sababun labare Labarun da ba tsammani Labarai wanda akafi karantawa
  • Laccar Assayid Adil-Alawi kai tsaye cikin dandali sadar da zumunci na Instagram
  • Muhadarorin Samahatus Assayid Adil-Alawi cikin watan Ramadan Mai albarka a shekara ta 1442 hijiri
  • Allah ya farantawa kwanakinmu da naku, muna farin cikin nuna murna da farin ciki ga al’umma musulmi shi’a da sunna kan haihuwar Imam Mahadi
  • MUNA TAYA KU MURNAR TUNAWA DA RANAR HAIHUWAR IMAM HUSAINI A.S
  • Allah ya faranta kwanakinku da namu cikin tunawa da ranar da aka aiko da Annabi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar kofar samun biyan bukatu Imam Musa Alkazim (A.S)
  • muna taya gurguzun al’ummar musulmi murnar zagayiwar ranar haihuwar Sarkin Muminai Aliyu BN Abu Talib amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa shahada wafatin Assayida Zainab diyar Sarkin Muminai amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Muna taya ku murna da farin ciki da haihuwar Imam Muhammad Jawad amincin Allah ya tabbata a gareshi.
  • Sabon littafi mai suna (Ruhul Inaba fi Tafsiril Du’a Sari’ul Ijaba) wallafar Samahatus Assayid Adil-Alawi
  • Ubangiji ya faranta kwanakinku bisa zagayowar ranar haihu war Assayada Fatima Zahara amincin Allah ya tabbata a gareta
  • Munasabar tunawa da nasarar juyin juya halin muslunci a cikin Iran
  • Cikin taimakon Allah da talalfinsa Assayid Adil ya fara bada bahasul Karijul Usuli cikin sabuwar Daura a shekara ta 1442 hijiriya
  • Shahadar Fatima Azzahra A.S
  • Lokutan shiryye-shiryen Aklak da Akidu na Samahatus Assayid Adil-Alawi da zai kasance a tashar Alkausar ta tauraron `dan Adam
  • Muna taya daukacin al'ummar musulmi murnar zagayowar Mauludin Annabi (s.a.w) da jikansa Imam Jafar Assadik (a.s)
  • Allah ya girmama ladanku da namu da tunawa da shahadar Imam Hassan Askari amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa da wafatin Manzon Allah (s.a.w) da kuma shahadar jikokinsa Imam Hassan Almujtaba da Imam Rida (a.s
  • Allah ya grimama ladanku da namu bisa tunawa da shahadar Imam Hassan Almujtaba amincin Allah ya tabbata a gareshi
  • Allah ya girmama ladanku da namu bisa tunawa shahadar Imam Sajjad (a.s)
  • sababun labare

    Labarun da ba tsammani

    SIRRIN RANAR ASHURA

    Da sunan Allah me rahama me jin kai

    Ashura: a zamanin jiran hukumancin Imam Mahadi, me nene falasar ashura a wannan zamani? Kuma mene alaqar shi da hukumancin Imam Mahdi? Sannan tayaya zai kasance sila tsakanin zamanin da ya wuce da kuma na yanzu?

    Lallai Ashura,  ya kasance a ko wani lokaci, tun daga farkon halitta wato Annabi Adam har zuwa ranar Alqiyama, shine rigima tsakanin gaskiya da karya, tsakanin Alheri da sharri, tsakanin ci gaba da ci baya, tsakanin haske da duhu, tsakanin rundunar Allah da na shaidan, tsakanin imani da nifaqi.

    Duk da dai ashura anyi shine a ranar goma ga watan muharram na shekaran sittin da daya na hiran annabi Muhammad a filin karbala, kuma a zamanin bani umayyawa,

    Lokacin hukumancin Yazidu mazinaci, fasiqi kuma mashiyin giya dan Mu’awiya, sun cancanci la’ana na har abada kamar yadda yazo cikin ziyarar Ashura, sai dai wannan la’ana ba su kadai ya shafaba har wanda yaji abinda suka aikata kuma ya yarda dashi, don haka ya hakamata mutum ya guje sannan yayi imani da imami adili. Sa’ad umawi yayi tamabaya akan wannan ibara (اللّهم العن بني أُميّة قاطبة) wato Allah ya la’anci bani umayya dukan su, cewa shin anan ana nufin kowa da kowane na zuri’ar bani umayya? ba wai ana nufin kowa da kowa bane, sai dai abin nufi anan shine umayyawa wanda sukayi zalunci musamman ga Ahlulbaiti,

