة إلى آدم 7 وهو بأرض الهند فلمّا نظر إليه أنس إليه وهو لا يعرفه بأكثر من أنّه جوهرة وأنطقه الله عزّوجلّ فقال له : يا آدم أتعرفني ؟ قال : لا، قال : أجل إستحوذ عليک الشيطان فأنساک ذكر ربّک ، ثمّ تحوّل إلى صورته التي كان مع آدم في الجنّة فقال لآدم : أين العهد والميثاق فوثب إليه آدم وذكر الميثاق وبكى وخضع له وقبّله وجدّد الإقرار بالعهد والميثاق ، ثم حوله الله عزوجلّ إلى جوهرة الحَجَر درّة بيضاء صافية تضيء فحمله آدم 7 على عاتقه إجلالاً له وتعظيماً فكان إذا أعيا حمله عنه جبرائيل 7 حتّى واقابه مكّة فمازال يانس به بمكّة ويجدّد الإقرار له كلُّ يوم وليلة ، ثمّ إنّ الله عزّوجلّ لمّا بني الكعبة وضع الحَجَر في ذلک المكان لأنّه تبارک وتعالى حين أخذ الميثاق من ولد آدم أخذه في ذلک المكان وفي ذلک المكان ألقم الملک الميثاق ولذلک وضع في ذلک الرّكن فلمّا
نظر آدم من الصّفا وقد وضع الحَجَر في الرُّكن كبّر الله وهلّله ومجده فلذلک جرت السّنة بالتكبير واستقبال الرّكن الذي فيه الحَجَر من الصّفا فإنَّ الله أودعه الميثاق والعهد دون غيره من الملائكة لأنّ الله عزوجلّ لمّا أخذ الميثاق له بالرُّبوبيّة ولمحمد 6 بالنبوَّة ولعليّ 7 بالوصيّة اصطكْت فرائض الملائكة فأوّل
من أسرع إلى الإقرار ذلک الملک لم يكن فيهم أشدُّ حبّاً لمحمد وآل محمد 6 منه ولذلک اختاره الله من بينهم وألقمه الميثاق وهو يجيء يوم القيامة وله لسان ناطقف وعين ناظرة يشهد لكلّ من وافاه إلى ذلک المكان وحفظ الميثاق[94]
21- ya zo cikin furu'ul kafi: daga muhammadu ibn yahaya da wasunsa daga muhammadu ibn ahmad daga musa ibn umar daga ibn sinanu daga abu sa'id qammaxu daga bukairu ibn a'ayuni ya ce: na tambayi baban Abdullah(as) me yasa Allah ya sanya dutsen hajarul aswad cikin rukunul yamani da yajke cikinsa bai sanya shi a waninsa ba ? me yasa ake sumbatarsa? Me yasa aka fito daga cikin aljanna me yasa aka sanya alqawalin bayi cikinsa ba a sanya cikin waninsa ba? ta qaqa sababi yake cikin hakan? Ka bani labari raina fansarka lallai tunani cikinsa ya na da ban mamaki, ya ce: sai ya ce: kayi tambaya ka tsananta cikin tambayar ka zurafafa ka nesanta ciki, saboda haka ka tsaya ka fahimci jawabi, ka karkaxe zuciyarka ka kasa kunnuwa da sannu zan baka labari da yardar Allah, lallai Allah maxaukaki da albarku ya ajiye dutsen hajarul aswad shi lu'lu'u ne da aka fito da shi daga aljanna ya zuwa adamu(as) sai ka ajiye shi a wannan waje na rukunul yamani saboda dalilin alqawali hakan ta faru lokacin da aka riqa daga `ya`ya adamu daga bayayyakinsu a zuriyarsu lokacin da Allah ya riqi alqawali daga garesu a wannan waje cikin wannan waje na nune garesu daga wannan waje ne tsuntsun zai sauka kan imam mahadi shi ne kuma farkon wanda zai fara yi masa mubaya'a shi wannan tsuntsun wallahi bawani bane face mala'ika jibrilu(as) ya zuwa wannan muqam imam zai jingina bayansa shi hujja ne kuma dalili kan qa'im kuma shaida ne kan wanda ya je masa a wannan waje, shi shaida ne kan wanda ya sauke alqawali gareshi da amanar da Allah ya riqa kan bayi.
Amma sumbata da rungumar ta yiwu shi alqawali ne domin sabunta wancan alaqawali da sabunta mubaya'a domin su sauke alqawali gareshi wanda Allah ya riqa a kansu cikin alqwali, sais u zo kowacce shekara su sauke alakwalin da suka xauka da amana da aka riqa a kansu. Ashe baka lura da cewa kana faxin( amanita na sauketa da alaqawalina da na xauka domin ka shida mini da cikawa) wallahi bamu su iya sauke wannan alaqawali in banda shi'armu, babu wani da ya iya kiyaye wannan alqawali face shi'armu, lallai su suna zuwar masa sai ya sansu ya gasgata su, sannan wasunsu suna zuwarr masa sai ya yi inkarinsu ya qaryata su, hakan ta faru ne sakamakon babu waxanda suka kiyaye face ku , saboda ki kaxai wallahi zai yi shaida, a kansu su kuma zai shaida da tawaya da inkari da kafirci shi hujja ne maiiasarwa daga Allah a kansu ranar qiyama, ranar da zaizo da harshe mai Magana da idanuwa biyu cikin surarsa ta farko halittu sun sanshi ba za su yi inkarinsa ba, zai yi shaida ga duk wanda ya je wajensa ya sabunda alqawali a wurinsa, haka ma zai shaida kan wanda ya yi inkarinsa yay i jayayya ya mantar da alaqawali da kafircewa da inkari.
Amma dalilin fitar da shi daga aljanna, shin kasan me hajarul aswad ya kasance a da gabanin fitarsa daga aljanna? Sai nace a a, ya kasance mala'ika daga manyan mala'iku wajen Allah lokacin da ya riqi alqawali daga mala'iku yana daga cikin wanda ya fara imani dashi ya tabbatar da hakan ya yi iqirari, sai Allah ya riqeshi amintacce kan dukkanin halittunsa ya wuraga alqawali cikin bakinsa ya snya shi haxiya ya ajye s wajensa ya bautar da halittuda jaddada alqawali da xaukar ma Allah wajensa duk shekara, sannan ya sanya shi tare da adamu cikin aljanna yana tunatar da shi alqawalin da Allah ya riqa a kansa da `ya`yansa domin muhammadu (s.a.w) da wasiyyinsa(as) ya sanya shi ya ruxe da gigita yayain da Allah ya karbi tuban adamu sai Allah ya sauya wannan mala'iika zuwa surar lu'ulu'a mai haskaka sai aka fito da shi daga aljanna zuwa ga adamu(as) lokacin adamu yana qasar hindu(indiya) lokacinda ya kalli wannan lu'ulu'a sai ya samu nutsuwa ya xebe haso da shi alahalin bai ma sanshi ba sai Allah ya sanya wannan lu'ulu'a Magana ya ce: ya adamu shin kasanni kuwa? Sai adamu ya ce: a a, sai ya ce haka ne lallai shaixani yay i galaba kanka ya sanya ka mantawa da ambaton ubangijinka, sai wannan lu'ulu'a ya sauya ya koma surarsa da ya kasance da adamu a aljanna ya cewa adamu ina alqawalinka sai adamu ya yi futar burtu ya afka gareshi ya tunada alqawali ya fashe da kuka ya sunkuya gareshi ya sumbace shi ya sabunta iqirari da alqawali da amana, sai Allah ya qara mayar da shi surar lu'ulu'a mai haske da ke haskaka sai adama ya xauke shi kan wuyansa domin girmamawa gareshi ya kasance idan ya gajiya sai jibrilu ya xaukar mmasa shi har ya kawo shi makka, adamu baigushe ba yaa xebe haso da nutsuwa da shi a makka yana sabunta alqawali da iqiqrari gareshi cikin kowanne dare da rana , sannan Allah lokacin da ya gina ka'aba sai ya sanya dutsen hajarul aswad cikin wannan waje , saboda allah maxaukaki da albarku lokacin da ya riqi alqwali daga `ya`yan adamu ya riqi alqawalin daga wannan waje a wannan waje ne Allah ya sanya mala'ika ya haxiyi takardar alqawali saboda haka ne aka ajiye shi a wannan waje a wannan rukuni, yayain da adamu ya hango daga daga dutsen safa an ajiye hajarul aswad a rukunul yamani sai adamu ya yi kabbara da hailala ya yi girmammawa ga ubangiji, saboda haka sunna ta gudana cikin yin kabbara da fuskantar rukunul yamani wanda anan dutsen hajarul aswad yake daga safa, lallai Allah ya ajiye alqawali cikinsa koma bayan waninsa daga mala'iku saboda lallai Allah mai girma da xaukaka ya riqi alqawali gareshi da ubangijintaka sannan ga muhammadu(s.a.w) da annabta sannan ga aliyu(as) da wasicci, sai kafaxun mala'iku suka girgiza farkon wanda ya fara gaggawa da iqirarin haka shi ne wancan mala'ika cikin mala'iku babu wanda ya kaishi tsananin soyayya ga muhammadu(s.a.w) da iyalansa(as) saboda haka ne Allah ya zabe shi daga cikinsu ya sanya shi haxiye alaqawali, lallai shi zai zo ranar qiyama alhalin yana da harshe mai Magana da idaniya mai gani zai yi shaida ga dukkanin wanda ya je wajensa ya kuma kiyaye alqawali.
وفي العلل : حدثنا علي بن محمد؛، قال : حدثنا محمد بن
أبيعبدالله الكوفي ، عن محمد بن اسماعيل البرمكي ، عن علي بن عباس ، عن القاسم بن اربيع الصحاف ، عن محمد بن سنان ان أبا الحسن علي بن موسى الرضا 7 كتب اليه فيما كتب من جواب مسائله علة استلام الحَجَر، ان الله تبارک وتعالى لما أخذ مواثيق بني آدم التقمه الحَجَر فمن ثم كلف الناس بمعاهدة ذلک الميثاق ومن ثم يقال عند الحَجَر: «أماتتي أديتها وميثاقي تعاهدته لتشهد لي بالموافاة » ومنه قول سلمان 2 ليجين الحَجَر يوم القيامة مثل جبل أبي قبيس له لسان وشفتان يشهد لمن وافاه بالموافاة[95]
22- ya zo cikin ilalu: aliyu ibn muhammadu ya bamu labari ya ce: muhammadu ibn abi Abdullah alkufi ya bamu labari daga muhammadu ibn isma'il baramiki dagaaliyu ibn abbas daga qasim ibn rabi'u sahhaf daga muhammadu ibn sinanu cewa baban Hassan aliyu ibn musa rida(as) ya rubuta masa wasiqa cikin abin da ya rubuta daga amsar tambayoyi kan dalilin rungumar dutsen hajarul aswad, lallai Allah mai albarka da xaukaka lokacin da ya riqi alqawalin `ya`yan adamu sai ya sanya duten hajarul aswad haxiye wannan alqawali daga nan ya kallafawa mutane lazimtar wannan alqawali daga nan ake cewa a wajen dutse:(amanita na sauketa na lazimci alqawalina domin kai mini shaida da cikawa) daga nan ne faxin sulaimanu(as) lallai hajarul aswad zai amasa ranar qiyama kamar misalin dutsen abu qabisu, kuma yana da harshe da laba biyu zai yi shaida da cikawa kan dukkanin wanda ya je wajensa.
