lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

SHIN MUTUM YANA DA ZABI KO KUMA AN MASA TILAS NE_TAREDA AYATULLAH ASSAYID ALI-ALAWI

 

Idan kuna nufin zabi cikin Kalmar (mukayyar), to sai muce muku: Allah ta’ala yayi umarni da ayi masa `da’a , kuma zai bada lada kan yi masa `da’ar, haka kuma yayi hani kan aikata sabo kuma zai yi ukuba kai, sannan ya baiwa bawansa zabi cikin abinda yake aikatawa, idan ya aikata alheri sai ya ga alheri, idan kuma ya aikata sharri to nan zai ga sharri.

Daga cikin abinda ya zo cikin littafin Usulul Kafi cikin (babin Alkairu wa Sharru):

 

عن أبي جعفر× قال

 (إنّ في بعض ما أنزل الله من كتبه: اني أنا الله، لا إله إلّا أنا، خلقت الخير، وخلقت الشر، فطوبى لمن أجريت على يديه الخير، وويل لمن أجريت على يديه الشر، وويل لمن يقول: كيف ذا وكيف ذا).

وإن أردتم بلفظة (مخير) ما يقابل المسير، ومعناه التفويض، فنقول:

لا ذا ولا ذا (أي لا مسير ولا مخير) بل أمر بين أمرين

Daga baban Jafar (as) ya ce: hakika ba’arin abinda Allah ya saukar daga litattafansa: lallai ni ne Allah babu abin bautawa da gaskiya sai ni, na halicci alheri, na halicci sharri, farin ciki ya tabbata kan wanda na zartar alheri kan hannayensa, bomi da azaba su tabbata kan wanda na gudanar da sharri kan hannayensa, azaba ga wanda yake fadin yaya haka.

 

Idna kuna nufin me zabi daga Kalmar mukayyar wanda take kishiyar wanda akaiwa tilashi shi ne (tafwili) sai muce muku Kalmar bata nufin tilashi haka kuma bata da ma’anar Tafwili, bari dai wani al’amari ne tsakankanin al’amuran biyu.

 

Daga cikin abinda ya zo daga Usulul Kafi cikin (babin Aljbaru wal Kadar wal Amru bainal Amraini):

عن أبي عبد الله× قال: (لا جبر ولا تفويض ولكن أمر بين أمرين) ثم سئل وما أمر بين أمرين؟ قال: مثل ذلك، رجل رأيته على معصية فنهيته فلم ينته فتركته، ففعل تلك المعصية، فليس حيث لم يقبل منك فتركته كنت أنت الذي أمرته بالمعصية

An karbo daga Abu Abdullah (as) ya ce: babu tilashi kuma babu Tafwili sai dai cewa lamari tsakankanin al’amura biyu, sai aka tambaye shim eye lamarin tsakanin al’amura biyu? Sai ya ce: misalin hakan: wani mutum ne da ka ganshi yana kan aikata sabo sai ka hana shi sai ya zamanto bai hanu ba sai ka kyale shi, sai ya aikata wannan sabo, ba zai zamanto sakamakon bai ji nasiharka ta hana shi aikata sai ka kasance kai ne ka umarce shi da aikata sabon.

 

عن أبي عبد الله× قال: الناس في القدر على ثلاثة أوجه

1 ـ رجل يزعم أنّ الله عز وجل أجبر الناس على المعاصي فهذا قد ظلم الله عزوجل في حكمه، فهو كافر.

2 ـ ورجل يزعم أنّ الأمر مفوض إليهم، فهذا [قد] وهن الله في سلطانه، فهو كافر.

3 ـ ورجل يقول إنّ الله عز وجل كلف العباد ما يطيقون، ولم يكلفهم ما لا يطيقون، فإذا أحسن حمد الله، وإذا أساء إستغفر الله، فهذا مسلم بالغ، والله الموفق

An karbo daga Abu Abdullah (as) fadinsa: mutane cikin Kaddara sun kasu zuwa kashi uku: 1-mutumin da yake raya cewa lallai Allah Azza wa Jalla ya tilasta shi kan sabo to irin wannan mutumi ya zalunci Allah Azza wa Jalla cikin hukuncinsa, shi kafiri ne.

2- mutumin da yake raya cewa an fawwala baki dayan lamari zuwa ga mutane, mai wannan akida ya raunana Allah cikin mulkinsa, shi kafiri ne.

3-mutumin da yake cewa Allah ya kallafawa bayinsa abinda za su iya, bai kallafa musu abinda ba zasy iya ba, idan ya kyawunta aiki sai ya yi godiya ga Allah, idan ya munana sai ya nemi gafarar Allah, mai wannan akida shi cikakkken musulmi ne, Allah ne mai datarwa.