    Allah ya yi alkawari cewa zai kubutar da Addininsa ta hanun muminai bayinsa, kuma bayinsa salihaine zasu gaje wannan duniya,                  وعده الصادق أنّه سيظهر دينه على الدين كلّه، ولو كره المشركون                             

    Duniya tana jiran zuwan wannan lokaci ne, kuma dole ne akan bayin Allah na kwarai kuma mabiya tafarkin Ahlulbaiti su kasance suna jiran lokacin da za’a kafa hukuma ta gari wanda da ita Allah zai daga mutuncin musulunci, sannan da ita nifaqi zai kaskanta, wato zamanin da hasken Allah zai bayyana (وأشرقت الأرض بنور ربّها), sannan duniya kuma zata cika da adalci.

    Allah zai cika kasarsa da adalci da kuma adilai bayan ta cika da zalunci da azzalumai, ba shakka duniya tana zaman jiran wannan zamani ne wato zamanin da duniya zata barranta da zalunci.

    Wannan jira da akeyi alamane na muqaddmar  cika alkawarin da Allah yayi na tabbatar da hukumarsa a doran kasa.

    Sannan wannan jira da muminai keyi da niyyah khalisa, cikin bege da qauna, kuka da kira, da tsarkake zukata, da kuma imani da gaiba da aiki na kware kuma me amfanarwa, sannan da kusantar da zuciya ga Allah, wadanda suka sami kansa cikin irin wannan hali kuma suna masu hidima da kuma jiran imamin su sannan suna masu isarda sakon Ashura, ba shakka suna da ga cikin sahhaban Imam mahadi.

    إنّ المنتظرين في عصر الغيبة الكبرى وفي دائرة الانتظار وفي أيام عاشوراء في كل عام، وتفاعلهم مع قضية سيّد الشهداء× في كل عصر وعصر، وبمظاهر الحزن والأسى، إنّما هم على أصناف ثلاثة: فمنهم من يعصي الله ورسوله وإمام زمانه، ولم يأخذ العبر والدروس من عاشوراء الحسين×، ومنهم من يواظب على نفسه صابراً محتسباً، يحبس النفس عن المعاصي، ويصبر على إتيان الطاعات كما يصبر في المصائب. ومنهم وهم الأقلّون (وقليل من عبادي الشكور) من يزيد في ذلك بتهذيب نفسه بالجهاد الأكبر، ويبالغ في جهده وجهاده في كسب رضا مولاه إمام زمانه

    Ba komai bane dole ya kasance ts hanyar mu’ujiza, ko da rayuwar imam Mahdi ta karsance mu’ujiza, yawan shekarun da Allah ya bashi, haka ashurama take da irin wannan alaka da mahdawiyya da kuma zamani na gaba

    An rawaito daga sayyid Ashshuhada imam Husain cewa:

    عن مولانا سيّد الشهداء الإمام الحسين× قال: «منّا إثنی عشر مهدياً، أوّلهم أميرالمومنين، وآخرهم التاسع من ولدي يُحيي الله به الأرض بعد موتها، ويظهر الدين على الدين كلّه، ولو كره المشركون».

    A cikin mu akwai Mahdi guda 12 na farkon su shine Amiril muminin, na karshen su shine na tara daga tsatsona, wanda da shi Allah zai raya kasa bayan ta mutu, sannan zai bayyanar da addini a kan dukkan addinai, ko da mushirikai basu so ba.

    Wannan hadisin na nuna mana cewa yakin ashura anyi shine duk daga cikin muqaddima ne na zuhurin imam Almahdi.

    Duk wannan fafatawa da ya ta faruwa cikin tarihin magabatan mu har zuwa zamanin, duk don saboda isar da dan adama zuwa ga kamala ne da kuma sa’ada, wanda shine bauta wa Allah ba tare da shirk aba, da kuma samun sa’ada abadiyya da kuma haduwa da Allah a daukakakken gida.