وفي العلل : اخبرني علي بن حاتم فيما كتب إلى قال : حدثنا جميل بن يزاد، قال : حدثنا احمد بن الحسين النخاس ، عن زكريا ابي محمد المؤمن ، عن عابر بن معقل ، عن أبان بن تغلب ، قال : قال أبوعبدالله 7: أتدري لأي شيء صار الناس يلثمون الحَجَر؟ قلت : لا، قال : ان آدم 7 شكى إلى ربه عزوجل الوحشة في الأرض فنزل جبرائيل 7 بياقوتة من الجنة كان آدم إذا مرت عليها في الجنة ضربها برجله فلما رآها عرفها فبادر يلثمها فمن ثم صار الناس يلثمون الحَجَر . [96]
23- ya zo cikin ilalu aliyu ibn hatim ya bani labari cikin abin da ya rubuta ya aika ya ce: kamilu ibn yuzadu ya bamu labari ya ce: ahmad ibn husaini nakkasu labari daga zakariyya abi muhammahamdu muminu daga abiru ibn ma'aqalu daga abbanu ibn taglibu ya ce: baban Abdullah(as) ya ce: shin kasan meyasa mutane ke sumbatar dutsen hajarul aswad? Sai nace: a a, sai ya ce: lallai adamu(as) ya kai kukan kaxaita da rashin nutsuwa ya zuwa ga ubangijinsa cikin qasa, sai mala'ika jibrilu ya sauko da yaqutu daga aljanna, adamu ya kasance idan ya gifta ta wajen wannan yaqutu a cikin aljanna sai ya zungureshi ya shureshi da qafarsa, ya yin da ya ga wannan yaqutu a duniya take ya gane shi sai ya yi gaggawa yaje ya sumbace shi, sai mutane suka zamanto suna sumbatarsa.
وفي الفروع : عدّة من أصحابنا، عن أحمد بن أبي عبدالله، عن عمرو بن عثمان ، عن عليّ بن خالد، عمّن حدّثه ، عن أبي جعفر 7 قال : كان أبي يقول : الدّاخل الكعبة يدخل والله راض عنه ويخرج عطلاً من الذنوب .[97]
24- ya zo cikin furu'ul kafi daga wasu adadi daga sahabbanmu daga ahmad ibn abi Abdullah daga amru ibn usman daga aliyu ibn Khalid daga wanda ya zantar da shi daga baban jafar(as) ya ce: babana ya kasance yana cewa: cikin xakin ka'aba wallahi wanda Allah ya yarda da shi yana shigarta kuma yana fitowa babu zunubi ko xaya gareshi zunubi ya wofinta gabarinsa.
وفي الفروع : محمد بن يحيى ، عن محمد بن أحمد، عن يعقوب بن يزيد، عن ابن فضّال ، عن ابن القدّاح ، عن جعفر، عن أبيه 8 قال : سألته عن دخول الكعبة ، قال : الدُّخول فيها دخول في رحمة الله، والخروج منها خروج من الذنوب ، معصوم فيما بقي من عمره مغفورٌ له ما سلف من ذنوبه[98] .
25 -Ya zo cikin furu'ul kafi daga muhammadu ibn yahaya daga muhammadu ibn ahmad daga yaqubu ibn yazidu daga ibn faddal daga ibn qaddahu daga jafar daga babansa(as)ya ce: na tamabaye shi game dashiga ka'aba sai ya ce: shiga cikinta shiga cikin rahamar Allah ne, fita daga cikinta fita daga cikin zunubi ne, sannan kuma wanda ya shiga zai kasance shingagge daga aikata zunubi cikin abin da ya yi ragowa a rayuwarsa sannan kuma an yafe masa dukkanin abin da ya gabata a baya.
ـ وفي الفروع : احمد بن محمد، عن صفوان بن يحيى ، عن معاوية بن عمّار في دعاه الولد قال : إفض عليک دلواً من ماء زمزم ، ثم ادخل البيت فإذا قمت على باب البيت فخذ بحلقة الباب ، ثمّ قل : «اللّهمّ إنّ البيت بيتک والعبد عبدک وقد قلت : (وَمَنْ دَخَلَهُ كانَ آمِناً)[99] فآمني من عذابک وأجرني من
سخطک » ثمّ ادخل البيت فصلّ على الرُّخامة الحمراء ركعتين ، ثم قم إلى الاُسطوانة الّتي بحذاء الحَجَر وألصق بها صدرک ، ثم قال : «يا واحد يا أحد يا ماجد يا قريب يا بعيد يا عزيز يا حكيم لا تذرني فرداً وأنت خير الوارثين هب لي من لدنک ذريّة طيبّة إنّک سميع الدُّعاء» ثم دِر بالاُسطوانة فألصق بها ظهرک وبطنک وتدعو بهذا الدُّعاء فإن يردالله شيئاً كان [100].
26- ya zo cikin furu'ul kafi daga ahmad ibn Muhammad daga sufwau ibn yaaya daga mu'awiya ibn ammar cikin addu'ar xa: ka kwarra guga xaya daga ruwan zamzam a kanka, sannan ka shiga xakin ka'aba idan ka tsaya bakin qofa ka riqi hannun qofar sai kace: Allah shi wannan xaki xakinka ne kuma bawa bawanka ne, haqiqa kace: (duk wanda ya shige shi ya kasance amintacce) to ka amintar dani daga azabarka ka ceceni daga fushinka, sannan ka shiga xakain kayi sallah raka'a biyu a kan jar marmara, sannan ka tashi ya zuwa ga roller da take sahun dytsen hajarul aswad ka liqa da jingina qrjinka cikinta, sannan ya ce: ya xaya ya ma'abocin girma ya makunsaci ya manesanci ya maxaukaki ya mai hikima ka da ka barni nai xaya kai ne mafi alherin masu gado ka bani tsaftatacciyar zuriya daga wurinka lallai kai mai jin addu'a ne. sannan ka juya baya daga roller ka jingina bayanka jikinta da cikinka sai ka karanta wannan addu'ar,iadan Allah yaso faruwar wani abu sai ya faru.
وفي التهذيب : أحمد بن محمد، عن اسماعيل بن همام ، قال : قال ابوالحسن 7: دخل النبي 6 الكعبة فصلى في زواياها الأربع في كل زاوية ركعتين[101] .
27- ya zo cikin tahzib daga ahmad ibn Muhammad daga isma'il ibn hammam ya ce: abu Hassan(as) ya ce: annabi(s.a.w) ya shiga xakin ka'aba sai ya yi sallah raka'a biyu a dukkanin zawiyoyinta guda huxu
() 28 ـ وفي التهذيب : يعقوب ، عن ابن ابي عمير، عن هشام بن الحكم ، عن أبي عبدالله 7، قال : ما دخل رسول الله 6 الكعبة إلّا مرّة وبسط فيها ثوبه تحت قدميه وخلع نعليه [102].
28 yazo cikin tahzib daga yaqubu daga ibn abi umairu daga hisham ibn hakam daga baban Abdullah(as) manzon Allah(s.a.w) bai taba shiga xakin ka'aba ba sais au xaya ya shimfixa tufafinsa cikinta qarqashin qafafuwansa yak wabe takalmansa.
() 29 ـ وفي التهذيب : الحسين بن سعيد، عن صفوان ، عن المجاهد، عن ذريح ، قال : سمعت أباعبدالله 7 في الكعبة وهو ساجد وهو يقول : «لا يرد غضبک إلّا حلمک ولا يجير من عذابک إلّا رحمتک ولا نجاء منک إلّا بالتضرع إليک فهب لي يا إلهي فرجاً بالقدرة التي بها تحتي أموات العباد وبها تنشر البلاد، ولا تهلكني يا إلهي غماً حتى تستجيب لي دعائي وتعرّفني الاجابة ، اللهم ارزقني العافية إلى منتهى أجلي ، ولا تشمت بي عدوي ولا تمكنه من عنقي ، من ذا الذي يرفعني أن وضعتني ، ومن ذا الذي يضعني إن رفعتني ، وإن أهلكتني فمن ذا الذي يعرض لک في عبدک أو يسألک عن أمرک ، فقد علمت يا إلهي إنه ليس في حكمک ظلم ولا في نقمتک عجلة ، وإنما يعجل من يخالف الفوت ويحتاج إلى الظلم الضعيف وقد تعاليت يا إلهي عن ذلک ، إلهي فلا تجعلني للبلاء غرضاً ولا لنقتمک نصباً ومهّلني ونفسي وأقلني عثرتي ولا تردّ يدي في نجري ولا تتبعني ببلاء على أثر بلاء فقدترى ضعفي وتضرعي إليک ووحشتي من الناس وأنسي بک ، أعوذ بک اليوم فأعذني ، واستجير بک فأجرني ، واستعين بک على الضراء فأعني ، وأستنصرک فأنصرني ، وأتوكل عليک فاكفني ، وأؤمن بک فآمني ، واستهديک فاهدني ، وأسترحمک فأرحمني ، وأستغفرک مما تعلم فاغفر لي ، وأسترزقک من فضلک الواسع فارزقني ، ولا حول ولا قوة إلّا بالله العلي العظيم [103] .
29- ya zo cikin tahzib daga husaini ibn sa'idu daga sufwanu daga mjahid daga zuraihu ya ce: naji baban Abdullah(as) cikin ka'aba yana halin sujjada yana cewa : ( babu abin da ke komar da fushinka face haqurinka babu mai tsura daga zabarka face da rahamarka babu mai tsira daga gareka face da qasqantar da kai gareka ka bani yayewa ya ubangiji abin bautana da iko wadda da ita kake raya matattu da ita kake yaxa garuruwa, ka da ka halaka ni domin baqin ciki ya abin bautata har sai ka amsa mini addu'ata, ka nuna mini ams.a.wa, Allah ka azurta ni da lafiya har qarshen rayuwata, ka da ka bari maqiyana su yi mini dariya ka da ka basu dama a kaina, wanene zai iya xaukakani idan ka qasqantar dani, wanene zai iya qasqantar dani idan ka xaukakani , idan ka halar dani wanene zai sai bijiro maka cikin sha'anin bawanka ko ya tambaye kan lamarinka, haqiqa na san cewa babu zalunci cikin hukuncinka babu gaggwa cikin azabarka, kaxai wanda ke tsoron faucewa da subucewa ke gaggawa kuma rarrauna ke talautuwa da aikata zalunci haqiqa ka xaukaka ya abin bautata daga haka, ya bain bautata ka da ka sanyani karan bara ga bala'i, haka ka da ka sanya masauki azabarka ka jinkirta mini da rain aka zobaitar dani tubatubaina, ka da ka mayar da hannuwana ga wuyana ka da ka bibiyeni da bala'I kan bala'I haqiqa kana ganin raunina da qasqantata gareka da kaxaita daga mutane da nutsuwata da kai. Ina neman tsari da kai yau ka tsareni. Ina tsratarwarka ka tseratar dani, ina neman taimakonka kan duk wata mai cutarwa ka taimakeni, ina neman nasararka ka bani nasara, ina dogaro da kai ka isar mini, ina neman aminci daga gareka ka amintar dani, ian neman shiriyarka ka shiryar dani, ina neman rahamarka ka rahamceni, ina neman gafararka kai mini gafara, ina neman arziqinka ka azurtani, babu tsimi babu dabara face da Allah maxaukaki mai girma.
