lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Karin karfin hadda

 

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

Mutane da yawan gaske suna fama da tareda kokawa kan matsalar yawan mantuwa da rashin hadda da karancin saurin tuna abubuwa, da yawa-yawansu musammam ma daliban ilimi da fannoni zaka same su suna bakin kokarinsu wurin magance wannan matsala da hanyoyi daban-daban, wannan duka yana komawa ga al'amura na dabi'a wani lokacin wani lokacin kuma yana komawa ga batutuwa na ma'anawiyya da ruhiya, lallai yawaita sabawa ubangiji na daga abinda yake jawo mantuwa da karancin hadda kamar yanda hakan ya zo daga madaukakan hadisai, hakama tafiya tsakiyar mata biyu da yin dariya cikin makabaru duk suna jawo wannan matsala.

Akwai wasu sabubba da suke taimakon mutum cikin dawo da kaifin basirarsa da karfafata da samun Karin hadda da karfafar riska da habbakata, daga cikin wadannan sabubba akwai magangunan gargajiya akwai kuma kayayyakin abinci, hakama akwai tarbiyantar da kai, akwai wuridai da azkar da addu'o'I da karatun kur'ani mai girma, lallai duka wannan yana kara karfin basira da hadda, sannan daga cikin wadancan jarrababbun wuridai akwai: salati.

Haka ma mutum ya zamanto mai kyawunta niyyarsa da tsarkake zuciya daga kazanta da zunubai da sabon ubangiji domin ya dace da karbar ilimi da haddace shi da dorewa kan hakak, lallai ita zuciya ita jagoran dukkanin gabban jiki, idan ta gyaru jiki ya gyaru, haramun ne kan zuciyar mai aikata zunubi mai duhun gaske haske ya shiga cikinta, sannan mutum ya nemi taimako kan hadda da karfin basira ta hanyar watsi da aikata zunubi, lallai aikata sabo kan sabo ba tareda tuba ba da kuma canja kyakkyawa da mummuna na daga abinda yake jawo mantuwa da raunin kwakwalwa da riskar ilimi.

Daga cikin abinda Kidir ya tambayi Hassan bn Ali (as)

أخبرني عن الرجل كيف يذكر وينسى ؟ قال : إنّ قلب الرجل في حُقّ ، وعلى الحُقّ طبق ، فإنّ صلّى الرجل عند ذلك على محمّد وآل محمّد صلاة تامّة ، إنكشف ذلك الطبق عن ذلك الحُقّ ، فأضاء القلب وذكر الرجل ما كان نسى ، وإن هو لم يصلّ على محمّد وآل محمّد أو نقص من الصلاة عليهم ، انطبق ذلك الطبق على ذلك الحقّ ، فأظلم القلب ونسي الرجل ما كان ذكره .

Ka bani labari kan yaya mutum yake tunawa yaya yake mantawa? Yace: lallai ita zuciyar mutum tana cikin gaskiya, kan gaskiya ta rufu, idan yayi salati ga Muhammad da iyalansa cikakken salati, sai wannan rufi da yake kan gaskiya ya yaye sai zuciyarsa ta haskakaya tuna abinda ya manta, idan kuma bai yi salati ba ko kuma ya tauye salatin, sai wannan murfi ya rufe gaskiya zuciyarsa ta yi duhu ya zama ya manta abinda ya tuna.

Ga wasu ba'arin ayyuka don neman Karin basira da lafiyarta musammam ma lokacin tsufa ta yanda zaka samu mutum yana jarrabtuwa da mantuwa. Allah ne mai taimako, daga cikinsu akwai:

1- duk wanda ya karanta duk wani suna daga Asma'ulllahi husna wanda yake dauke da harafin mimun misalin Arrahmanu da Arrahimu kafa 90 lallai yana da amfani cikin Karin basira da kawar da mantuwa, tareda dawwama kan hakan tsahon shekaru.

2- bayan daura alwala duk wanda ya rubuta ayatul kursiyu da ruwan za'afaran da wardi a kan tafin hannun damansa sannan ya lashe rubutun da harshensa yayi hakan har sau bakwai lallai zai samu Karin kaifin basira da hadda.

3-duk wanda ya rubuta wannan addu'a- da ruwan wardi da za'afaran sannan ya wanke ya sha gabanin ketowar asubahi lallai zai haddace dukkanin abinda yaji da yardar Allah. ga addu'ar:

 (بسم الله نوّر بكتابك قلبي وإشرح به صدري وأطلق به لساني بحولك وقوتك لا حول ولا قوة إلّا بالله العلي العظيم)، وإذا كنت شاكاً في أثره فلا تفعله فإنّ الختومات والأذكار والأوراد لا تنفع مع الشك والترديد كما ذكرت.

4- daga cikin abinda yake kara kaifin hadda akwai wannan addu'a musammam ma gabanin mudala'ar litattafai kamar misalin litattafan da ake darasunsu a makarantu

 (اللّهم أُرزقني فهم النبيين وحفظ المرسلين وإلهام الملائكة المقربين آمين يا رب العالمين).

5- ya zo cikin littafin mafatihul jinan cikin ta'akibatul amma: bayan idar da sallaoli ka karanta wannan addu'a wacce annabi (s.a.w) ya sanar da ita don basira

 (سبحان من لا يعتدي على أهل مملكته، سبحان من لا يأخذ أهل الأرض بألوان العذاب، سبحان الرؤوف الرّحيم، اللّهم إجعل لي في قلبي نوراً وبَصَراً وفَهمَاً وعلماً إنّك على كل شيء قدير).

Allah ya bamu sa'a da taimakonsa.

Tura tambaya