 

Daga cikin abinda ya zo cikin ta’aliki kan Kisal na Assayid Fadlullahi Tabataba’I Yazdi ya ce: fadinsa cikin Kaddara cikin fuskoki uku, ma’ana mutane cikin tabbatar da kaddara da koreta sun kasu zuwa fuskoki uku: daga cikinsu akwai wanda ya tafi kan cewa ayyuka bayi baki dayansu suna kan kaddarawar Allah Ta’ala, kuma mutane an musu tilas ne kan aikata sabo, sannan daga cikin su akwai wadanda suka tafi kan cewa ayyukan bayi basa kan kaddarawar Allah Ta’ala, suna cewa Allah Ta’ala ya fawwala baki dayan lamarin ayyukan bayinsa zuwa ga hannun bayin nasa, ya halasta musu abinda suke so, daga cikinsu akwai wadanda suka tafi kan cewa akwai wani mataki na tsakatsaki tsakanin matakan kaddara da tafwili, shi ne cewa Allah Ta’ala ya baiwa halittu iko da dama kan ayyukansu ya basu damar daga ayyukansu  ya iyakance musu iyakoki cikin haka, ya shata musu layuka da ya zana musu, ya hana su aikata munana ta hanyar kwabarsu da tsorata su da yin alkawarin azaba kan wanda yaki kwabuwa, ubangiji bai kasance mai tilastasu ta hanyar basu dama, bai kuma mika ragamar lamari hannunsu sakamakon haninsa daga mafi yawancin ayyukan, da kuma sanya iyakoki garesu cikin ayyukan, bayani yak are.

Sannan  zai iya yiwuwa kaddara ta kasance da ma’anar kudura iko, ma’ana mutane cikin kore kaddara da tabbatar da ita kashi uku suke: daga cikinsu akwai wadanda suka yi Imani kan fuska ta farko wadanda sune ake kira da Jabariya, daga cikinsu akwai wadanda suka yi Imani da fuska ta biyu wadanda sune Mufawwila ko kuma muce mu’utazilawa wadanda suka tafi kan cin gashin kan bawa cikin ayyukansa, daga cikinsu akwai wadanda suka yi Imani da mataki na tsakatsakiya kamar misalin Imamiya, abinda yake shiryarwa kan wannan tsammani da ihtimali na koshiyantakuwar Jabaru da Tafwili shi ne riwayar Abu Abdullah (as) an tambaye shi kan jabar da tafwili sai ya ce: babu maganar jabaru haka babu ta tafwili sai dai cewa wani matsayi tsakankaninsu.

Allah Ta’ala yayi umarni da yi masa biyayya ya zai kuma yi sakamako kai, haka yayi hani kan sabo haka zai yi ukuba kai, ya baiwa bawansa zabi cikin abinda yake aikatawa, idan ya aikata alheri sai ya ga alheri, idan ya aikata sharri ya hadu da sharri.

Idan cikin Kalmar mukayyar kuna nufin wanda yake kishiyantar wanda aka tilasta wanda ma’anarsa shi ne wanda aka mika komai hannunsa aka kyaleshi da kansa, to sai mu ce muku: hakika wadannan fikrori guda biyu ma’ana Jabariyanci da mu’utazilanci

Jabariyawa sunce: hakika mutum an tilasta shi ne bashi da iko kan samarwa kan amfani ko cuta, bai da iko kan yin matsi ko kishiyarsa, kadai hannun gaibu yake iko cikinsa, da wannan ne suka bayyana mutum kamar wani kayan aiki kurma da bai iya sanya hankali cikin kai kawonsa da tasarrufinsa, idan ya aikata alheri to daga Allah ne, idan ya aikata sharri shima daga Allah ne, daga nan suka yi inkari Husunu wal Kubuhu da kasantuwarsu daga hankali, saboda kan wannan ra’ayi Allah Ta’ala shi ne yake afkar da kafirci cikin zuciyar kafiri, da Imani cikin zuciyar mumini, sannan ya shigar da wanda ya so aljannarsa ko wuta, babu wata matsala cikin dawwamar mumini a wuta, wannan Magana tana cin karo da Kur’ani mai girma karara a fili, ta inda yake cewa:      

 

﴿ فَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْراً يَرَه (7) وَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرّاً يَرَه ﴾ (الزلزال: 7 ـ 8).

Duk wanda ya aikata alheri gwargwadon kwayar zarra zai gan shi* duk wanda ya aikata sharri gwargwadon kwayar zarra zai gan shi.

 

Allah ya daukaka daga abinda suke fadin babban daukaka.

 

Mufawwila (Mu’utazilawa) su suna cewa: hakika Allah ya halicci bayi sai ya fawwala lamari ya mika shi zuwa garesu, suna iya aikata abinda suka so, Allah bai da wani hannu cikinsa, da wannan suka kishiyanci fikirar jabariyanci, suka cire Allah Ta’ala daga matsayin la’akari da shi, suka bude fili ga Shaidan domin ya batar da mutane ya mallaki garuruwa, babu mai kwaba da tsawa, Allah ya tsarkaka daga abinda suke siffantawa.

an tambayi Imam Assadik (as) gameda jabar da tafwili sai ya ce: babu jabar babu tafwili sai dai cewa akwai wani al’amari tsakanin al’amura biyu.