(فِيهِ آيَاتٌ بَيِّنَاتٌ مَقَامُ إِبْرَاهِيمَ.( [104]
Cikinsa akwai ayoyi mabayyana muqamu Ibrahim.
1 muqamu Ibrahim shi ne dutsen da ibrahim ya tsaya kansa domin ginin xakin ka'aba, haka domin ya yi shela da yekuwa ckin mutane ga ibadar hajji, saboda tsananin qararsa da xagawar sautinsa an gano cewa akwai alamar kufanqafafuwansa a kan dutsen, kamar yadda Allah ya tausasa baqin qarfe ga anabi dauda(as).
2 ibrahim ya tsaya kansa lokaci da matar xansa isma'il ta nemi da ta wanke masa qafafuwansa, lale shi Ibrahim (as) ya yiwa matarsa saratu alqawali ba zai sauka qasa daga kan taguwarsa ba sai kufan qafafuwansa ya bayyana kansa.
3 muqamu ya kasance a hagun xakin ka'aba:
ـ. عن الامام الصادق 7: مقام محمّد عن يمين عرش ربّنا عزّوجلّ ، ومقام إبراهيم عن شمال عرشه .
An karbo daga imam sadiq(as) muqamu muhammadu yana daga daman al'arshi, muqamu Ibrahim yana daga hagunnta.
4 muqamu Ibrahim a wannan zamani ya nesanta daga matsugunin xakin ka'aba da nisa mitatoci sha'uku 13 da abin da ke tsakaninsa da tsakanin ka'aba bisa abin da yafi shahara tsakanin malaman fiquhun shi'a, sai dai lokacin turmutsitsi da cinkoso da larura a bisa sabanin malamai.
عن الامام الباقر 7: كان موضع المقام الذي وضعه إبراهيم عند جوار البيت فلم يزل هناک حتّى حوّله عمر بن الخطّاب عن محلّه .
Daga imam baqir(as) muqamu ibrahim ya kasance a wajen da Ibrahim ajiye ya yin gifta xaki bai gushe ba a wannan waje har umar ibn kaxxab ya canja masa waje daga wajensa na asali.
5 wajibi ne sallar da ake raka'a biyu ta xawafi ta askance bayan muqamu Ibrahim, amma xawafin mustahabbi sallarsa ya halasta ayi a kowane mahalli daga cikin masallcin harami.
6 dutsen ibrahimiyya cikin jakar zinariya, an rubuta( kuma tsaresu baya nauyayarsa shi ne maxaukaki mai girma) (cikinsa akwai ayoyi bayyanannu muqamu Ibrahim)kan zinariyar da aka kewaye dutsen da ita. Daga cikin ayarsa shi ne ya wanzu har wannan zamani da muke ciki da sannu zai cigaba da wanzuwa, lallai an kareshi daga bacewa ko sacewa da dai makamantan haka.
عن الامام الباقر 7: إن بين الركن والمقام لمشحون من قبور الأنبياء ـ ويسمّى بالحطيم ـ.
7 daga imam baqir(as) lallai tsakanin rukuni da muqamu Ibrahim cike yake da kabaurburan annabawa, ana kiransa da haximu
() 8 ـ في العلل : أبي ؛ قال : حدثنا سعد بن عبدالله، قال : حدّثنا أحمد : وعلي ابنا الحسن بن علي بن فضال ، عن عمرو بن سعيد المدائني ، عن موسى بن قيس بن أخي عمار بن موسى الساباطي ، عن مصدق بن صدقة ، عن عمار بن موسى ، عن أبي عبدالله 7 أو عن عمار، عن سليمان بن خالد، عن أبي عبدالله7 قال : لما أوحى الله تعالى إلى ابراهيم 7 ان اذن في الناس بالحج اخذ الحجر الذي فيه اثر قدميه وهو المقام فوضعه بحذاء البيت لاصقا بالبيت بحيال الموضع الذي هو فيه اليوم ، ثم قام عليه فنادى بأعلى صوته بما أمره الله تعالى به فلما تكلّم بالكلام لم يحتمله الحجر فغرقت رجلاء فيه فقلع ابراهيم 7 رجليه من الحجر قلعاً فلما كثر الناس وصاروا إلى الشرو البلاء ازدحموا عليه فرأوا ان يضعوه في هذا الموضع الذي هو فيه اليوم ليخلو المطاف ، لمن يطوف بالبيت ، فلما بعث الله تعالى محمداً 6 ردّه إلى الموضع الذي وضعه فيه ابراهيم 7 فما زال فيه حتى قبض رسول الله 6 وفي زمن ابي بكر وأول ولاية عمر، ثم قال عمر: قد ازدحم الناس على هذا المقام فأيّكم يعرف موضعه في الجاهلية ؟ فقال له رجل ، انا اخذت قدره بقدر قال : والقدر عندک ؟ قال : نعم ، قال : فأتِ به فجاء به فأمر بالمقام فحمل وردّه إلى الموضع الذي هو فيه الساعة . [105]
8 ya zo cikin ilalu : na babana(rh) ya ce: sa'adu ibn Abdullah ya bamu labari , ya ce: ahmad ya bamu labari: da aliyu `ya`yan Hassan ibn aliyu faddal daga umar ibn sa'id almada'ini daga musa ibn qaisu xan xan'uwan ammar ibn musa sabaxi, daga musaddaq ibn sadaqatu daga ammar ibn musa daga baban Abdullah(as) kokuma daga ammar daga sulaimanu ibnkhalid daga baban Abdullah(as) ya ce: lokacin da Allah maxaukaki ya yi wahayi ga Ibrahim(as) da ya yi shela cikin mutnae da ibadar hajji sai Ibrahim ya kama dutse wanda cikinsa akwai kufan sahun qafafuwansa shi ne muqamu sai ya sanya kusa da xakin ka'aba ya na manne da xakin a wajen da yake a wannan zamani sannan ya tsaya a kansa sai yay i shela da abin da Allah maxaukaki ya umarce shi da shi da mafi qara da xagawar sautinsa, ya yin da ya yi Magana sai dutsen ya kasa xaukar abin da ya faxa sai dutsen ya nutse da qafafuwan Ibrahim sai Ibrahim ya tsamo qafafuwansa daga cikin dutsen tsamowa ya yinda mutane suka taru suka yawaita suka kasance zuwa ga sharri da bala'I sai suka cunkoso da turmutsitsi a kansa, sai suka ga cewa ya fi dacewa su xauke shi su sanya a wannan waje da yake a yanzu domin wajen xawafi ya samu ga wanda zai xawafi.. lokacin da Allah ya aiko da muhammadu(s.a.w) sai ya mayar da shi wajen da Ibrahim(as) ya ajiye shit un farko, bai gushe ba a wannan har zuwa wafatin manzon Allah(s.a.w) haka zamanin mulkin abubakar da farko farkon mulkin umar , lokacinda mutane suka yi cunkoso suka cika maqil da turmutsitsi sai umar ya ce: wanene ya san mahalllin wannan dutse a lokacin jahiliya? Sai wani mutum ya ce masa ni na auna awonsa, sai umar ya ce masa awon yana wajenka, sai mutumin ya ce eh, saiumar ya ce masa jeka ka zo da shi, sai ya zo da shi sai ya yi umarni da xauke muqamu sai ya xauke shi ya ajiye a inda yake yanzu.
1 alhaximu yana tsakanin dutsen hajarul aswad da muqamu Ibrahim(as) an kara shi wannan suna na haximu(mar rugujewa) saboda mutane suna tattake junansu lokaci xawafi da cunkoso, saboda zunubai suna ragargajewa.
عن الامام الباقر 7: إنّ أفضل البقاع ما بين الركن الاسود والمقام وباب الكعبة ، وذلک حطيم إسماعيل ، ووالله لو انّ عبداً صفّ قدميه في ذلک المكان وقام الليل مصلّياً حتّى يجيئه النهار وصام النهار حتّى يجيئه الليل ، ولم يعرف حقّنا وحرمتنا أهل البيت لم يقبل الله منه شيئاً أبداً[106] .
2 Daga imam baqir(as) lallai mafi falalar bigire shi ne tsakanin rukunul aswad da muqam da qofar xakin ka'aba, da wancn haximu isma'il, wallahi da ace bawa zai daidaita sahun qafafuwansa a wancan wuri ya tsaya dare yana sallah har gari yaw aye yay i azumi wayewar gari har wani daren ya qara riskarsa, amma kuma ace bai san haqqinumu ba da alfarmarmu mu iyalan annabi(as) allah ba zai karbi komai daga gareshi ba har abada.
3 lallai nan ne mahallin saukar jibrilu lokacin bayyanar imam mahadi(as) shi ne farkon wanda zai fara yi masa mubaya'a[107]
4 a da can haximu shi ne bangon baka daura da dutsen isma'il,
عن الامام الصادق 7: إنّكم تسمّونه الحطيم ، وإنّما كان لغنم إسماعيل وإنّما دفن فيه اُمّه ، وكره أن يوطأ قبرها فحجر عليه ، وفيه قبور الأنبياء[108] .
An karbo daga imam sadiq(as) lallai ku kuna kiransa da sunan haximu, kaxai dai ya kasance daga ganimar isma'il kaxai dai an binne mahaifiyarsa cikinsa. Ya kyamaci a dinga takawa sai ya sanya dutse kai, cikinsa akwai qaburburan annabawa.
() 5 ـ كان إبراهيم 7 يحطم الزرع لأغنامه في ذلک المكان .
5- Ibrahim ya kasance yana kakkarya shukar dabbobinsa a wannan waje.[109]
6 – larabawa sun kasance a zamanin jahiliya suna sanya tufafinsu a wannan waje lokacin xawafi domin ya kasance ragaraga.[110]
() 7 ـ عن أبي عبدالله الصادق 7 قال : لمّا كان آدم بالبيت وإنتهى إلى الملتزم قال جبرئيل 7: يا آدم أقرّ لربّک بذنوبک في هذا المكان ، قال : فوقف آدم 7 فقال : يا رب إنّ لكلّ عامل أجراً، قد عملت فما أجري ؟ فأوحى الله عزّوجلّ إليه يا آدم قد غفرت ذنبک ، قال : يا ربّ ولولدي أو لذرّيتي ؟ فأوحى الله عزّوجلّ : يا آدم من جاء من ذرّيتک إلى هذا المكان وأقرّ بذنوبه وتاب كما تبت ثمّ إستغفر غفرت له . [111]
7 Daga baban Abdullah sadiq(as) ya ce: adamu ya kasance a xakin ka'aba har ya kai ga abin lazimta sai jibrilu ya ce; ya adamu kayi iqirari zunubanka ga ubangijinka a wannan waje, ya ce: sai adamu tsaya ya ce: ya ubangijina lale dukkain mai aiki yaa da ladan aikinsa, lallai ni nayi aiki meye ladana? Sai Allah ya yi wahayi gareshi ya ce ya adamu an yafe maka zunubanka, ya ce: ya ubangiji ga xana da zurayata ? sai Allah mai girma da xaukaka ya yi wahayi ya damu duk wanda ya zo wanan waje daga zuriyarka ya yi iqirarin zunubansa ya tuba kamar yadda ka tuba ya nemi gafarata to na gafarta masa.
