lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Gamammiya Annabta da kebantacciya daga cikin hadisai masu daraja

ــ قال هشام بن الحكم : سأل الزنديق الذي أتى أبا عبد الله   فقال : من أين أثبت أنبياءً ورسلا؟

قال أبو عبد الله :

«إنّما لمّا أثبتنا أنّ لنا خالقآ صانعآ متعاليآ عنّا وعن جميع ما خلق ، وكان ذلک الصانع حكيمآ، لم يجز أن يشاهده خلقه ولا يلامسوه ولا يباشرهم ولا يباشروه ، ويحاجّهم ويحاجّوه ، فثبت أنّ له سفراء في خلقه يدلّونهم على مصالحهم ومنافعهم وما به بقاؤهم ، وفي تركه فناؤهم ، فثبت الآمرون والناهون عن الحكيم العليم في خلقه وثبت عند ذلک أنّه له معبّرين وهم الأنبياء وصفوته من خلقه ، حكماء مؤدّبين بالحكمة مبعوثين بها غير مشاركين للناس في أحوالهم على مشاركتهم لهم في الخلق والتركيب ، مؤيّدين من عند الحكيم بالحكمة والدلائل والبراهين والشواهد، من إحياء الموتى وإبراء الأكمه والأبرص ، فلا تخلو أرض الله من حجّة ، يكون معه علم يدلّ على صدق مقال الرسول ووجوب عدالته » .

Hisham bn Hakam ya ce:wani zindiki da ya je wajen Abu Abdullah (as) ya tambaye shi sai ya ce: ta yaya zan iya tabbatar da Annabawa da manzanni?

Sai Abu Abdullah (as) ya ce: kadai dai mun tabbatar da cewa muna da mahalicci makagi wanda ya daukaka daga garemu daga dukkanin abin da ya halitta, wancan mahalicci ya kasance makagi mai hikima, bai halasta halittunsa su ganshi ba ko su shafe shi ko kuma ya taba su ko su taba shi, ka kuma suyi jayayya da shi shima ya yi jayayya da su, sai ya tabbata lallai shi yanada jakadu cikin halittunsa suna shiryar da su zuwa kan abubuwa da suke gyaransu ne da amfanoninsu da abin da wanzuwarsu take tare da shi cikin barinsa kuma karewarsu take, sai masu umarni da hani suka tabbata daga mai hikima masani cikin halittunsa, ya kuma tabbata wannan lokaci cewa lallai shi yanada masu bayaninsa wadanda sune Annabawa da zababbunsa daga halittunsa, masu hikima masu ladabi da hikima wadanda aka aiko su da ita ba masu tarayya da mutane cikin yanayiyyikansu kan tarayyarsu gare su cikin fasalin yadda aka haliccesu da harhaduwarsu, masu samu goyan baya da hikima da dalilai da hujjoji da shaidodi daga wurin Allah mai hikima. Daga raya matattu da warkar da kuturu da makaho, lallai kasa ba zata taba wofinta daga hujja bar Allah ba, wanda ilimi da ke shiryarwa zuwa ga gaskiyar maganar manzon Allah da wajabtin adalcinsa ke kasantuwa tare da shi.[1]

   ــ وعن أبي الحسن الرضا  ، قال  :

«إنّما سمّي اُولو العزم لأنّهم كانوا أصحاب العزائم والشرائع ، وذلک أنّ كلّ نبيّ كان بعد نوح   كان على شريعته ومنهاجه وتابعآ لكتابه إلى زمن إبراهيم الخليل ، وكلّ نبيّ كان في أيام إبراهيم وبعده كان على شريعة إبراهيم ومنهاجه وتابعآ لكتابه إلى زمن موسى ، وكلّ نبيّ كان في زمن موسى وبعده كان على شريعة موسى ومنهاجه وتابعآ لكتابه إلى أيام عيسى ، وكلّ نبيّ كان أيام عيسى وبعده كان على منهاج عيسى وشريعته وتابعآ لكتابه إلى زمن نبيّنا محمّد.

فهؤلاء الخمسة اُولوا العزم وهم أفضل الأنبياء والرسل   :، وشريعة محمّد لا تنسخ إلى يوم القيامة ، ولا نبيّ بعده إلى يوم القيامة ، فمن ادّعى بعده نبوّة أو أتى بعد القرآن بكتاب فدمه مباح لكلّ من سمع ذلک منه » .

Daga Abu Hassan Rida (as) ya ce: kadai an sanyawa annabawa ulul azmi wannan suna sakamakon sun kasance ma'abota Azamomi da shari'a, hakan ya kasance saboda lallai dukkanin Annabin da ya zo bayan Nuhu (as) ya kasance kan shari'arsa da tsarinsa mai bin littafinsa har zuwa zamanin Ibarahim badadin Allah, dukkanin wani annabi lokacin Ibrahim da bayansa to ya kasance kan shari'arsa da tsarinsa da tafiya  kan littafinsa har zuwa zamanin Musa, haka dukkanin wani annabi a zamaninsa da bayansa to yana kasancewa ne kan shari'arsa da tsarinsa da tafiya kan littafinsa har zuwa zamanin Isa, haka shima dukkanin wani annabi a zamaninsa da bayan zamaninsa yana kan shari'arsa da tsarinsa da tafiya kan littafinsa har zuwa zamanin annabinmu Muhammad (s.a.w).

