b Muna tayaku murnar zagayowar ranar haihuwar siddika dahira Fatima zahara amincin Allah ya kara tabbata gareta
sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Labarun da ba tsammani

    Muna tayaku murnar zagayowar ranar haihuwar siddika dahira Fatima zahara amincin Allah ya kara tabbata gareta

     



     

    Daga cikin abinda yake shiryarwa zuwa ga ismarta

    1-ayat tadhir cikin fadinsa madaukaki  

     :

     (إنَّمَا يُرِيدُ اللهُ لِيُذْهِبَ عَنْكُمُ الرِّجْسَ أهْلَ البَـيْتِ وَيُطَهِّرَكُمْ تَطْهِيرآ) ،

    Kadai Allah yana nufin tafiyar muku da datti ya kuma tsarkakeku tsarkakewa sosai.

    Allah tsarkakakke ne da iradarsa takwiniya ya tsarkake Ahlil-baiti: daga cikinsu akwai Fatima amincin Allah ya kara tabbata gareta ya kuma katangesu da isma mudlaka wajiba a hankalce da nakali.

    2-lallai ita tsaran kur’ani ce mai girma dogaro da hadisi da shi’a da sunna sukai ittifaki kansa, yayinda kur’ani ya kasance ma’asumi to haka ma tsaransa Ahlil-baiti tsatso manzo Mustafa suma ma’asumai ne.

    3-lallai ita Fatima itace tsaran Ali ba da ban shi ba da bata da tsara daga bil adama baki dayansu, babu mai aurar ma’asuma sai ma’asumi,lallai mazaje sune masu tsayuwa kan mata, Fatima idan muka cire imamanci tana da dukkanin wata falala da Ali yake da ita dukkanin abinda ya tabbata ga Ali amincin Allah ya kara tabbata gareshi to ya tabbata ga Fatima bisa lazimci, sannan dukkanin wani abu d aya tabbata ga Fatima da mudabaka to ya tabbata da dalala iltizamiyya ga sarkin muminai Ali (as)

    4-lallai ita hurul ini da ta zo da surar mutane, mala’iku ma’asumai ne hakama Fatima haura’ul insiya.

    5-dayantuwar iradar Allah da ta Allah, lallai Allah yana yarda da yardarta yana kuma yin fushi da fushinta, lallai Allah bai yi fushi domin Yunus ma’abocin kifi ba, bari dai kadai yana fushi da fushinta, dayantuwar iradarta da Allah dalili ne kan ismarta.

    6-lallai itace shugabar mataye duniya da lahira, ta yaya zata kasance shugabar matan farko dana karshe ba idan ba da ban ita ma’asuma bace.

    7-ayar mubahala, ta gabatar da mata kan kawuka, mai yiwu hakan ya zama ishara ya zuwa lallai cewa kawuka fansarta ne, {babanki ya fansheki} babanta ya fansheta da ransa.

    8-itace madaukakiyar duniya da makaskaciyar duniya  da kausul su’udi da nuzuli.

    9-itace kirjin annabi tsira da amincin Allah yak ara tabbata gareshi wand wanda yake dauke da kur’ani karo daya kuma cikin daren lailatul kadari, wanda shi daren lailatul kadari shine Fatima zahara (as).

    10-baban wanda ya san daraja sai wanda ya girmamata, babu mai sanin asraranta face wanda ya halicceta da wanda Allah yayi masa izini.  

    11- lallai ita biyayyar ta wajibi ce kan dukkanin halittu, ta yay aba zata kasance wajibi ba saki babu kaidi alhalin ita fa ma’asuma ce.

    12-ita hujjar kan hujjojin Alllah kuma itace abar koyinsu kamarcv yadda ya zo cikin hadisai masu daraja.

    13-mahadar haske biyu da hadisin Aflak, tana dauke da asraran annabta da imamanci, lallai ita babar babanta.

    14- mikakkiyar igiyar Allah dole ta kasance ma’asumiya, idan bata zama ma’asumiya ta yaya za ai riko da ita mudlakan ba tareda kaidi ba

    «قال رسول الله  صلى الله عليه واله وسلم : فاطمة بهجة قلبي وحبله الممدود بينه وبين خلقه ، من اعتصم به نجا، ومن تخلّف عنه هوى.

    Manzon Allah tsira da amincin Alla su kara tabbata gareshi da iyalansa yace: Fatima ce farin ciki zuciyata kuma itace igiyar Allah mikakka tsakaninsa da halittunsa, duk wanda yayi riko da ita ya tsira duk wanda ya barta ha halaka.

    15-jarrabata da hakuri wacce itace asasin kamala da Akhlak wanda daga cikinsa akwai zuhudu

    16-iliminta daga wurin Allah yake.

    17-ijma’i yankakke mai shiryarwa kan ismarta, kamar yadda wurin shehunnai Saduk da mufid da Dusi da wasunsu.

    18-ayoyi da riwayoyi masu tarin yawa da suke shiryarwa zuwa ga falalarta da girmanta, da ratayuwarta da duniyar gaibu.

    19-tarihinta da yadda ta rayu kamshin ismar Allah na tashi daga gareshi

    Akwai wasu fuskokin da mai dandake bincie zai iya tsinkayarsu, ya sami da yakini da yankewa da cewa lallai babu kokwanto babu shakka lallai Fatima zahara amincin Allah ya kara tabbata gareta babbar ismar Allah ce.