() 8 ـ عن أبي عبدالله 7 قال : سألته عن الملتزم لأيّ شيء يُلتزم ؟ وأي شيء يذكر فيه ؟ فقال : عنده نهر من الجنّة تلقى فيه أعمال العباد كل خميس[112] .
8 adaga baban Abdullah(as) ya ce: na tambayeshi gamaeda wanda ake lazimta me yasa akec lazimtarsa? Me akecambata cikinsa? Sai ya ce: wajensa akwai qorama dahga aljanna da take wurga ayyuaka bayi cikinsa dukkanin ranar alhamis.
1- Kalmar hijr hijru da wasalin qasa ga harafin ha'aun mara xigo yana da ma'anar xora duwasu wasu kan wasu har soma zama xaki shingagge, hijru isma'il nan wajen da mahallin da aka binne mahaifiyarsa hajara, ya kasance yana kyamar yaga ana tattaka kabarinta sai ya katange shi.[113]
Hairmarsa da gidansa da ya kasance yana rayuwa cikinsa shi da matarsa da babarsa.
2 – kabarin hajara da babarsa da `ya`yansa- da annabawa saba'in an shigar da shi cikin xawafi min girmama garesu.
3 kabarin shubbar da shubairu daga `ya`yan annabi haruna wazirin annabi musa abokin hirar Allah.
4 mafi falalar bigire shi ne masallacin harami domin sallah imamai tsarkaka sunyi sallah cikinsa.
5 indararon zinariya wanda akafi sani da indararon rahama yana kwararar daruwa lokacin saukar ruwan sama.
6 mustahabbi ne yin ihramin tamattu'I cikinsa.
7 musatabbi ne yin sallolin farilla cikinsa, lallai dukkanin sallah tana da matsayin karbabbiyar hajji kamarb yadda hakan ya zo cikin hadsi daga imam rida(as)
1 mustajar yana kusa da ruul yamani yana fuskantar qofar ka'aba daga xaya gefan.
2 an kirashi da wannan suna sakamakon neman tsiran da mutane suke da Allah daga zunubansa.
3 a cikinsa mahallin da aka haifi sarkin muminai ali(as) yake cikin xakin ka'aba. Sannan har zuwa yanzu kuafaifayi da alamomi da ke nuni da haka basu gushe ba.
وفي الفروع : عدّة من أصحابنا، عن أحمد بن محمّد، عن الحسين بن سعيد، عن النضر بن سويد، عن عبدالله بن سنان ، عن أبي عبدالله 7 قال : يستحب أن تقول بين الركن والحجر: «اللهمّ آتنا في الدُّنيا حسنة وفي الآخرة حسنة وقنا عذاب النار» وقال : إنّ ملكاً موكّلاً يقول : آمين . [114]
4 Ya zo cikin furu'ul kafi daga wasu adadi daga sahabbanmu daga ahmad ibn Muhammad daga husaini ibn sa'id daga nadaru ibn suawaidu daga Abdullah ibn sinanu daga baban Abdullah(as) ya ce: mustahabbi ne tsakanin rukuni da haima ka faxi : ( Allah ka bamu kyakkyawa a duniya ka bamu kyakkyawa a lahira ka cece mu daga azabar wuta) mala'ikan da aka wakilta zai ce amin.
وفي الفروع : أحمد بن محمّد، عن محمّد بن يحيى ، عن غياث بن إبراهيم ، عن جعفر، عن أبيه 8 قال : كان رسول الله 6 لا يستلم إلّا الرّكن الأسود واليماني ، ثمّ يقبّلهما ويضع خدّه عليهما ورأيت أبي يفعله . [115]
5 yazo cikin furu'ul kafi daga ahmad ibn Muhammad daga Muhammad ibn yahaya daga giyasu ibn Ibrahim daga ja'afar daga babansa(as) ya ce: manzon Allah(s.a.w) ya kasance bai runguma face rukunul aswad da yamani sannan ya sumabcesu ya xora kuncinsa kansu, nag a babana yana aikata haka.
وفي الفروع : أحمد بن محمّد، عن البرقي ، رفعه ، عن زيد الشحّام أبي أسامة ، عن أبي عبدالله 7 قال : كنت أطوف مع أبي عبدالله 7 وكان إذا انتهى إلى الحَجَر مسحه بيده وقبّله وإذا انتهى إلى الرّكن اليماني التزمه فقلت : جعلت فداک تمسح الحَجَر بيدک وتلتزم اليماني ؟ فقال : قال رسول الله 6: ما أتيت الرّكن اليمانيُ إلّا وجدت جبرائيل قد سبقني إليه يلتزمه . [116]
6 Ya zo cikin furu'ul kafi daga ahmad ibn Muhammad daga baraqi ya yi rafa'in hadisin daga zaidul shahham abi usamatu daga baban Abdullah(as) ya ce: na kasance ina xawafi tare da baban Abdullah ya kasance idan ya tuqe mahallin dutsen hajarul aswad sai ya shafa shi da hannunsa ya sumbace shi, iadan kuma ya tuqe ga mahallin rukunul yamani sai ya lazimce shi ya rungumeshi, sai nace raina fansarka kana shafar hajarul aswad da hannunka kana lazimtar rukunul yamani? Sai ya ce: manzon Allah(s.a.w) ya ce: ban taba zuwa wajen rukunul yamani ba face na samu jibrilu ya gabaceni gareshi ya lazimceshi.
وفي الفروع : أحمد بن محمّد، عن الحسين بن عليّ، عن ربعيّ، عن العلاء بن المقعد قال : سمعت أباعبدالله 7 يقول : انّ الله عزوجلّ وكّل بالرّكن اليماني ملكاً هجيراً[117] يؤمن على دعائكم .
7 yazo cikin furu'ul kafi daga ahmad ibn Muhammad daga husaini ibn aliyu daga raba'I daga ula'I ibn miqdadau ya ce: naji baban Abdullah(as) yana cewa: lallai Allah mai girma da xaukaka ya wakilta wani mala'ika mai daraja kan rukunul yamani yana amintar da addu'o'inku.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن ابن أبي عمير، عن العلاء بن المقعد قال : سمعت أباعبدالله 7 يقول : إنّ ملكاً موكّلاً بالرّكن اليماني منذ خلق الله السماوات والأرضين ليس له هجير إلّا التأمين على دعائكم فلينظر عبد بما يدعو، فقلت له : ما الهجير؟ فقال : كلام من كلام العرب أي ليس له عمل . وفي رواية أخرى ليس له عمل غير ذلک[118] .
8 yazo cikin furu'ul kafi daga aliyuibn Ibrahim daga babansa daga ibn abi umairu daga ula'u ibn miqdadu ya ce: naji baban Abdullah(as) yana cewa lallai mala'ika da aka wakilata kan rukunul yamani tun lokacin da Allah ya halicci sammmai da qassai bai da wani aiki da yawuce aminytar da addu'o'inku saboda sai bawa ya dubi abin da zai roqa. Sai na tambaye shi menene ma'a'anar kalamr hajiru? Sai ya ce: zance ne daga zancen larabawa ma'ana bai da aiki. A wata riwayar kuma bai da wani aiki da yawuce haka.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن إبن أبي عمير، عن معاوية ]بن عمّار[، عن أبي عبدالله 7 قال : الرّكن اليماني باب من أبواب
الجنّة لم يغلقه الله منذ فتحه . [119]
9 Yazo cikin furu'ul kafi daga aliyu ib Ibrahim daga babansa daga ibn abi umairu daga mu'awiyatu ibn ammar daga baban Abdullah(as)ya ce: rukunul yamani qoface daga qofofin aljanna Allah bai taba rufeshi tun loakci da ya buxe shi.
10 A cikin wata riwayar qofarmu zuwa aljanna wadda daga gareta zamu shiga.
وفي الفروع : عدّة من أصحابنا، عن سهل بن زياد، عن الحسن بن عليّ بن النعمان ، عن إبراهيم بن سنان ، عن أبي مريم قال : كنت مع أبي جعفر 7 أطوف فكان لا يمرُّ في طواف من طوافه بالرُّكن اليماني إلّا إستلمه ، ثم يقول : «اللّهمّ تب عليّ حتى أتوب واعصمني حتى لا أعود» .[120]
11 yazo cikin furu'ul kafi daga wasuadadi daga sahabbanmu daga sahalu ibn zayad daga Hassan ibn aliyu ibn nu'umanu daga Ibrahim ibn sinanu daga abi Maryam ya ce: na kasance tare da baban jafar ina xawafi ya kasance bai giftawa ta gefan rukunl yamani face ya rumgumeshi, sannan ya ce: ya Allah ya karbi tubana har in tuba ka katangeni har ya zmanto b azan koma in qara aikata sabo ba.
عدة من أصحابنا عن سهل بن زياد، عن يعقوب بن يزيد، عن أبي الفرج السندي ، عن أبي عبدالله 7 قال : كنت أطوف معه بالبيت فقال : أيُّ هذا أعظم حرمة ؟ فقلت : جعلت فداک أنت أعلم بهذا منّي فأعاد عليّ فقلت له : داخل البيت ، فقال : الرُّكن اليماني على باب من أبواب الجنّة مفتوح لشيعة آل محمّد مسدود عن غيرهم ، وما من مؤمن يدعو بدعاء عنده إلّا صعد دعاؤه حتّى يلصق بالعرش ، ما بينه وبين الله حجاب . [121]
12 daga wasu adadi daga sahabbanmu daga sahalu ibn zayad daga yaqubu ibn yazid daga abi faraju sanadi daga baban abdullah9as) ya ce: na kasance inaxawafi tare da shi sai ya ce: me yafi wannan alfarma? Sai nace masa raina fansarka kai ne mafi sani daga gareni, sai ya qara maimaita abin da ya faxa, sai nace masa ckin xakin, sai ya ce: rukunul yamani kan qofar daga qofofin aljanna an buxe shi domin shi'ar iyalan manzon Allah(s.a.w) sannan kuma a toshe ga wasunsu, babu wani mumini da zai yi addu'a wajensa face addu'arsa ta haura ta manne da al'arshi, sannan kuma babu hijabi tsakaninsa da Allah.
