lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Bahasul Karijul Fikhi shekara 1442 cikin mas’alar shimfida hannun yatsu hade da juna hatta babban yatsa zuwa kusa da kunne

Wuri: Qum mai tsarki-cibiyar Muntada Jabalul Amil Islami-tare da Samahatus Assayid Uztaz Adil Alawi (h)

Lokaci: karfe 8 na Safe.

Fikhu (101)

22 ga Sha’aban shekara 1442

Mas’ala ta shida: shimfida hannu kan kasa yatsu hdae da juna hatta babban yatsa mai sallah yana mai fuskantar Alkibila da su.

Ina cewa: daga cikin mustahabbai cikin sujjada d afarko akwai shimfida hannu kada ya dunkule tafin hannunsa, na biyu ya shimfida yastunsa a hade da juna hatta babban yatsa kada bude tsakankaninsu, na uku ya kasance kusa da kunnuwansa biyu m na uku yana mai fuskantar Alkibla da sun a hudu Kenan.

Wannan shi ne ra’ayin da Mashhur suka karkata zuwa gareshi kuma jumlar nassoshi suna hsiryarwa zuwa gareshi daga cikinsu akwai: abin da ya zo cikin Sahihatu Hammada riwaya ce mai tsayin gaske cikin kaifiyar sallar Imam Amincin Allah ya tabbata a gareshi:

 

 (ثم سجد وبسط كفيه مضمومتي الأصابع بين ركبتيه حيال وجهه)

Sannan ya yi sujjada ya shimfida tafin hannuwansa yatsunsa hade da juna a tsakankanin gwiwowinsa kusa gefan fuskarsa.

Littafin Wasa’il: babi daga babukan ayyukan sallah hadisi na 2.

Fuskar kafa dalili: a bayyane yake cewa abin da ya aikata yana shiryarwa kan rinjayar aikin da mustahabbancinsa koma bayan wajabcinsa.

Misalinsa ya zo cikin Sahihatu Zurara mai tsayi wacce ta gabata a cikin Wasa’il babi 1 daga babukan  Af’alil salati  hadisi 3, haka cikin Kabaru Abu Basir:   

 (إذا سجدت، فأبسط كفيك)

Idan kayi sujjada to ka shimfida tafukan hannunka.

Wasa’il babi 19 daga babukan Sujud hadisi 2, haka cikin riwayar Samma’atu wacce rawaito daga Kitabu Zaidu Narasi cewa ya ga Imam Abu Hassan Alkazim kamar yanda yake zahirin kamar kuma yanda yake cikin littafin Almumtamsak da cikin Alhada’iku daga Imam Sadik amincin Allah ya tabbata a gareshi yana sallah ,,, har zuwa lokacin da yake cewa:  

فليبسطهما على الأرض بسطاً، ويفرّج بين الأصابع كلّها ...

Lallai ya shimfida tafukan hannaunsa a kan kasa shifidawa ya bude tsakankanin yatsunsa baki dayansu….

Zuwa wajen da yake cewa:

ولا يفرج بين الأصابع إلّا في الركوع والسجود، وكذا إذا بسطهما على الأرض

Kada ya bude tsakankanin yatsunsa sai cikin ruku’u da sujjada , haka idan ya shimfida su kan kasa.

Littafin Almustdarak Wasa’il babi 1 daga babukan Afa’alil salati hadisi 3 da kuma babi 20 daga babukan sujud hadisi 3.

Zahiri daga Kabar din cikin bude yatsu yana cin karoi da abin da ya gabata daga hade su da juna, duk da cewa Assayid Hakim (ks) yana cewa: tana iya yiwuwa baya cin karo da abin da ya gabata, a lokacin cin karo gayyar hadisan farko suna mikewa sakamakon kasancewasru sune suka fi yawa da kuma inganci isnadi da bayyanuwar shirywara.

