lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Ayoyin samun nutsuwa


Wadanne ayoyi ne ayoyin samun nutsuwa meye ye falalarsu?

Wani mutum yace: na ziyarci daya daga makusantana a asibiti bayan ta haihu tana cikin matsananciyar damuwa da ta kai ga ba ma ta son wani mutum yayi mata Magana, to bayan na ganta cikin wannan hali sai na karanta mata ayoyin samun nutsuwa sai tayi bacci cikin iradar Allah madaukaki da tawakkali da shi.

Sai wannan mutumi ya tafi yayin da gari ya waye sai ta kira shi da wayar tarho ta ce masa: me kayi mini ne jiya wallahi na samu damar yin cikakken bacci kai kace anyi mini allurar sa bacci sannan na farka na dauki diyar da na Haifa kuma lafiya ta ta inganta.

Mene ne sababin hakan?

Dukkan wanda aka jarrabe shi da mu da bakin ciki da rashin bacci da tsananin fushi da cutarwar shaidan da dukkanin cututtukan ruhi da zuciya to ya lazimcikaranta ayoyin nutsuwa wadanda sune:

﴿وَقَالَ لَهُمْ نَبِيُّهُمْ إِنَّ آيَةَ مُلْكِهِ أَنْ يَأْتِيَكُمُ التَّابُوتُ فِيهِ سَكِينَةٌ مِنْ رَبِّكُمْ وَبَقِيَّةٌ مِمَّا تَرَكَ آلُ مُوسَىٰ وَآلُ هَارُونَ تَحْمِلُهُ الْمَلَائِكَةُ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً لَكُمْ إِنْ كُنْتُمْ مُؤْمِنِينَ﴾

 

Annabinsu yace musu lallai ayar mulkinsa shine wani akwatu ya zo muku wanda cikinsa akwai nustuwa daga ubangijinku da ragowa daga abin da Alu Musa da Alu Haruna suka bari da Mala’iku suke dauke da shi lallai cikin wancan akwai aya gareku idan kun kasance muminai.  Bakara/248

 

﴿ثُمَّ أَنْزَلَ اللَّهُ سَكِينَتَهُ عَلَىٰ رَسُولِهِ وَعَلَى الْمُؤْمِنِينَ وَأَنْزَلَ جُنُودًا لَمْ تَرَوْهَا وَعَذَّبَ الَّذِينَ كَفَرُوا ۚ وَذَٰلِكَ جَزَاءُ الْكَافِرِينَ﴾

 

Sannan Allah ya saukar da nutsuwa kan mazonsa da kan muminai ya saukar da runduna da baku gansu ba ya azabtar da wadanda suka kafirce wancan shi ne sakamakon kafirai. Tauba/26

 

﴿إِلَّا تَنْصُرُوهُ فَقَدْ نَصَرَهُ اللَّهُ إِذْ أَخْرَجَهُ الَّذِينَ كَفَرُوا ثَانِيَ اثْنَيْنِ إِذْ هُمَا فِي الْغَارِ إِذْ يَقُولُ لِصَاحِبِهِ لَا تَحْزَنْ إِنَّ اللَّهَ مَعَنَا ۖ فَأَنْزَلَ اللَّهُ سَكِينَتَهُ عَلَيْهِ وَأَيَّدَهُ بِجُنُودٍ لَمْ تَرَوْهَا وَجَعَلَ كَلِمَةَ الَّذِينَ كَفَرُوا السُّفْلَىٰ ۗ وَكَلِمَةُ اللَّهِ هِيَ الْعُلْيَا ۗ وَاللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ﴾

 

Idan baku taimake shi ba to hakika Allah ya taimake shi yayin da wadanda suka kafirce suka fitar da shi yana na biyun biyu lokacin da yake cikin kogo lokacin da yake cewa da abokinsa kada kayi bakin ciki lallai Allah yana tare da mu sai Allah ya saukar da nutsuwars kansa ya karfafe shi da rundunar da baku ganta bay a snaya Kalmar wadanda suka kafirce makaskanciya Kalmar Allah itace madaukakiya Allah mabuwayi ne mai hikima. Tauba/40

 

﴿هُوَ الَّذِي أَنْزَلَ السَّكِينَةَ فِي قُلُوبِ الْمُؤْمِنِينَ لِيَزْدَادُوا إِيمَانًا مَعَ إِيمَانِهِمْ ۗ وَلِلَّهِ جُنُودُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ وَكَانَ اللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمًا﴾

 

Shi ne wanda ya saukar da nutsuwa cikin zukatan muminai domin su kara Imani tare da imaninsu Allah yana da rundunar sammai da kasa Allah ya kasance masani mai hikima. Fatahu/4

 

﴿لَقَدْ رَضِيَ اللَّهُ عَنِ الْمُؤْمِنِينَ إِذْ يُبَايِعُونَكَ تَحْتَ الشَّجَرَةِ فَعَلِمَ مَا فِي قُلُوبِهِمْ فَأَنْزَلَ السَّكِينَةَ عَلَيْهِمْ وَأَثَابَهُمْ فَتْحًا قَرِيبًا﴾

 

Hakika Allah ya yarda da muminai lokacin da suke maka bai’a karkashin bishiya sai ya san abin da yake cikin zukatansu sai ya saukar da nutsuwa kansu ya kuma saka musu da wani cin nasara makusanci. Fatahu/18

 

﴿إِذْ جَعَلَ الَّذِينَ كَفَرُوا فِي قُلُوبِهِمُ الْحَمِيَّةَ حَمِيَّةَ الْجَاهِلِيَّةِ فَأَنْزَلَ اللَّهُ سَكِينَتَهُ عَلَىٰ رَسُولِهِ وَعَلَى الْمُؤْمِنِينَ وَأَلْزَمَهُمْ كَلِمَةَ التَّقْوَىٰ وَكَانُوا أَحَقَّ بِهَا وَأَهْلَهَا ۚ وَكَانَ اللَّهُ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمًا﴾

 

Yayin da wadanda suka kafirce suka sanya hananar kabilanci irin kabilancin jahiliya sai Allah ya saukar da nutsuwarsa kan manzonsa da kan muminai ya lazimta musu Kalmar tak’wa sun kasance mafi cancanta da ita kuma ahalinta kuma Allah ya kasance masani ga kowanne irin abu. Fatahu/26

Tura tambaya