lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

SHIN kana karanta qur'ani

Da sunan Allah mai rahama

Yaya alakar ka da Qur’ani

Babu shakka Manzan Allah tsira da amuncin Allah sutabbata ga reshi da iyalan gidan sa bayan wafati shi ko kafin wafatin shi yayi wasiyya da abubuwa masu naiyi guda biyu 1-abu nafarko shine Qur’ani da kuma iyalan gidan sa masu tsarki saidai bayan rasuwar shi al-umar sa takasu gida biyu kasha na xaya sai sukayi riqo da Qur’ani kaxai batare da suhaxa da iyalan gidan sa ba suka bujiriwa shugabancin da Allah ya basu kuma shima Qur’ani basu fahimceshiba sanna tunda basufahimce shiba to tayaya zasu iya xabbaqashi,kuma babu wanda yake da shakka akan fifikon da qur;ani yake da shi akan sauran magagganu,to dagaske yakamata mukasance mun xanfaru da qur’ani akodayaushe mucigaba da karantar rayuwar mu shin tana dacewa da shi kowa? Domin sanin abun da yadace da dakuma wanda baidace ba yazo a hadisi cewa duk wanda yakaranta qur’ani na yaro to zaizamo yahaxa jinisa da qur;ani kuma bugu da kare yazo cewa mafificinku shi wannda koyi Al-qur;ani kuma yakoyar da shi.shi qur;ani kariyace da waraka daga dukkan bala’I da musiba kuma karanta shi yana da lada nai yawa mutiqa sanna shi mai cetone gobe kiyama yana matsayin tataunawa da ALLAH ne, yakamata na karanta qur’ani kamar yadda wani balarabe mazaunin qauye yakasance yana karantawa kamar yadda yazo a wata qissa ida shi wanna balarabe yatafi gurin manzan Allah yakuma yi imani da shi yakuma nuna sha’awar sa yanaso yakoyi karatun qur’ani sai mazan Allah ya haxashi wani sahabin sa domin yakoyar da shi to sai suka fara da suratui zilzal to yayin da suka kai kan ayarna da takecewa  فَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْراً يَرَه (7) وَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرّاً يَرَه ﴾ abun nufi duk wanda yayi wani abu na alheri to zagan shi abun nufi zaiga sakamakon sa kazalika duk wanda yayi abun tsiya zaiga sakamakon sa gobe kiyama.To sai balaraban yace yaisa haka sai yacewa sahabin da yake koyar dashi ni yanzu nasam abun da yahau kaina.to bayan hakane sai sahabi yabawa mazan Allah yadda akayi da balarabe, sai manzan Allah yace balarabe yafahimce karatu,domin yafahimci duk abun da zai aikata to yana da sakamako shin na alherine ko na tsiya a gobe kiyama.

Sanan shi qur’ani yanada sashi sashi na duk abun da dan adam yake bukata na shiriya sabo dahaka duk mutum dayake karanata Qur’ani yafahimta zaigan ya qunshi abubuwa daban-daban kamar ,Aqida,hukunce-hukunce,akalaq,labarai waxanda suke dauke da fadakarwa,to shi qur’ani ya qunshi abubuwa waxanda mutane daya zasu iya sani amma akwai wasu abubuwa daya qunsa waxanda ba kowa yake iya isa zuwa ga resuba sabo dahakanema mutum yake buqatar dauki daga ALLAH domin yasanar da shi ilimin sa ,kamara wani hadisa ya yake cewa shi ilimi haskene wanda Allah yakebawa duk wada yaso.kuma mutum na’iya rabauta da wanna ilim ne ta hanyar bin Allah sau da qafa dik inda yabaka umarni da kakasance acen to asameka gun kazalika duk abun da yahanaka to kada asameka kana aikata wani abu daya hanaka ka’aikata.to yakamata mudauki tarihi na muminan farko a cikin wanna addini namu idan nafara daga kan mazammu annabi Muhammad xan Abdullah tsara da amicin Allah sutabbata a gare shi da kuma iyalan gidan shi to shi ba’ayi kamar saba kuma baza’ayiba kazalika iyalan gidan sa,saboda sune suke fahimta qur’ani mai girma saboda tsarkin zuciyar su da tsananin bauta dakuma cewa su aka saukar da qurna domin su isar da ga mutane bakixaya a duniya saboda hakane zakaga duk wani ilimi ana jingina shi zuwa gare su, to aqarshe ina jahakali ga dukan musulmi a duk inda suke a duniya dasu ware wani loqaci domin karanta qur’ani da yinquri na fahimtar sakon da Allah yake su ya isar muminai a duk inda suke .

Da fatan Allah ya datatdamu amin

Tura tambaya