Ya zo cikin Alhada’iku j 8 sh 294 daga cikinsu: ai daga cikin mustahabban sujjada akwai hade yatsu da juna yana mai fuskantar Alkibla da su yayin da yake dora su kan kasa sabida fadinsa amincin Allah ya tabbata a gareshi cikin ingantacciyar riwayar da ta gabata- Sahihatu Zurara daga Imam Bakir (A.S)

(ولا تفرّجن بين أصابعك في سجودك ولكن ضمهن جميعاً)

Lallai kada ka sake ka bude tsakankanin yatsunka cikin sujjadarka sai dai cewa ka hade su da juna baki daya.

Haka cikin Sahihatu Hammad:

 (وبسط كفيه مضموتي الأصابع بين يدي ركبتيه حيال وجهه).

Ya shimfida tafun hannunsa yatsunsa suna hade da juna tsakanin gwiwowinsa kusa da fuskarsa.

Fuskar kafa dalili: zahirin wadannan hadisai biyu da aka ambata shi ne tattarowa da hade yatsu biyar ba’arinsu zuw aga ba’ari kamar yanda Musannif (K.S) ya fada: (yatsun hannu a hade hatta babban yatsa)

An nakalto banbance babban yatsa daga garesu daga littafin Azzikra daga Ibn Junaidu, ya nakalto shi daga littafin Habalul Matin daga babban Shehinmu Shaik Baha’i (K.S) daga ba’arin Malamanmu ya ce: sai dai cewa banci karo da madogarar hakan ba.

Amma fuskantar Alkibla da yatsu hakika malaman mu biyu Addudi da Mufid (K.S) sun ambaci haka Har ma da Ibn Junaidu da wasunsu, mawallafin Alhada’iku ya ce: (banci karo da madogararsa ba face cikin littafin Arridwa sh 3 inda ya ce: (ka hade yatsunka ka dora su kan kasa kana mai fuskantar Alkibla)

Hakika an rawaito banbancewa cikin dora yatsu, Zaidu Narasi ya rawaito cikin littafinsa daga Samma’atu Bn Mihran (Almustadarak Wasa’il babi 2 daga babukan sujud   

(أنّه رأى أبا عبد الله عليه السلام إذا سجد بسط يديه على الأرض بحذاء وجهه وفرّج بين أصابع يديه ويقول أنهما يسجدان كما يسجد الوجه).

Ya ga Abu Abdullahi (A.S) idan yayi sujjada sai ya shimfida hannunsa kan kasa kusa da fuskarsa ya bude tsakanin yatsunsa ya ce lallai suma suna sujjada kamar yanda fuska take sujjada.

Ansamu cin karo da juna Tsakanin riwayoyin guda biyu: zamu iya dora gayya ta biyu kan halasci domin hade su da juna, lallai da ma’ane mafi gamewa ko kebantatta baya kore mustahabanci, ko kuma a dora kan uzuri ko banbancewa cikin kebance babban yatsa kamar yanda Ibn Junaidu ya karkata zuwa gareshi duk da cewa yana cin karo da zahirin hadisin, sai a laura

Magana tana gudana cikin fadin Musannif: (daura da kunnuwansa biyu) kamar aynda ya zo cikin Sharayi’i da waninsa, sai dai kuma abin da ya gabata cikin ingantacciyar riwaya ya tafi kan daura da fuska

Amma dangane da ra’ayoyi manya manyan Malamai cikin wannan mas’ala: cikin fadin Musannif (K.S) (yatsu hade da juna hatta babban yatsa) Assayid Ustaz Mar’ashi (K.S) ya ce: (ya zo cikin hadisi da cewa manyan yatsu guda biyu bisa mafi karfin Magana.

Sannan cikin fadin sa: (daura da kunnuwa biyu) ya zo daga Assayid Milani (K.S) yana cewa: (hakika ya zo cikin ba’arin nassoshi: daura da fuska a wasu kuma daura da kafada).

Cikin fadinsa: (yana mai fuskantar Alkibla) Assayid Qummi (K.S) yana cewa: (zai yi hakan ne yana mai fatan lada) sannan cikin fadinsa: (hannuwansa biyu zuw aga Alkibla) Assayid Husaini Qummi yana cewa bisa fata babu laifi cikin ihtiyadi cikin wannan mukami kuma shi ne ra’ayinmu. 

Tura tambaya