b maulidin imam zainul abidin
sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Labarun da ba tsammani

    maulidin imam zainul abidin


    Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

    A ranar biyar ga watan Sha’aban shekara ta talatin da takwas ta hijirar Ma’aiki (s.a.w.a) matar Imam Husaini (a.s) ta haifi danta mai albarka.

    Lokacin da aka isar da wannan labari mai dadi ga Amirul Muminina Ali bn Abi Talib (a.s), sai ya yi sujada don nuna godiyarsa ga Allah Madaukakin Sarki, daga nan kuma sai ya sa masa suna Aliyu. Shi dai wannan jariri da aka haifa shi ne Allah Ya kaddara zai ba shi matsayi na Imamanci, don kuwa shi ne Imami na hudu na daga Imaman gidan Manzon Allah (s.a.w.a) bayan kakansa Imam Ali (a.s) da baffansa Imam Hasan al-Mujtaba da kuma babansa Imam Husaini (a.s), kamar yadda Allah din ya kaddara dukkan sauran Imamai (a.s) za su kasance ne daga tsatsonsa mai albarka.

    Wannan batu kuwa ba wai kirkiransa muka yi ba, face dai magana ce daga Manzon Allah (s.a.w.a), don kuwa an ruwaito Imam Husain bn Ali (a.s) yana cewa: Wata rana na tafi wajen kakana Manzon Allah (s.a.w.a), sai ya zaunar da ni akan cinyarsa, ya ce min: ‘Hakika Allah Ya zaba daga tsatsonka, Ya Husain, Imamai tara, na taransu kuwa shi ne Ka’im dinsu, dukkansu kuwa matsayinsu guda ne a wajen Allah([i])”.

    Haka nan an ruwaito daga Ibn Abbas (r.a) yana cewa: Na ji Manzon Allah (s.a.w.a) yana cewa: Ni da Ali da Hasan da Husaini da kuma tara daga Husaini tsarkaka ne kuma ma’asumai (wadanda ba sa sabo)([ii])”.

    Har ila yau Ahmad ya ruwaito daga Masruk cewa: Wata rana muna zaune tare da Abdullah bn Mas’ud yana karantar da mu Alkur’ani, sai wani mutum ya ce masa: Ya Abdallah! Shin kun taba tambayar Manzon Allah (s.a.w.a) kuwa kan halifofi nawa wannan al’umma za ta samu? Sai Abdullah ya ce masa: ‘Ba wani mutum da ya tambaye ni tun daga lokacin da na iso daga Iraki kafinka’. Daga nan sai ya ce: Na’am, lalle mun tambayi Manzon Allah (s.a.w.a) kuma ya gaya mana cewa: Su goma sha biyu ne tamkar zababbun Bani Isra’ila([iii])”.

    An kuma ruwaito daga Abdullah bn Ja’afar al-Tayyar cewa: ‘Na ji Manzon Allah (s.a.w.a) yana cewa: Ni na fi cancanta a wajen muminai daga kawukansu, sai kuma dan’uwana Ali, wanda ya fi cancanta a wajen muminai daga kawukansu, idan ya yi shahada sai dana Hasan, shi ya fi cancanta a wajen muminai daga kawukansu, sai dana Husaini, shi ya fi cancanta a wajen muminai daga kawukansu, idan ya yi shahada sai dansa Ali, shi ya fi cancanta a wajen muminai daga kawukansu….([iv])”.

     

     

    ([i]).Yanabi’ul Mawadda na al-Balkhi al-Kanduzi, juzu’i  na 2, shafi na 105.

    ([ii]). Kamar na sama da Bihar al-Anwar, juzu’i na 36, shafi na 243 da kuma Kifayat al-Athar , shafi na 19.

    ([iii]). Musnad Ahmad, juzu’i na 1, shafi na 398, da kuma sauran ruwayoyi masu yawa da suke cikin Sahih Bukhari, juzu’i na 9, shafi na 81, da Sahih Muslim, juzu’i na 6, shafi na 4 da Bihar al-Anwar, juzu’i na 36, shafi na 230.

    ([iv]). Ikmalluddin wa Itmam al-Ni’ima na al-Saduk, shafi na 157 da al-Khisal, juzu’i na 2, shafi na 77 da kuma Uyun Akhbar al-Ridha, shafi na 28.