وفي الفروع : عليّ بن إبراهيم ، عن أبيه ؛ ومحمّد بن اسماعيل ، عن الفضل بن شاذان ، عن ابن أبي عمير، عن حفص بن البختري ، عن أبي عبدالله7 قال : انّ في هذا الموضع يعني حين يجوز الرُّكن اليمانيّ ـ ملكاً اُعطي سماع أهل الأرض فمن صلّى على رسول الله 6 حين يبلغه أبلغه إيّاه . [122]
13 yazo cikin furu'ul kafi daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga muhammadu ibn isma'il daga fadalu ibn shazan daga ibn umairu daga hafsu ibn buktari daga baban Abdullah(as)ya ce: lallai cikin wannan wuri ma'ana rukunul yamani akwai wani mala'ika da aka bashi damar jin halittun da suke qasa duk wanda ya yi sati ga muhammadu(s.a.w) lokacin da yake isa gareshi zai isar masa da saltinsa.
() 14 ـ وفي الفروع : محمّد بن يحيى ، عمّن ذكره ، عن محمّد بن جعفر النوفلي ، عن ابراهيم بن عيسى ، عن أبيه ، عن أبي الحسن 7 أنّ رسول الله 6 طاف بالكعبة حتّى إذا بلغ الرُّكن اليماني رفع رأسه إلى الكعبة ، ثم قال : «الحمد لله الذي شرَّفک وعظّمک والحمد لله الذي بعثني نبيّاً وجعل عليّاً اماماً، اللّهمّ اهد له خيار خلقک وجنّبه شرار خلقک[123]
14 yazo cikin furu'ul kafi daga muhammadu ibn yahaya daga wanda ya ambace shi daga muhammadu ibn jafar naufali daga Ibrahim ibn isa daga babansa daga baban Hassan(as): lallai manzon Allah yay i xawafi ya kewaya ka'aba lokacin da yakai ga mahallin rukunul yamani sai ya xaga kansa zuwa ga xakin ka'aba sannan ya ce; godiya ta tabbata ga Allah wanda ya xaukakaka ya girmamaka godiya ta tabbata Allah wanda ya turoni annabi ya sanya aliyu imami, ya Allah ka shiryar masa zababbun halittuka ka nesanta shi daga mafi sharrin halittunka.
وفي العلل : حدثنا أبي 2، قال : حدثنا سعد بن عبدالله، قال : حدثنا محمّد بن عبدالجبار، قال : حدثنا جعفر بن محمد الكوفي ، عن رجل من أصحابنا رفعه ، عن أبي عبدالله 7 قال : لما انتهى رسول الله 6 إلى الركن الغربي فقال له الركن ؛ يا رسول الله ألست قعيداً من قواعد بيت ربک فما لي لا أستلم ؟ فدنا منه النبي 6 فقال له : اسكن عليک السلام غير مهجور[124] .
15 yazo ciki ilalu babana ya zantar damu sa'ada ibn Abdullah ya zantar damu ya ce; muhammadu ibn abdul jabbar ya zantar damu ya ce: jafar ib Muhammad kufi ya zantar damu daga wani mutum daga ckin sahabbanmu ya yi rafa'in riwayar daga baban Abdullah(as)ya ce: lokacin manzon Allah ya tuqe ga mahallin rukunul garbi sai rukunin ya ce masa: ya manzon Allah ashe kai ba harsashin bane daga harsashen xakin ka'aba me yasa ba zaka rungume nib a, sai manzon Allah(s.a.w) ya matso kusa da shi ya ce masa kwantar da hankalinka aminci ya tabbata gareka kai baa bin hijircewa bane.
وفي العيون : حدثنا أبي 2، قال : حدثنا محمّد بن يحيى العطار، عن محمّد بن احمد بن يحيى بن عمران الأشعري ، قال : حدثني ابوسعيد الآدمي ، عن أحمد بن موسى بن سعد، عن ابي الحسن الرضا 7 فرفع يديه ، ثم قال : «يا الله يا ولي العافية ويا خالق العافية ، ويا رازق العافيه والمنعم بالعافية والمنان بالعافية والمتفضل بالعافية عليّ وعلى جميع خلقک ، يا رحمن الدنيا والآخرة ورحيمهما صل على محمّد وآلمحمد وارزقنا العافية ودوام العافية وتمام العافية وشكر العافية في الدنيا والآخرة يا ارحم الراحمين[125] » .
16 Yazo cikin uyunu: baban ya zantar damu ya ce: muhammadu ibn yahaya axxar ya znatr damu daga muhammadu ibn ahmad ibn yahaya ibn imrana ala'ash'ari ya ce: abu sa'idu adami ya zantar damu daga ahmadd ibn musa ibn sa'ad dagababan Hassan rida (as) sai ya xaga hannayensa sanna ya ce: ( ya Allahu ya majibancin lafiya ya mai bada lafiya ya mahaliccin lafiya, ya mai azurtawa da lafiya ya mai ni'imtawa da lafiya ya mai tautayi ya mai falala da lafiya a kaina da kan dukkanin halittunka, mai rahamar duniya da lahira da jin qansu, kayi salati ga muhamammadu da iyalansa ka azurtamu da lafiya da dawwamar lafiya da ckair lafiya da yabawa kan lafiya duniya da lahira ya mafi rahamar masu rahama.
() 17 ـ وفي البحار: نقلاً عن كشف الغمة قبل : ان الحسن بن علي بن أبي طالب التزم الركن فقال : «الهي انعمت عليّ فلم تجدني شاكراً، وابتليتني فلم تجدني صابراً، فلا أنت سلبت النعمة بترک الشكر، ولا أنت أدمت الشدّة بترک الصبر، إلهي ما يكون من الكريم الاالكرم » .[126]
17 yazo cikin biharu anwar: an naqalto daga kasheful gumma: cewa ibn alyu ibn abi xalibi ya rugumi rukunul yamani ya ce: ( ya abin bautata akayi ni'ima kaina amma baka sameni iana yabawa ba, ka jarrabeni baka sameni mai haquri kan jarrbawa ba, kuma kai ka kwace ni'imarkaba saboda kin yabawa ta ba, kuma kai baka dawwamar da tsananini ba saboda rashin haqurina ba. ya abin bautata babu abin da ke gangarowa daga mai karamci face karamci.
وفي العلل : حدثنا محمد بن الحسن بن احمد بن الوليد 2، قال : حدثنا احمد بن ادريس ، عن محمد بن حسان ، عن الوليد بن ابان ، عن علي بن جعفر، عن محمد بن مسلم ، عن أبي عبدالله 7، قال : قال رسول الله 6 : طوفوا بالبيت واستلموا الركن فانه يمين الله في أرضه يصافح بها خلقه مصافحة العبد أو الدخيل ويشهد لمن استلمه بالموافاة . [127]
1 yazo cikin ilalu muhammadu ibn Hassan ibn ahmad ibn walidu ya zantar damuya ce: ahmad ibnidrisu ya zantar damu daga muhammadu ibn hassanu daga walidu ibnabbanu daga aliyu ibn jafar daga muhammadu ibn muslimu daga baban Abdullah(as) ya ce: manzon Allah(s.a.w)ya ce: ku kewaya ku sumbaci runul yamani lallai shi daman Allah ne cikin qasa yana gais.a.wa da halittunsa irin gais.a.wa da bawa lallai shi zai yi shaida ga wanda ya shafeshi ranar qiyama da cikawa.
وفي العلل : أخبرنا علي بن حاتم ، قال : حدثنا علي بن الحسين النحوي ، عن احمد بن محمد بن عيسى ، عن ابن فضال ، عن ثعلبة بن ميمون ؛ وغيره ، عن بريد بن معاوية العجلي ، قال : قلت لأبي عبدالله 7: كيف صار الناس يستلمون الحَجَر والركن اليماني ولا يستلمون الركنين الآخرين ؟ فقال : قد سألني عن ذلک عباد بن صهيب البصري فقلت له : لأن رسول الله 6 استلم هذين ولم يستلم هذين فإنما على الناس أن يفعلوا ما فعل رسول الله 6 وسأخبرک بغير ما أخبرت به عباداً إن الحَجَر الأسود والركن اليماني عن يمين العرش وإنّما أمر الله تبارک وتعالى أن يستلم ما عن يمينه عرشه ، قلت : فكيف صار مقام ابراهيم عن يساره؟ فقال: لأن ابراهيم 7 مقاماً في القيامة ولمحمد 9 مقاماً فمقام محمد عن يمين عرش ربنا عزوجل ، ومقام ابراهيم عن شمال عرشه ، فمقام ابراهيم في مقامه يوم القيامة ، وعرش ربنا مقبل غير مدبر . [128]
2 yazo cikin ilalu aliyu ibn hatimu ya bamu labari ya ce: aliyu ibn husaini annawahi daga ahmad ibn Muhammad ibn isa daga faddal daga sa'alabatu ibn maimunatu da waninsa daga buraidu ibn mu'awiyatu al'ajali, ya ce: na cewa baban Abdullah(as) ta yaya zamanto suke sumbatar dutsen hajarul aswad da rukunul yamani amma kuma bas a sumbatar ragowar rukunan ? sai ya ce: haqiqa suhaibu ibn ibaul albasaari yay i mini wannan tamabayar, sai nace masa saboda manzon Allah(s.a.w) ya sumabaci hajarul aswad da rukunl yamani bai kuma sumbaci ragowar ba, kaxai dai mutane suna kwaikwayar abin da manzon Allah(s.a.w) ya aikata da sannu zan baka labari sabanin wanda na baiwa suhaibu ibn ibadu albasari lallai hajarul aswad da rukunul yamani suna daman al'arshi, kaxai dai Allah yay i umarni da a sumbaci daman al'arshinsa, sai nace ta qaqa muqamu Ibrahim ya kasance daga hagunsa? Sai ya ce: saboda Ibrahim(as) yana da muqami a lahira muhammadu (s.a.w) yana da muqam a lahaira, muqamu muhammadu(s.a.w) yana daman al'arshi,muqamu Ibrahim(as) yana hagun al'arshi, saboda haka muqamu Ibrahim yan muqam xinsa ranarb qiyama, al'arshin ubnagijinmu yana fuskantowa ne baya bada baya.
وفي العلل : حدثنا أبي 2، قال : حدثنا سعد بن عبدالله، عن أيوب بن نوح ، عن صفوان بن يحيى ، عن معاوية بن عمار، عن أبي عبدالله 7، قال : بينا أنا في الطواف إذا رجل يقول ما بال هذين الركنين يمسحان ـ يعني الحَجَر والركن اليماني ـ وهذين لا يمسحان ؟ قال : فقلت : لأن رسول الله 6 كان يمسح هذين ولو يمسح هذين فلانتعرض لشيء لم يتعرض له رسول الله 9[129] .
3 yazo cikin ilalu: babana ya bamu labari ya ce: sa'adu ibn Abdullah daga ayyuba ibn nuhu daga sufwanu ibn yahaya daga mu'awiyatu ibn ammar daga baban Abdullah(as) ya ce: ya yin da ni nake cikin xawafi sai ga wani mutum yana cewa:me yasa waxannan ruknai guda biyu ake shafarsu ma'ana hajarul aswad da yamani , ama kuma waxannan ragowar biyun ba'a shafarsu? Sai ya ce: sai nace: saboda manzon Allah(s.a.w) ya kasance yana shafar waxannan biyun, da ace ya shafi waxannan ragowar saboda haka ka da ka zakkewa abin da manzo Allah(s.a.w) bai aikata ba.