    Sannan gwagwarmayan imam Mahdi a karshen zamani cigaban gwagwarmayan imam Husain ne, wanda hakan yazo cikin falsafar tarihi, kuma hadisai da ruwayoyima sun bayyana hakan, saboda ba da jini da shahidan karbala sukayi sun bayar ne don fada da azzalumai.

    Sannan lokacin zuhurinshi saiyi kira da sauti guda biyar: Na farko shine yaku mutanen duniya nine imamul qa’im, Na biyu shine ya ku mutanen duniya nine samsam me daukan fansa, Na uku shine ku saurara ya ku mutanen duniya lallai sun kasha kakana yana me kishin ruwa, Na hudu shine ya ku mutanen duniya lallali sun jefe kakakna tsirara, Na biyar shin kusani ya ku mutanen duniya sun tattakashi cikin gaba

    Acikin ziyarar nahiya ya na cewa:

    (فلئن أخرتني الدهور، وعاقني عن نصرك المقدور، فلا ندبنّك صباحاً ومساءً لأبكينك بدل الدموع دما)

    Lallai annabawa da kuma wasiyyay tun daga Adam  har Annabi Muhammad sun zone don kafa musulunci, wato tauhidi da kuma mika wuya, sannan da imani da farko da kuma ranar karshe.

    Amma illar da ke hada tsakanin zamanin da ya gabata da kuma wanda zai zo shine imam Husain da kuma ranar Ashura, shine ya hada alaqa tsakanin salihai da suka gabata da kuma salihai na nan gaba, sannan sakamako wannan illoli biyu zai bayyana ne bayan fitowan wasiyyi na karshe, domin bayyanar sa ne zai cimma burin annabawa.

    Lalai jinin imam Husain da iyalan gidan sa da kuma na sahabban sa shine ya kafar da bishiyar tauhidi da kuma na ranar karshe.

    (إن كان دين محمد لم يستقم إلاّ بقتلي فيا سيوف خذيني).

    Saboda a ranar ashura ne imani ta bayyana sannan munafunci ta bullo kai, kamar yadda ya faru bayan rasuwar ma’aiki, da wasu kwace khalifanci wacce ta isa ga yazidu la’ananne, fajiri wanda ta samo tushene tun zamanin annabi Muhammad, bayan an bisine shi sai fitina ta kunno kai har zuwa zamanin umayyawa da kuma zamanin mu na yanzu, irin su yazidu suna ne man kankare addinin musulunci ne a doron kasa

    Ganin fasadi yayi yawa imam ya tashi tsaye don ya kawo gyara cikin addinin da kakansa ya kawo har zuwa ranar alqiyama, su kuma bani umayya ba abinda ya rage game da su sai dai laanta da ake ta musu, wasu kuma suna kokarin boye abin da yayi har suna sa shi cikin khalifofin annabi guda sha biyu, wanda annabin tsira yayi bushara akan su cewa zasu tabbatar da addini a doron kasa.

    Amma shi kuma imama husai haka zai kasance cikin zukatan jama’a, domin shi fitilar tsira ne sannan kuma jirgin ceto ne, duk wanda ya yarda da abun da yazidu yayi, zai kasance cikin sansanin hukumancin yazidu har bayyanar imam Mahdi.

    Allah zai dau fansan a kana bin da umayyawa da kum abbasiyawa suka aikata a doron kasa a ranar bayyanar imam Mahdi, kamar yadda suka kasance mal’unai abakin muminai da salihan bayin Allah da kuma suran mutane na tsawon tarihi,

    Ananne zamu gane alaqar da take tsakanin gwagwarmayar imam Mahdi da kuma na imam Husain da akayi tun a shekara na 61 na hijira, domin alaqar dayace kuma ta samo asalini tun daga masdari daya

    Wannan alaqa itace a tsaida adalci a doron kasa, a ranar bayyanar imam Mahdi hadafi da kuma manufofin zasu bayyana. Wadannan manufofi na gwagwarmaya sun hada da, 1: yaqi da dagutu da kuma azzaluma, 2: tabbatar da adalci da zaman lafiya a doron kasa, 3: yaqi da fasadi da kuma barna, 4: tsarkake ruhi da kuma tarbiyanta mutane bisa tafarkin musulunci na kwarai, 5: kafa hukuma ta gari kuma adila.

    Allah tabbatar da mu daga cikin masu jiran sa na haqiqa.

    وآخر دعوانا أن الحمد لله رب العالمین.