b Muna taya daukacin al’ummar musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar Imam Jawad (as)
sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Muna taya daukacin al’ummar musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar Imam Jawad (as)

    Kissar haihuwarsa amincin Allah ya kara tabbata a gareshi:

    Sayyada Hakima `yar Imam Kazim (as) ta rawaito yanda aka haife shi  mai girman daraja da karamomin da suka bayyana, sai take cewa:

    لمّا حضرت ولادة خيزران أُمّ أبي جعفر(عليه السلام)، دعاني الرضا(عليه السلام) فقال: «يا حكيمة، اِحضَري ولادتها

    وأدخلني(عليه السلام) وإيّاها والقابلة بيتاً، ووضع لنا مصباحاً، وأغلق الباب علينا.

    فلمّا أخذها الطلق طَفئَ المصباحُ، وبين يديها طست فاغتممتُ بطفي المصباح، فبينا نحن كذلك إذ بدر أبو جعفر(عليه السلام) في الطست، وإذا عليه شيء رقيق كهيئة الثوب، يسطع نوره حتّى أضاء البيت فأبصرناه.

    فأخذتُه فوضعتُه في حِجري، ونزعتُ عنه ذلك الغشاء، فجاء الرضا(عليه السلام) ففتح الباب، وقد فرغنا من أمره، فأخذه(عليه السلام) ووضعه في المهد وقال لي: «يا حكيمة، الزمي مهده».

    قالت: فلمّا كان في اليوم الثالث رفع(عليه السلام) بصره إلى السماء، ثمّ نظر يمينه ويساره، ثمّ قال(عليه السلام): «أشهدُ أن لا إِلَه إلّا الله، وأشهدُ أنّ مُحمّداً رسولُ الله».

    فقمتُ ذعرة فزِعةً، فأتيتُ أبا الحسن(عليه السلام) فقلت له: سمعتُ من هذا الصبي عجباً؟! فقال(عليه السلام): «وما ذاك»؟ فأخبرته الخبر، فقال(عليه السلام): «يا حكيمة، ما تَرَونَ مِنْ عجائبه أكثر

    Lokacin da nakuda ta kama Kizaran mahaifiyar Imam Jawad (as) sai Imam Rida (as) ya kirani yace: ya Hakima ki shirya karbar haihuwarta, sai Imam (as) ya shiga da ni daki tareda unguwar zoman da zata karbi haihuwar ya bamu fitila ya kulle kofa, lokacin da  na kuda ta tsananta kanta sai fitilar ta mutu, a gabata akwai wata yar kwarya sai ta suma sakamakon mutuwar wannan fitila, yayin da muke cikin wannan hali sai ga hasken Abu Jafar Jawad cikin wannan kwarya, sai muka ga wani siririn abu kan jikinsa kamar tufafi, hasken na ta huda har sai da ya haskaka dakin muka ganshi, sai Imam Rida (as) dauke shi ya dora shi kan shimfida yace: ya hakima ki lazimci makwancinsa, Hakima tace: rana ta uku da haihuwarsa sai Imam Jawad (as) ya daga kansa sama ya dubi damansa da hagunsa sannan yace: na shaida babu abin bauatawa da gaskiya sai Allah Muhammad manzonsa ne sai kawai na tashi a firgice cikin tsoro na tafi wajen Imam Rida (as) nace masa na ji wani abin ban mamaki daga wannan jinjiri?! Sai yace: me kika ji? Sai na bashi labari, sai yace: ya Hakima kadan kika gani daga abubuwan ban mamakinsa.

    Daga wasiyoyinsa (as)

    ۱ـ قال(عليه السلام): «العَامِل بالظلمِ، والمُعينُ عليهِ، والراضِي به شُرَكَاءٌ

    Amincin Allah ya tabbata a gareshi yana cewa: mai aiki da zalunci da mai taimakonsa kai, da wanda ya yarda dukkansu abokanan tarayya ne.

    ۲ـ قال(عليه السلام): «أربعُ خِصالٍ تُعيِّنِ المَرءَ على العمل: الصحّة، والغِنَى، والعِلم، والتوفِيق

    Aminci Allah ya kara tabbata a gareshi yace: abubuwa guda hudu suna taimakon mutum kan aiki: lafiya, wadata, ilimi, taufiki.

    ۳ـ قال(عليه السلام): «إنّ لله عباداً يخصّهم بالنعم ويقرّها فيهم ما بذلوها، فإذا منعوها نزعها عنهم وحوّلها إلى غيرهم

    Amincin Allah ya kara tabbata a gareshi yace: Allah yana da wasu bayi da yake kebantarsu da ni’imomi yake ku tabbatar da su cikin matukar sun sadaukar da su, idan suka noke suka hana sai Allah ya zare wadannan ni’imomi daga garesu ya mika su ga wasunsu.  

    ۴ـ قال(عليه السلام): «من استغنى بالله افتقر الناس إليه، ومن اتّقى الله أحبّه الناس وأن كرهوا

    Amincin Allah ya tabbata a gareshi yace: duk wanda ya wadatu da Allah mutane zasu bukatu zuwa gareshi, duk wanda yaji tsoran Allah mutane zasu so shi ko basa so.

    ۵ـ قال(عليه السلام): «لن يستكمل العبد حقيقة الإيمان حتّى يؤثر دينه على شهوته، ولن يهلك حتّى يؤثر شهوته على دينه

     Amincin Allah ya tabbata a gareshi: bawa bai cika hakikanin Imani har sai ya fifita addininsa kan sha’awarsa, kuma bawa bazai taba halaka har ya fifita sha’awarsa kan addininsa.

    ۶ـ قال(عليه السلام): «الفضائل أربعة أجناس: أحدها الحكمة وقوامها في الفكرة، والثاني العفة، وقوامها في الشهوة، والثالث القوّة وقوامها في الغضب، والرابع العدل وقوامه في اعتدال قوى النفس»

    Amincin Allah ya tabbata a gareshi yace: faloli jinsi hudu ne: na farkonsu hikimad da daidaitarta cikin tunani, na biyu kame kai daga biyewa sha’awa, tsayuwarsa na cikin sha’awa, na uku karfi tsayuwarsa na cikin fushi, na hudu adalci tsayuwarsa na cikin daidaita karfin nafsu.