Wadannan annabawa biyar ulul azami sune mafi falalar cikin annabawa da manzanni (as) sharia'ar Muhammad ba za a shafe ta ba har zuwa tashin kiyama, duk wanda bayansa yayi da'awar annabta ko kuma bayan alkuur'ani ya kawo wani littafi to jinsa ya halasta daga dukkanin wanda yaji hakan daga gare shi.[2]  

ــ وعن الحسين بن نعيم الصحّاف : قلت لأبي عبد الله  7: أيكون الرجل مؤمنآ قد ثبت له الإيمان ثمّ ينقله الله بعد الإيمان إلى الكفر؟

قال : «إنّ الله هو العدل ، وإنّما بعث الرسل ليدعوا الناس إلى الإيمان بالله، ولا يدعو أحدآ إلى الكفر».

قلت : فيكون الرجل كافرآ قد ثبت له الكفر عند الله فينقله الله بعد ذلک من الكفر إلى الإيمان ؟

قال : «الله عزّ وجلّ خلق الناس على الفطرة التي فطرهم الله عليها لا يعرفون إيمانآ بشريعة ولا كفرآ بجحود، ثمّ ابتعث الله الرسل إليهم يدعونهم إلى الإيمان بالله حجّة لله عليهم ، فمنهم من هداه الله ومنهم من له يهده ».

Daga Husaini bn Na'im sahhaf: na cewa Abu Abdullah (as) shin mutum na kasancewa mumini hakika imani ya tabbatu gare shi sannan Allah bayan imanin ya daukeshi zuwa ga kafirci?

Sai ya ce: Allah shi ne adalci, kadai dai ya aiko manzanni domin suyi kira mutane zuwa ga imani da Allah kada su kira kowa zuwa ga kafirci.

Sai nace: sai mutum ya kasance kafiri hakika kafirci ya tabbata gare shi wurin Allah sai bayan haka sai Allah ya dauko shi daga kafirci zuwa imani?

Sai ya ce: Allah mabuwayi mai girma ya halicci mutane kan fidira wacce ya kage su kai basu san imani da shari'a bah aka kafirci da jayayya ba, sannan Allah ya aiko da manzanni zuwa gare su suna kiransu zuwa ga imani da Allah wanda hujjar Allah ce kansu, daga cikinsu akwai wanda Allah ya shirayar da shi daga cikinsu kuma akwai wanda Allah bai shiryar da shi ba.[3]  

ــ وعن الرضا  ، جوابآ لأحدهم  :

«فإن قال : فلِمَ وجب عليهم معرفة الرسل والإقرار بهم والإذعان لهم بالطاعة ؟ قيل : لأنّه لمّا لم يكن في خلقهم وقواهم ما يكملوا لمصالحهم ، وكان الصانع متعاليآ عن أن يرى وكان ضعفهم وعجزهم عن إدراكه ظاهرآ، لم يكن بدّ من رسول بينه وبينهم ، معصوم ، يؤدّي إليهم أمره ونهيه وأدبه ويقفهم على ما يكون به إحراز منافعهم ودفع مضارّهم ، إذا لم يكن في خلقهم ما يعرفون به ما يحتاجون إليه منافعهم ومضارّهم ، فلو لم يجب عليهم معرفته وطاعته لم يكن لهم في مجيء الرسول منفعة ولا سدّ حاجة ، ولكان يكون إتيانه عبثآ لغير منفعة ولا صلاح وليس هذا من صفة الحكيم الذي أتقن كلّ شيء».

Daga Rida (as) cikin amsa ga dayansu:

Ya ce: idan ya ce: to me yasa Allah ya wajabta sanin manzanni da ikirari da su da mika wuya ga da'a gare su kansu? Sai ace: saboda yayinda abin da zasu kammala maslahohinsu bai kasance cikin halittarsu da karfinsu ba, sannan makagi ya kasance madaukaki daga barin ganinsa kuma rauninsu da gazawarsu  daga riskar zahiri ya kasance, sai ya zama babu wata makawa daga sanya jakada manzo tsakaninsa da tsakaninsu, wanda zai askance ma'asumi da zai sauke umarninsa gare su da haninsa da ladabinsa ya kuma tsinkayar da su kan abin da zai tabbatar da amafaninsu  da tunkude cutuwarsu, saboda cikin halittarsu abin da zasu sani da shi da abin da zasu bukatu da shi zuwa ga amfaninsu da cutuwarsu bai kasance ba, da bai wajabta saninsa da da'arsa kansu ba da zuwar manzanni bai kasance mai wani amfani gare su ba da toshe bukata, da lallai ya kasance kasantuwar zuwansa wargi ne da wasa kawai da rashin kawo gyara wana hakan ba ya daga cikin siffar mai hikima wanda ya kyawunta komai[4]

ــ وعن أبي بصير، قال : قلت لأبي عبد الله  : لأيّ علّة أعطى الله عزّ وجلّ أنبياءه ورسله وأعطاكم المعجزة

فقال : ليكون دليلا على صدق ما أتى به ، والمعجزة علامة لا يعطيها إلّا أنبياءه ورسله وحججه ليعرف به صدق الصادق من كذب الكاذب.

