b muna taya daukacin al’ummar musulmi murnar zagayowar ranar da aka haifi Imam Hassan Askari (as)
sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Labarun da ba tsammani

    muna taya daukacin al’ummar musulmi murnar zagayowar ranar da aka haifi Imam Hassan Askari (as)

     

     


    an haifi Imam Abu Muhammad Hassan Askari (as) 8 ga watan Rabi’u sani hijira na da shekara 232 a birnin mai Madina  wannan ra’ayi da akasarin malamamn tarihi suka tafi kai, ana kiran Imam Hassan da Imam Aliyu annakiyu (as) da lakabin Askariyaini sakamakon a nan ne mahallin da suka zauna cikin samarra, Ibn Sukaitu ya tambayi Imam Hadi sakamakon umarnin sarkin Mutawakkil yana mai fadin cewa: mene ne ya sanya Allah ya aiko Musa (as) da sanda, ya kuma aiko Ida da warkar da kutare da makafi da raya matattu, sannan ya aiko Muhammad da kur’ani da takobi?

    Sai Imam Hadi ya bashi amsa da fadin Allah madaukaki: ( Allah maduakaki ya aiko Musa da sanda da hannu mai haske da take bayyana ba tareda wahala a cikin zamanin sihiri yake kan tashensa a lokacin matsafa da masu sihiri sunyi matukar tasiri cikin kwakwalen mutane da tunaninsu lamarin da ya kai ga karkacewarsu daga barin hanyar Allah-hanyar gaskiya hanyar shiriya, sai Musa ya zo da abinda yake ruguje da’awowinsu shine sandarsa da ta kasance tana hadiye abinda suke kag, sannan cikin hujja ya tabbatar da abinda ya rushe da’awowinsu da karerayinsu, amma wazifar Isa ta saba da Musa saboda kasantuwar zamanin Musa abin da ya shahara shine cigaban likitanci, sai ya zo musu da mu’ujiza da ta gagare su ya tabbatar musu da gazawarsu, domin sun kasance suna warakar da mutane daga cututtuka sai dai tare da hakan sun gaza warakar da kuturu da makaho, sai Annabi Isa yayi musu kalubale, ta yand aya kasance ya na shafa kutare da makafi da hannunsa sai su warke da izinin Allah, sannan bugu da kari ya zo da abinda kowa da kowa ya gaza kansa shine raya matattu da izinin Allah, hakika ya kasance yana tashin matattu da umarnin Allah lokacin da yake addu’a lamarin da ya sanya shi zama mai nasara da galaba kan su cikin fagen munazara da jidali.

    Amma aiko da manzon Allah Muhammad (s.a.w) to shi a lokacinsa abinda yake tashe shine wake-wake da fasaha da kuma takobi don daukakar kai da izza da kabilanci da alfahari da karamci da al’adunsu, sai ya zo musu da mafi girman mu’ujiza, ya rusa dukkanin da’awowinsu da hujjojinsu da ayoyi manzanci bayyanannu, kuma balagar manzo da rawar da ya taka mai girma cikin isar da sako da nusantarwa. Kuraishawa sun bi hanyoyi daban-daban da dukkanin dabaru domin taka birki ga yaduwa sakonsa da bunkasarsa sai dia cewa ba su yi nasara ba yayin da kur’ani ya kalubalance su da su zo da surori ko kuma sura guda daya rak ko da kuwa zasu tallafi junansu cikin hak, lamarin da ya sanya su fagarniya cikin amfani da nuna karfi da cutarwa sai dai cewa hakan bai amfanar da komai ba, Allah madaukaki yana cewa:   

     [واللَّهُ مُتِمُّ نُورِهِ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ]

     

    Allah zai cika haskensa ko da kuwa kafirai basa so.