lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Abuta ko qawance

Tambayata dagane da abuta ni nakaranta littafinka wanda yake Magana akan abuta naga kuma yadda kake qarfafa abuta dakuma yin jahakali akan yawaitata to ni mutum ne wanda ya fuskanci matsala a gidamu akan abuta saboda ni matashi ne wanda baiyi aure ba kuma inada abukai masusona sosai amma iyaye na da ‘yan uwana sunhanani sakat dukkan abukan dazanyi sai sunshiga tsakani domin rabamu da su sai suce bamutanan kirkiba ne kawai ni sai nafahimci kamar sosuke na killace kaina daga cikin mutane yazamo kawai daga gida sai gida to malam wace nasiha zakayimin domin magacce wanna matsala?

Nasihata gareka yakai xana idan yazamo abuta takai ga kodai kazavi iyayaka da ‘yan gidanku ko abokanka to iyayaka da ‘yan gidanku yakamata kazava sabo da sune a gaba a duk wata alaqa.

Saidai ana zan’iya cemaka kayi qoqari kahaxa biyu watu tsakanin dagginka da abokai tahayar da baza’a sami matsala ba.kuma daxi da kari kokasan cewa aboki na gaskiya wani abune mai wahalar samu? Masammama a wanna zamanin shi kai ka jarraba abokan ka akan wani sirrika kaga yadda suke ? to kiranka da kajarraba su ko xaya daga cikin su akan wani sirrinka kuma kanemi kahaifar da matsala a tsakaninku to matiqar baka daceba to zakaga yadda zai tuna asirin ka.

Bari nabaka wani labari wanda mahaifiyarmu tabani loqacin da a farkon samartakata nima nakasance mai yawan abokai,shi wanna labari shine wani mutum ne yake da abuki guda xaya amma adaidai loqacin xansa yanada abokai arba’in,to shi wanna mutum sai yasa yayiwa xansa nasiha akan yadda yakamata yazavi aboki,to sai yafara da tambayasa shin duk waxanna abokannaka kazaxe sune a matsayin abokanka na haqiqa? Matashinka sai ya buxa baki yace da mahaifin shi aibabukata domin dukkanin su abokai nane na haqiqa sai mahaifinnasa yace bakomai mujarraba mugani daggane da abun da kake faxa yazu kaje kakamo ragonmu kakawoshi to matashika sai yabi maganar mahaifinsa yakawo rigo sai mahaifinsa ya yanka rigo yasashi a cikin akwatu to sai yacewa xanshi yanzo mutafi gidan abukinka wanda kake ganin shine babban abukinka muce masa wani mutum ne baqao yazo gidammu sai muka sami saxani da shi ,to sai muka kasheshi mukeso kataimakamana mubinne shi hakakowa sukayi suna zuwa gidan su abokin xansa yatarbesu hannu biyu yace kushigo daga ciki sai sukace a’a mumunzo ne domin kataimaka mana sukace masa kaji kaji abun dayafaru damu to yanzu taimakwanka muke bukata komai karatu yasa mai zaifito daga bakin abokin xansa,shine neman uziri da mageya cewa lalle shi bazai sami dama ba domin yanada abubuwa dayawa,to wanna shine babban abokin xansa to mai karatu yaga jawabin sa .To kuma haka sukayi tayawo har saida suka zagaye gidajen abokan xansa amma ba’asami koxaya daga cikin su yayarda dacewa zai taimakamusu sai mutuman yacewa xansa to yanzu kazu muje gidan su abokina shima mujarrabashi kagani sai suka tafi isarsu kidawiya suka kwankwasa qofa aka tambayesu suwanene? Sai suka faxi kosuwanene akayi shiru ba’a buxe ba saica saiga abokin sa yafuto da fitila da takobi ,sai mahaifin matashin yacewa abokin sa yanaga kafito da takobi da fitila? Saiyace a irin wanna loqacin nasan babu abun da zai kawoka sai dai neman taimako ita fitila dimin na hasakamaka hanya amma takobi domin nakareka da ita daga dukkan makiyinka ,to sai suka yimasa bayanin abun dayakawo su sai kawai yakada baki yace mutafi domin taimakwan ku domin duk abun dayasaku to kamar yasameni ne to amma abun mamaki shi kafin sudawo gida sun doso gidansu sai suka gano dandazan ‘yan saanda har sunzo suncika gidan su domin waxanna mutanan da xansa yake ganin abokansa ne to wanna itace irin abutarsu da shi.kuma shi matashi yaga abuta ta haqiqa a tsakanin mahaifinsa da abokin sa .

 To matasa yakamata anutsu wajan zavar abokai

ALHAMDU LILLAH.

 

Tura tambaya