 

Daga Abu basir, ya ce: na cewa Abu Abdullah (as) da wanne dalili Allah mabuwayi mai girma ya baiwa annabawansa da manzanninsa da ku mu'ujiza?

Sai ya ce: domin ya kasance dalili kan gaskiyar abin da ya zo da shi, ita mu'ujiza alama ce da bai bayar da ita face ga annabawansa da manzanninsa da hujjojinsa domin a san gaskiyar mai gaskiya daga karyar makaryaci[5]

ــ وقال عليّ بن محمّد بن الجهم لمولانا الرضا  7: يا بن رسول الله، أتقول بعصمة الأنبياء؟ قال:  بلى.

Aliyu bn Jaham ya cewa shugabanmu Rida (as) ya dan manzon Allah, shin kaima kayi imani da ma'sumancin annabawa?

Sai ya ce: na'am.[6]

ــ وقال أمير المؤمنين  7 في ضمن خطبة له  :

«فبعث محمّدآ بالحقّ ليخرج عباده من عبادة الأوثان إلى عبادته ، ومن طاعة الشيطان إلى طاعته ، بقرآن قد بيّنه وأحكمه ليعلم العباد ربّهم إذ جهلوه ، وليقرّوا به إذ جحدوه ، وليثبتوه بعد إذ أنكروه ، فتجلّى سبحانه لهم في كتابه من غير أن يكونوا رأوه بما أراهم من قدرته ...» .

Sarkin muminai (as) cikin wata hudubarsa ya ce: sai Allah ya aio da Muhammad (s.a.w) da gaskiya domin ya fitar da bayinsa aga bauta gumaka zuwa ga bautar Allah, daga da'a ga shaidan zuwa da'ar Allah, da kur'ani hakika ya bayyana hkunce-hukuncensa domin bayi su san waye ubangijinsu idan suka jahilce shi, domin suyi ikirari da shi idan sun jayayya da samuwarsa, domin su tabbatar da shi bayan da sun yi inkarinsa, sai tsarki ya tabbatar masa yayi tajalli gare su cikin littafinsa ba tare da sun ganshi da ido da abin da ya nuna musu daga ikonsa.[7]

ــ وقال   :

«ثمّ إنّ الله بعث محمّدآ   بالحقّ حين دنا من الدنيا الانقطاع ، وأقبل من الآخرة الاطلاع ، وأظلمت بهجتها بعد إشراق ، وقامت بأهلها على ساق ، وخشن منها مهاد... ـإلى أن يقول :ـ ثمّ أنزل عليه الكتاب نورآ لا تطفأ مصابيحه ، وسراجآ لا يخبو توقّده ، وبحرآ لا يدرک قعره ، ومنهاجآ لا يضلّ نهجه ، وشعاعآ لا يظلم ضوءه ، وفرقانآ لا يخمد برهانه ، وتبيانآ لا تهدم أركانه ، وشفاء لا تخشى أسقامه ، وعزّآ لا تهزم أنصاره ، وحقّآ لا تخذل أعوانه ، فهو معدن الإيمان وبحبوحته ، وينابيع العلم وبحوره ، ورياض العدل وغدرانه ، وأثافي الإسلام وبنيانه ...».

Amincin Allah ya kara tabbata gare shi ya ce: sannan ya aiko da Muhammad (s.a.w) da gaskiya lokacin da yankewa daga duniya ta kusanto tsinkaya zuwa ga lahira ta fuskanto, duniya ta duhuntar da haskenta bayan haskawarsa, ta mikar da wanda ke cikinta tsaye kan kwauri, makwanci yayi kaushi…har zuwa inda yake cewa-sannanysa saukar masa da littafi haske da fitilunsa basa mutuwabaya. Fitila wacce kunnuwarta bai bushewa, tafki da ba cimma kasansa matafiya da bai batar da wanda ya bishi, kyalkyali da haskensa baya yin duhu, mai banbancewa wand aba a rusa hujjojinsa, bayani filla-filla ba a iya rusa rukunansa, waraka da ba a tsoran cututtukansa, buwayar da ba cin nasara kan mataimakanta, gaskiya da ba tozarta mataimakanta, shi ne ma'adanin imani da farfajiyarsa, mabubbugan ilimin tafkunansa, dausayin adalci da tsirransa, turakun muslunci da gininsa



[1] Biharul-anwar: m 11 sh 29

[2] Biharul-anwar: m 11 sh 34

[3] Biharul-anwar: m 11 sh 40

[4] Biharul-anwar:  m 11 sh 40 daga liattafin ialalul shara'I da littafin uyunu akbarul rida

[5] Biharrul-anwar: m 11 sh 71

[6] Biharul-anwar: m 11 sh 71

[7] Nahjul balaga:317

Tura tambaya