ـ قال الامام الصادق 7: انه ـ الركن اليماني ـ بابنا الذي ندخل منه الجنّة .
4 imam sadiq(as) : lallai shi rukunul yamani qofar mune da muke shiga daga gareshi.
ـ وقال 7: إنّ فيه باباً من أبواب الجنّة لم يغلق منذ فتح ، وفيه نهر من الجنّة تلقى فيه أعمال العباد، وهذا هو الركن اليماني لا ركن الحجر[130] .
5 ya ce: lallai cikinsa akwai wata qofa daga qofofin aljanna ba a taba kulleta bat un daaka buxeta, cikinsa akwai qorama tana wurga ayyaukan bayi, wannan shi ne rukunul yamani ba rukunu hajarul aswad ba.
عن بريد العجلي قال : قلت لأبي عبدالله 7: كيف صار الناس يستلمون الحجر والركن اليماني ولا يستلمون الركنين الآخرين ؟
فقال : قد سألني عن ذلک عباد بن صهيب البصري ، فقلت له : لأن رسول الله 6 إستلم هذين ولم يستلم هذين ، فانّما على الناس أن يفعلوا ما فعل رسول الله 6، وسأخبرک بغير ما أخبرت به عبّاداً، إن الحجر الأسود والركن اليماني عن يمين العرش ، وإنّما أمر الله تبارک وتعالى أن يستلم ما عن يمين عرشه ، قلت : فكيف صار مقام إبراهيم 7 عن يساره ؟ فقال : لأنّ لابراهيم 7 مقاماً في القيامة ومحمّد 6 مقاماً فمقام محمّد 6 عن يمين عرش ربّنا عزّوجلّ ، ومقام ابراهيم 7 عن شمال عرشه ، فمقام إبراهيم 7 في مقامه يوم القيامة ، وعرش ربّنا مقبل غير مدبر.
Cikin wannan hadisi mai daraja akwai sirrika da hikimomi da tarbiya da ta'alimi.
Daga cikinsu: lallai jawabin tambayoyin ya banbata bisa banbatar mutanen, wani lokaci jawabi ya kasance ba'ame mai gamewa ga kowa ga kowa kamar yadda ya kasance ga suhaibu ibn ibadu al;basai, wani lokacin kuma ya zama kebantacce ga kebantattu da sahabbai kamar yadda ya kasance ga buraidu ajili.
Wani lokaicn kuma jawabin ya kasance cikin fiqihul asgar da bin sunnar manzo Allah(s.a.w) wani lokaci kuma ya kasance da fiqihul akbar da dangantakarsa da Allah da ranar qiyama.
Daga ckinsu: falalar da fifitar dama kan hagu da banbantar muqaman annabawa, lale mafi falalar manzanni da annnabawa cikin matsayi da muqami shi ne cika makin annabawa muhammadu Mustafa(s.a.w).
Daga cikinsu al'arshin ismi da musamma'I, lallai shi mai fsukantaowa ba mai bada bay aba.
Daga cikinsu: shafar rukunai biyu daga daman al'arshi wanna a haqiqa ya nuni da gais.a.wa da Allah, dukanin hannuwansa biyu dama ne babu hagu, kamar yadda hadisi ya tabbatar da hakan, saboda shi daman a nuni da ishara zuwa damaita da albarka da rahama mayalwaciya.
Daga ckinsu: daidaita tsakanini duniya da lahira, yayain da muqamu Ibrahim ya kasance a hagun al'arshi sai ya zamanto muqaminsa a duniya daga hagunn xakin ka'aba yake.
() 1 ـ وفي الفروع : عليّ بن ابراهيم ، عن أبيه ، عن ابن أبي عمير؛ ومحمّد بن إسماعيل ، عن الفضل بن شاذان ، عن ابن أبي عمير؛ وصفوان بن يحيى ، عن معاوية بن عمّار قال : قال أبوعبدالله 7: إذا فرغت من طوافک وبلغت مؤخّر الكعبة ـ وهو بحذاء المستجار[131] دون الرّكن اليماني بقليل ـ فابسط يديک على
البيت وألصق بطنک وخدّک بالبيت وقل : «اللّهمّ البيت بيتک والعبد عبدک وهذا مكان العائذ بک من النار» ثم أقرّ لرّبک عملت فإنّه ليس من عبد مؤمن يقرُّ لربّه بذنوبه في هذا المكان إلّا غفر الله له إن شاء الله وتقول : «اللهم من قبلک الرّوح والفرج والعافية ، اللّهمّ إنّ عملي ضعيف فضاعفه واغفر لي ما اطلعت عليه منّي وخفي على خلقک » ثمّ تستجير بالله من النار وتخيّر لنفسک من الدُّعاء، ثمّ إستلم الرُّكن اليماني ، ثمَّ إئت الحَجَر الأسود[132] .
1 yazo cikin furu'ul kafi; daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga abi umairu daga muhammadu ibn isma'il daga fadlu ibn shazanu daga abi umairu daga sufwanu ibn yahaya daga mu'awiyatu ibnammarya ce: baban Abdullah(as) ya ce: idan ka kagama xawafinka ka sia ga bayan ka'aba shi yana kusa da mustajar kafin akai ga rukunul yamani to ka shimfixa hannunka kanxakin ka'aba ka manna cikinka da kuncinka jikin xakin sai kace( ya Allah xaki dai xakinka ne kuma bawa bawanka ne wanna wurie na mai nema tsarinka daga wuta,) sanan ka yiwa ubangijinka iqirarin abin da kaaikata, lallai babubwanibawa mumini da zai yi iqirari ya bayyanawa ubangijinsa abin da ya aikata face ya yi masa gafara da yardarm Allah, sai kace: ( Allah daga gareka hutu da buxi da lafiya suke, Allah lallai aikina nada matuqar rauni ina roqonka ka ninninka shi kai mini gafara da abin daka tsinkaya kansa daga gareni wanda ya buya wurin halittunka) sannan sai ka nemi tsarin Allah daga wuta ka zabarwa kanka addu'a, sai ka shafi rukunul yamani, sannan ka jewa hajarul aswad.
() 2 ـ وفي فقه الرضا: تطوف أسبوعاً وتقارب بين خطاک وتستلم الحَجَر
في كلّ شرط فإن لم تقدر عليه فأشر إليه بيدک ، وقل عند باب البيت : «سائلک مسكينک ببابک عبيدک بفنائک فقيرک نزل بساحتک تفضّل عليه بجنّتک » فاذا بلغت مقابل الميزاب فقل : «اللّهمّ أعتق رقبتي من النار وَادْرَأ عنّي شرّ فسقة العرب والعجم وأظلّني تحت ظلّ عرشک واصرف عني شرّ كل ذي شرّ وشرّ فسقة الجنّ والأنس » وتقول في طوافک : «اللّهمّ إنّي أسألک باسمک الذي يمشي به على الماء كما يمشي على جدد الأرض ، وباسمک المكنون المخزون عندک ، وباسمک الأعظم الأعظم الذي إذا دعيت به أجبت واذا سئلت به أعطيت أن تصلي على محمّد وآل محمّد أن تغفر لي وترحمني وتقبّل منّي كما تقبّلت من إبراهيم خليک 7 وموسى كليمک 7 وعيسى روحک 7 ومحمد حبيبک 6» فاذا بلغت الركن اليماني فاستلمه فانّ فيه باباً من أبواب الجنّة لم يغلق منذ فتح ، وتشير منه إلى زاوية المسجد مقابل هذا الركن وتقول : «أصلي عليک يا رسول الله» وتقول بين الركن اليماني وبين ركن الحَجَر الأسود: «ربّنا آتنا في الدُّنيا حسنة وفي الآخرة حسنة وقنا عذاب النار» فاذا كنت في الشوط السابع فقف عند المستجار وتعلّق بأستار الكعبة وادع الله كثيراً وألحّ عيله وسل حوائج الدُّنيا والآخرة فإنّه قريب مجيب . [133]
2 yazo cikin fiqihun rida: za kayi xawafi keawaye bakwai ka kusantr da tsakanaknin tattakinka ka shafa hajarul aswad cikinkowane kewaye idan baka sam damar hakan to kayi ishara da hannunka zuwa gareshi da, dadai qofar ka faxiL almajirinka talakanka a bakin qofarka, bawanka a farfajiyarka talakankaka ya sauka filinka kayi falala kansa da aljannarka) idan ka isa fuskar indararon rahama sai kace: ( Allah lallai ni ina roqonka ka `yantar da wuyana daga wuta ka kare ni daga sharrin fasiqai daga sharrin dukkanin mai sharri mutum da aljanni balarabe da ba'ajame ka sanyani cikin qarqashin inuwar al'arshinka ka kautar da dukkanin sharrinma'abocin sharri da sharrin fasiqai mutane da aljannu) cikin xawafinka kace: ( Allah lallai ni ina roqonka da sunanka wanda ake tafiya da shi kan ruwa kamar yanda ake tafiyar kan tsandaurin qasa, da sunan kiyayye taskatacce wajenka, da sunanka mafi girma wanda idan ka kira da shi kake ams.a.wa iadan aka roqeka da shi saika bayar kayi salati ga muhammadu da iyalannsa ka yafe mini kaimni gafara ka yi mini rahama ka karba daga gareni kamar yadda ka karba daga Ibrahim badaxinka(as) da musa(as) abokin hirarka da isa ruhinka(as) da muhammadu(s.a.w) massoyinka) idan ka kai ga rukunul yamani sai ka sumbace shi lallai cikinsa akwai wata qofa daga qofofin aljanna ba a taba kulle ta bat un da aka buxeta, sai kayi ishara daga gareshi zuwa zawiyya masallaci dake kishiyantar rukunul yamani saikaceL ina salati gareka ya manzon Allah) tsakanin rukunul yamani da hajarul aswad k ace: ( ya ubangijinmu ka bamu kyakkyawa a duniya kyakkyawa a lahira ka tseratar damu daga azabar wuta) idan ka kasance cikin kewaye na qarshe kewaye na bakwai sai ka tsaya wurin mustajar ka ratayu da labulen ka'aba kayi addu'a ka roqi Allah da yaw aka tamabayi buqatunka na duniya da lahira lallai shi makusanci mai ams.a.wa.
() 3 ـ وفي البحار: نقلاً عن الهداية ، المواطن التي ليس فيها دعاء موقّت : الصّلاة على الجنازة والقنوت ، والمستجار، والصّفا، والمروة ، والوقوف بعرفات ، وركعتي الطواف . [134]
3 yazo cikin biharul anwar an naqalto daga hidaya, wuraren da ckinsu addu'a bata da lokaci: sallah gawa da qunutu, mustajar, safa, marwa, tsayuwar Arafat, raka'a biyu ta xawafi.
1 haqiqa ruwan rijiyar zamzam ya bubbugo sakamakon shuri da zungurin da isma'il(as) yay i lokacin da yake qanqanin yaro lokacin da mahaifiyarsa hajara ta ke kaikawo tsakanin safa da marwa domin nenman ruwan sha, domin tayi maganin qishurwar xanta, sa'ailin da ta hango turbaya ta tattaru daura da isma'il(as) tana faxin zamzam, sa aka wayi gari ana kiransa da zamzam.