Cikin wata kissar Abu Hanifa tareda Imam Kazim (as) tun yana karamin yaro_ya ce: ya kai yaro daga wane ne sabo yake gangarowa, sai Imam (as) ya bashi Amsa yana mai cewa: lamarin ba zai fita daga abubuwa guda uku ba: ko dai sabon ya kasance daga Allah Ta’ala sai dai kuma cewa ba daga gareshi yake ba, bai kamata mai karamci ya azbatar da bawansa ka abinda bashi ne ya aikata ba, ko dai ya kasance daga Allah Azza wa Jalla da kuma shi bawan tare, idna yayi masa azaba to yayi ne sakamakon zunubin bawan, bai kamata ga abokin tarayya karfaffa ya zaluncin abokin tarayyarsa raunanna ba.

Ko kuma dai ya kasance daga bawan kuma dama a hakika daga gareshin ne, idan Allah yayi masa ukuba kai to sakamakon zunubin da ya aikata ne, idan kuma yayi masa afuwa to don karamcinsa ne da kyautarsa.

Biye da fikrar wannan kissa, karkashin abinda za a yi istinbadi daga cikinta, muna cewa alal misali_ Allah Ta’ala ya karfe ya kuma halicci hankali, yayi umarni da alheri yayi hani da sharri, ya baiwa bawa cancanta da zabi cikin abinda zai yake aikatawa, ya sanya duniya gidan jarrabawa da ibtila’i, lahira kuma gidan bada sakamako, idan bawa ya kera wuka daga karfe lallai shi umartacce ne cikin amfani da wukar cikin halastacciyar hanya, kuma hananne daga sabanin haka, yayi aiki ya kuma samu sakamako.

 

Daga cikin abinda ya zo daga Usulul Kafi (babin jabaru wal kadaru wal amaru bainal amraini): sarkin muminai Ali (as) ya kasance zaune Kufa bayan dawowa daga Yakin Siffin sai kwatsam ga wani tsoho ya zo sai ya zauna a gabansa, sannan ya ce: ya sarkin muminai! Bamu labara kan tafiyarmu zuwa ga mutanen Sham, shin da hukuncin Allah da kaddara ya kasance? sai Sarkin muminai (as) ya ce: na’am ya kai wannan tsohom baku hau kan wani tsauni ba, ba kuma kun keta wani kwazazzabo ba face cikin hukuncin Allah da kaddararsa, sai wannan tsoho ya ce masa: wurinb Allah zan tsammace wahala ta ya Sarkin muminai, sai ya ce masa: yi shiru ya tsoho! Wallahi hakika Allah ya girmama lada cikin tafiyarku alhalin kuna tattakawa, haka ma cikin mukamanku kuna tsugne ciki, cikin juyawarku alhalin kuna juyawa, babu abinda aka tilasta ku ciki ko akai muku dole sai tsohon ya ce: ta kaka zaka ce ba a tilasta mu cikin komai a halayen d amuka samu kan mu, ba kuma anyi mana dole ba kuma tareda haka tafiyarmu da juyowarmu ya kasance da hukuncin Allah da kaddararsa! Sai ya ce masa: shin kana zton cewa ya kasance da da yankakken hukuncin Allah da tabbacacciayr kaddara, da ya kasance kamar yanda kake tunani da sakamakon da lada da ukuba sun gurbata, haka ma umarni da hani da kwaba daga Allah, da ma’anar alkawarin ni’ima da na azaba tun sun fadi, da babu wani abun zargi kan mai aikata zunubi da babu yabo kan mai kyatutatawa, da tabbas ya kasance mai zunubi, wancan Magana ce ta yan’uwna masu bautar gumaka, masu rgima da Allah, rundunar Iblis, Kadariyyar wannnan al’umma Majusawanta.

Allah tabaraka wa ta’ala ya kallafa saboda zabi, yayi hani don tsoratarwa, ya bayar da lada mai yawa kan aiki kadan, ba a saba masa ba sabida anfi karfinsa ba, kuma ba ai masa `da’a ba sakamakon tilashi, bai mika wani abu ga wani bay a fawwala shi baki daya, bai halicci sammai da kasa da abinda yake tsakaninsu ba don wargi, bai turo Annabawa masu gargadi don wasa da wargi ba   

﴿ ذَلِكَ ظَنُّ الَّذِينَ كَفَرُوا فَوَيْلٌ لِلَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ النَّارِ ﴾ (ص: 27)

Wadancananka zaton wandanda suka kafirce ne bomi ga wadanda suka kafirce daga wuta.

Sai wanann tsoho ya kama cewa kai ne Imami wanda da biyayayarsa muke fatan samun gafara daga Allah ranar kiyama, ka yi mana bayani dallla-dalla daga lamarin da ya shige mana duhu, Allah ya saka maka da kyautatawa kyautatawa.

 

«يا أبا ذر: إنك ما دمت في الصلوة فإنك تقرع باب الملك الجبار ومن يكثر قرع باب الملك يفتح له».

Ya Abu Zar: hakika kai matukar dai ka dawwama cikin sallah lallai zaka kwankwasa kofar mamallaki mabuwayi duk wanda ya yawaita kwankwasa kofa za a buda masa.

Tura tambaya