2 mustahabbi ne shan ruwan zamzam da kwarara shi kan qirji da gadon baya bayan kammala xawafi da sallarsa gabanin fara sa'ayi tsakanin safa da marwa da yin kebantacciyar addu'a.
(اللّهمّ انّي أسألک علماً نافعاً ورزقاً واسعاً وشفاءً من كلّ داء وسقم[135] .(
Ya Allah lallai ni ina roqonka ilimi mai amfani da arziqi mayalwaci da waraka daga dukkanin ciwo.
3 zamzam ya nuni da ishara ya zuwa mabubbugar ilimi da tsoron Allah da soyayyay da qauna da rahama da fata da Allah, lallai hajara duk dacewa tayi sassarfa tsakanin dutsen safa da marwa sau bakwai sai daicewa bata xebe tsammani da yanke fata ba, da haka nema Allah ya buxeta mata wata qofar daban sai ruwa ya bubbugo sakamakon shurin da ismail(as) ya yiwa qasa domin ya kasance daga ayoyinsa da suke nuni ya zuwa ga ni'imarsa da tausayinsa da luxufinsa.
4 lallai zamzam yana daga cikin ayyoyin Allah cikin msallacin harami, lallai shi bayan shuxewa dubban shekaru bai gushe ba ruwa yana bubbuga ba daga wannan rijiya ta zamzam tare da da kasantuwar qasar makka qasa marmaru babu dusar qanqara kanta kuma wasu rijiyoyin daban basu maqotanci rijiyar zamzam balle su tunkuxo mata ruwa.
ـ عن رسول الله 6 ينفع لكلّ ما ينويه الانسان ، وإنّه أفضل ماء على الأرض .
5 An karbo daga manzon Allah(s.a.w) ya ce: ruwan zamzam yana amfanarwa ga dukkanin abin da mutum ya yi niyya, lallai shi ne mafi falalar ruwa a ban qasa.
() 6 ـ ماء زمزم لِما شرب له : فمن شربه لمرض شفاه الله، ولجوع أشبعه الله، أو لحاجة قضاها الله . [136]
6 ruwan zamzam na afanarwa ga abin da aka shahsi domin shi: idan aka shashi domin warkewa daga cuta Allah zai bada waraka, idan aka shashi domin maganin yunwa Allah zai qosar, idan aka shashi domin neman biyan buqata Allah zai biya buqata.
لشدّة شوق النبي 9 بماء زمزم، كان في المدينة يستهديه أي يطلبه من الوافدين من مكّة المكرّمة بعنوان هدية [137]، وكذلک فعل الإمام الصادق 7.
7 saboda tsananin shauqin annabi(s.a.w) ga ruwan zamzam ya kasance ya na neman kyautarsa daga masu zuwa daga makka da taken hadaya, haka ma imam sadiq(as) ya kasance yana aikatawa.
8 rijiyar zamzam ta shahara da kasantuwarta abar yin rowa da katangewa daga fuskanin qabilar kuza'atu a zamanin da, daga baya abdul muxallib ya dawo da ita sai sunanta ya shahara da sunan ramin abdul muxallib.
ـ وفي الفقيه : روي انه من روي من ماء زمزم أحدث له به شفاء وصرف عنه داء[138] .
9 yazo cikin littafin alfaqihu: an rawaito cewa duk wanda ya sha daga ruwan zamzam zai warkar da shi zai kareshi daga ciwo
وفي الفقيه : كان رسول الله 6 يستهدي ماء زمزم وهو بالمدينة .[139]
10 Yazo cikin alfaqihu: manzon Allah(s.a.w) ya kasance yana neman a bashi kyuatar ruwan zamzam alhalin shi yana madina.
وفي الدعائم : عن الحسن والحسين 8 انهما طافا بعد العصر وشربا من زمزم قائمين[140] .
11 ya zo cikin littafin da'a'im: daga Hassan da husaini(as) cewa sunyi xawafi bayan la'asar sun sha ruwan zamzam suna tsaye.
وفي فقه الرضا: روي عن أبي عبدالله 7، عن رسول الله 6، قال : ماء زمزم شفاء لما شرب له . [141]
12 ya zo cikin fiqihul rida: an rawaito daga baban Abdullah(as) daga manzon Allah(s.a.w) ya ce: ruwan zamzam waraka ne ga abin da ka shashi domin shi.
() 13 ـ وفي الفروع : علي بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن إبن أبي عمير؛ ومحمد بن إسماعيل ، عن الفضل بن شاذان ، عن صفوان بن يحيى ؛ وإبن أبي عمير، عن معاوية بن عمّار، عن أبي عبدالله 7 قال : إذا فرغت من الرُّكعتين فأت الحَجَر الأسود وقبَّله واستلمه أو أشر اليه فإنّه لابدَّ من ذلک ، وقال : إن قدرت أن تشرب من ماء زمزم قبل أن تخرج إلى الصفا فافعل وتقول حين تشرب : «اللّهمّ أجعله علماً نافعاً ورزقاً واسعاً وشفاء من كلّ داء وسقم » قال : وبلغنا أنّ رسول الله6 قال حين نظر إلى زمزم : لولا أنّي أشقّ على اُمّتي لأخذت منه ذنوباً أو ذنوبين[142] .
13 yazo cikin furu'ul kafi: daga alyu ibn Ibrahim daga babansa daga ibn abu umairu daga muhammadu ibnisma'il daga fadalu ibn shazanu daga sufwanu ibn yahaya daga ibn abiumairu daga mu'awiyatu ibn ammar daga baban Abdullah(as) idan ka idar da raka'a biyu to kaje wajen hajarul aswad ka sumbace shi ka shafe shiko kuma kayi nuni ko ishara da hannu zuwa gareshi lallai dole kayi haka, ya ce: idan ka samu ikop shan ruwan zamzam gabaninfita ya zuwa safa to ka aikata hakan, loakcin da zaka sha kace: ( Allah ka sanya shi ilimi mai amfani da arziqi mayalwaci da waraka daga dukkanin ciwo da cuta) ya ce: mun sami labari cewa manzon Allah(s.a.w) yayain da ya kalli zamzam sai ya ce: bada ban kada in tsananta kan al'ummata ba dana xibi qaton guga kansa ko kuma in xibi guga biyu
() 14 ـ وفي الفروع : علي بن إبراهيم ، عن أبيه ، عن إبن أبي عمير، عن حمّاد، عن الحلبيّ، عن أبي عبدالله 7 قال : إذا فرغ الرّجل من طوافه وصلّى ركعتين فليأت زمزم وليستق منه ذنوباً أو ذنوبين وليشرب منه وليصبّ على رأسه وظهره وبطنه ويقول : «اللّهمّ اجعله علماً نافعاً ورزقاً واسعاً وشفاءً من كلّ داءٍ وسقمٍ » ثمّ يعود إلى الحَجَر الأسود[143] .
14 yazo cikin furu'ul kafi: daga aliyu ibn Ibrahim daga babansa daga ibn abi umairu daga hammad daga halabi daga baban Abdullah(as) ya ce: idan mutum ya idar da xawafinsa yay i sallah raka'a biyu to ya tafi wajen zamzam ya xebo qaton guga ko kuma guga biyu ya sha daga gareshi ya zuba a kansa da gadon bayansa da kan cikinsa sanna ya ce: ( ya Allah ka sanya shi ilimi mai amfanarwa da arziqi mayalwaci da waraka daga kowacce cuta da ciwo) sannan ya koma wajen dutsen hajarul aswad.
قال الله تعالى : (إِنَّ آلصَّفَا وَآلْمَرْوَةَ مِن شَعَائِرِ آللهِ.( [144]
1 Lallai dutsen safa da dutsen marwa suna daga wuraren ibadun Allah.
2 dutsen safa ya samun wannan suna sakamakon saukar adamu(as) kansa wanda shi adamu safiyullahi ne (zababben Allah) sai dutsen ya samu wannan suna albarkacin saukar adamu kansa. Ita kuma hauwa'u ta sauka kan dutsen marwa wadda ita mar'atu ce(mace) sai dutsen ya samu wannan suna na marwa daga mar'atu, tskanini safa da marwa akwai nisan mitoci 240, sannan tsayin dutsen safa ya kai mita 15 shi kuma marwa ya kai mita 8
3 sha'a'ir jam'aine na sha'iratu wadda take da ma'anar alama a harshen larabci, ya kasance kan dutsen safa akwai wani gunki mai suna (asafu) kan dutsen marwa ma haka akwai gunki mai suna (na'ilatu) ba'arin wasu musulmi sun kasance basa yin sassarfa tsakanin safa da marwa saboda waxancan gumaka kamar yadda qissar umarar ramuwa, sai Allah ya saukar da aya:
(إِنَّ آلصَّفَا وَآلْمَرْوَةَ مِن شَعَائِرِ آللهِ)
Lallai dutsensafa da marwa suna daga wuraraen ibadun Allah.
Lallai su kamar xaki ka'aba suke wadda ta kasance a zamanin jahilaya cike maqil da gumaka, lallai hakan bai hana yin xawafi daura da itaba, kamar yadda kake kewaya xakin ka'aba da xawafi haka zaka yi sassarfa da kai kawo tsakanin dutsen safa da marwa, shi xawafi wani motsi ne na kewaye wanda zaka dawo daga in da ka fara tafiya.
4 asalin safa cikin harshen larabci shi ne tsantsar dutse da babu komai kansa baubu zne zane jikinsa, sannan asalin Kalmar marwa a harshen larabci daga marina ma'ana taushi. Sha'a'ir jam'I ne daga sh'iratu da ma'anar alama.
Imam sadiq(as) yana cewa:
ـ اذا أردت الحج فجرّد قلبک لله تعالى من قبل عزمک من كل شاغل وحجاب كل حاجب (التجرّد والاخلاص).
1 Idan kayi niyyar zuwa aikin hajji ka karkaxe zuciyarka domin Allah gabanin azamarka daga dukkanin wanin Allah da zai shagaltar da kai gabarin Allah haka daga hijabin dukkanin wanda zai sanya hijbi tsakanin da Allah(karkaxewa da tsarkakewa).
2 ka fawwala al'amuranka ga Allah mahaliccinka ka dogara da shi cikin dukkanin abin da ke bayana daga motsinka da zamanka( fawwalawa da tawakkali)
3 ka sallamwa hukncin ubangijinka da qaddararsa.
4 ka yi bankwana da duniya da jin daxi da hutu da halittu(zuhudu)
5 ka fita daga haqqoqi da ya lazimceka daga bangaren ababen halitta.
6 kada ka dogara kan guzurinka da taguwarka da qarfinka da abokanka da dukiyarka da quruciyarka domin gudun kada hakan ya zama musiba da maqiyi gareka. Lallai dukkanin wanda ya yi da'awar yardarm Allah amma kuma ya dogara da waninsa to Allah mayarda wannan abu da ya dogara da shi musiba da maqiyi gareshi.(dogaro da Allah da yarda da shi).
7 ya kama mutum ya san cewa bai da wani qarfi da wata dabara face da kariyar Allah da datarwarsa(neman kariya daga Allah).
8 kayi shiri irin shirin wada bai fatan dawowa(yankewa zuwa ga Allah).
9 ka kyawunta abokantaka(kyawunta mu'amala tare da mutane)
10 ka kiyaye lokutan farillai da na sunnonin annabi(s.a.w) (kyawunta ibada)
11 da abin da ya wajaba kanka daga ladubba da haquri da juriya da godiya da tausayi da kyauta da fifita waninka cikin guzurinka cikin ts.a.won lokacin tafiya(kyawunta xabi'a).
12 sannan ka wanke zunubanka da tsarkakakken ruwan tuba(tuba)
13 ka sanya tufafin gaskiya da tacewa qanqan da kai da tsaoro( gaskiya da tsoro)
14 ka haramtawa kanka dukkanin abin da zai hanaka ambaton Allah da shiga tsakaninka da biyayyarsa(ambataon Allah da xa'arsa cikin kowanne hali)..
15 ka nemi ams.a.war Allah cikin addu'arka(addu'a tsarkakakka).
16 ka kasance kana riqo da qaqqarfar igiya( riqo da igiyar Allah qur'ani da manzo da iyalansa)
17 kayixawafi da zuciyarka tare da mala'iku daura da al'arshikamar xawafin tare da musulmi a xakin ka'aba( ruhaniyya da ma'anawiyya)
18 ka gujewa biyewa son rai, ka qauracewa dukkanin dabararka da qarfinka (sabawa so rai da zuciya)
19 ka fita daga gafalarka da zamewarka da fitowarkazuwa mina, kada ka yi buri da fatan abin da bai halsta gareka ba bai cancanceka ba(tsarki da farkawa da hikima)
20 ka yi iqirarin laifukanka a taron Arafat, ka sabunta alqawalinka wajen Allah da xayanta shi(iqirari da tauhidi)
21 ka nemi kusanci zuwa ga Allaha muzdalifa(kusantar Allah)
22 ka xaga ruhinka zuwa mala'i a'ala da hawanka dutse( xauaka da kammaluwa)
23 ka yanka wauyan son zuciya da kwaxayi lokacin da kake yanka abin hadaya(sabawa son rai)
24 kayiwurgi da sh'awe sha'awe da qazanta da miyagun ayyuka lokacin da kake jefe shaixan(jihadu nafsi)
25 ka shiga cikin aminci Allah da shingensa da kiayyewarsa da suturarsa daga bibiyar buqatarqa lokacin da kake shiga harami(amincin Allah).
26 ka aske aibobi na zahiri da baxini lokacin da kake aske gashin kanka(tsarkaka da ado)
27 ka ziyarci xaki kana tabbatar da girman ma'abocinsa da sanin girmamarsa da mulkinsa( sanin Allah)
28 ka shafi hajarul aswad domin yarda da kason ubangiji da kuma miqa wuya da qasqanta da kai ga izzarsa(yarda da qaddarar Allah da hukuncinsa)
29 ka tsarkake ruhinka da sirrinka domin haxuwa da Allah ranar da zaka haxu da shi da tsayuwarka kan safa( tacewa da soyayya)
30 kayi watsi da bankwana da wanin ubangiji da xawafinka na bankwana.
31 ka kasance ma'abocin mutumtaka daga Allah, ka kasance mai tsarkakakkun siffofi lokaicn tsayuawarka a dutsen marwa.(mutumtaka da taqawa)
32 ka daidaitu a sharaxin hajjinka.
33 ka cika alqawalinka wand aka xaukarwa ubangijinka ka zalimceshi har zuwa ranar qiyama.(cika alqawali).[145]
Natija a taqaice:
Lallai imam(as) ya yi nuni ya zuwa muhimman sirrikanhajji muyi samu alama da take na game gari duk wanda Allahya taimaka ya tafi kan haskensu zai azurta cikin rayuwarsa da bayan mutuwarsa, lallai cikinsu akwai waxanda suka ratayu da bawa tare da ubangijinsa kamar misalin yarda da qaddara da hukuncin Allah da cika alqawali da neman shingentuwa da shi, daga cikinsu akwai waxanda suka ratayu da ransa kamar yaqar biyewa son rai da zuciya da daidaita kan sahu da zuhudu gudun duniya da sallamwa ubangiji da tsarkake niyya.
Daga cikinsu akwai waxanda suka ratayu bawa tare da ragowar muane, kamar tacewa da soyayya da kiyaye mutumtakarsa da kyautata zamantakewa da ragowar mutane da kiyaye haqqoqinsu
[1]bakara:126
[2] Alkasasu:57
[3] Bakara:125
[4] Bakara:126
[5] Kuraishi:4
[6] Alkasasu:57
[7]Ankabut:67
[8] Wasa'ilul shi'a:juz 9 sh 339
[9] Annahlu:112
[10] Tafsirul ayyashi: juz 1 sh 190
[11] Saba'i:18
[12] Hajji:25
[13] Ilalul shara'i:593
[14] Alkafi:juz 4 sh 564
[15] Biharul anwar:juz 99 h 26
[16] Biharul anwar:juz 99 h 16
[17] Biharul anwar:juz 16 sh 47
[18] Bakara:125
[19] Hajji:25
[20] Tarikul baihaki:juz 6 sh 35
[21] Hajji:25
[22] Nahjul balaga:kitab 67
[23] Wasa'ilul shi'a:juz 8 babu 1-2
[24] Wasa'ilul shi'a :juz 8 sh 222
[25] Masdarin da ya gabata
[26] Wasa'ilul shi'a:juz 8 sh 225
[27] A'araf:144
[28] Bakara:189
[29] A'araf:143
[30] Taha:12
[31] Hajji wal umaratu fil kitabu was sunna:234
[32] Ilalul shara'i:433
[33] Mudaffifin:6
[34] Alkafi: juz 4 sh 209
[35] Uyunul akhbarul rida: juz 2 sh 90
[36] Biharul anwar:16
[37] Wasa'ilul shi'a:juz 9 sh 19
[38] Biharul anwar:juz 61 sh 47
[39] Bakara:125
[40] Biharul anwar:juz 61 sh 47
[41] Alkafi:juz 4 sh 401
[42] Hajji:29
[43] Tauba:17
[44] Hajji:25
[45] Bakara:192
[46] Tauba:18
[47] Anfal:34
[48] Hajji:25
[49] Isra'i:1
[50] Bakara:144
[51] Bakara:150
[52] BAKARA:144
[53] Bakara:144
[54] Alu imrana:96
[55] Ilalul shara'i:juz 2 sh 398
[56] Shamsu:9-10
[57] Bakara:125
[58] Waki'a:79
[59] Anfal:35
[60] Saba'i:46
[61] Ma'ida:97
[62] Nisa'i:5
[63] Bakara:126
[64] Alu imrana:96
[65] Hajji fil kitabu was sunna:25
[66] Alu imrana:96
[67] Alu imrana:97
[68] Ma'ida:2
[69] Kuaraishi:3
[70] Alhajji fil kitabu was sunna: sh 25
[71] Alkafi:juz 4 sh 189
[72] Biharul anwar: juz 96 sh 56
[73] Majma'ul baharaini: 1 sh 134
[74] Biharul anwar: juz 96 sh 59
[75] Alkafi:juz 4 sh 189
[76] Alkafi:juz 4 sh 195
[77] Hajji:26
[78] Bakara:127
[79] Nuru:36
[80] Ilalul shara'i: juz 2 sh 399
[81] Hijru:21
[82] ZumAR:6
[83] Hadidu:25
[84] Annhlu:96
[85] Wasa'ilil shi'a:juz 9 sh 403
[86] Alkafi:juz 4 sh 185
[87] Biharul anwar: juz 96 sh 222 h 1
[88] Wasa'ilul shi'a:juz 10 sh 206
[89] Alu imrana:19
[90] Da'a'imul islam:12 sh 293
[91] Ilalu:juz 2 sh 427
[92] 'aaraf:172
[93] Amali tusi: juz 2 sh 91
[94] Furu'ul kafi: juz 4 sh 180-186
[95] Ilalu: 2 sh 424
[96] Ilalu:juz 2 sh 427
[97] Furu'ul kafi:juz 4 sh 572
[98] Alfaqihu:juz 2 sh 70
[99] Alu imrana:97
[100] Furu'ul kafi:juz 4 sh 530
[101] Tahzib : juz 5 sh 278
[102] Masdarin da ya gabata: sh 491
[103] Tahzib: juz 5 sh 277
[104] Hajji:28
[105] Alkafi:juz 4 sh 214
[106] Wasa'ilul shi'a: juz 3 sh 539
[107] Biharul anwar: juz 52 sh 337
[108] Wasa'ilul shi'a:juz 9 sh 431
[109] Biharul anwar: juz 56 sh 86
[110] Lisanul arab: juz 12 sh 137
[111] Alkafi:juz 4 sh 191
[112] Biharul anwar: juz 96 219
[113] Alkafi: juz 4 sh 210
[114] Furu'ul kafi: juz 2 sh 408
[115] Furu'ul kafi: juz 4 sh 408
[116] Masdarin da ya gabata
[117] Kitabul wafi: juz 2 kitabul hajji sh 127
[118] Alwafi:juz 2 kitabul hajji sh 127
[119] Furu'ul kafi:juz 2 sh 134. Alfakihu: juz 2 sh 409
[120] Furu'ul kafi:juz 4 sh 409
[121] Masdarin da ya gabata
[122] Masdarin da ya gabata
[123] Masdarin da ya gabata: sh 410
[124] Ilalu:juz 2 sh 429
[125] Uyunu akhbarul rida: juz 2 sh 16
[126] Biharul anwar:juz 99 sh 197, kashefaul gumma: juz 2 sh 414
[127] Ilalu: juz 2 sh 424
[128] Masdarin da ya gabata: 428
[129] Masadarin da ya gabata: sh 429
[130] Biharul anwar: juz 96 sh 428
[131] Mustajar xaya daga cikin rukunan xakin ka'aba gudu ne kuma ana kiransa da suan rukunul multazam.
[132] Furu'ul kafi: juz 4 sh 411
[133] Fikhul rida:27
[134] Biharul anwar: juz 99 sh 199. Kiatabul hidaya: sh 40
[135] Alkafi: juz 4 sh 250
[136] Biharul anwar:juz 57 sh 45
[137] Wasa'ilul shi'a: juz 9 sh 350
[138] Alfakihu:juz 2 sh 135
[139] Masdarin da ya gabata daga littafin almasain: juz 2 sh 574
[140] Da'a'imul islam: juz 1 sh 315
[141] Fikihu rida:46. Alfakihu: juz 2 sh 135 daga imam sadik(as) ya ce: ruwan zamzam waraka domin abin da aka shahi.
[142] Zunubu ma'anarsa shi ne katon guga da ake xebo ruwa daga rijiya da shi. Sannan maganar annabi(as) na nuni da cewa yana jin tsoron kada al'ummarsa su riqi hakan matsayin sunna sai ya wayi gari tsanani garesu. Mir'atul ukul: juz 3 sh 326
[143] Masdarin da ya gabata
[144] Bakara:158
[145] Mbahu shari'a:142