mauro,i daban-daban Taambayoyin karshe Wasu daga cikin tambayoyi Tambayoyin da akafi karantawa

Taambayoyin karshe

MANENE RA’AYINSU AKARAMAKALLAHU KAN WANNAN RIWAYA

Salamu Alaikum
1-menene ra’ayinsu malam dangane da wannan riwaya da fuskar isnadi da da ma’ana?
hadisin nan da yake cewa: (duk wanda ya mutu bai san Imamin zamaninsa bay a mutu irin mutuwar lokacin jahiliya) shin wannan hadisi mutawatiri ne a wurin mu? Shin an rawaice shi da isnadai da basu da matsala don ya zama raddi kan wanda yake cewa isnadin hadisin zai iya karbar ishkali da nakadi?
2-Shin mi’iraji da Manzon Allah (s.a.w) yaje ya kasance a loukuta da dama ko kuma sau daya ya faru? Menene dalili da shaida kan hakan
3- wanne littafi ne ya fi falala fifiko don yin munakasha da shi kan abin da ya zo cikin litattafan Kiristoci da Yahudu da kuma yi musu martani da shi.
4-shin fadin Allah ta’ala
"قُلْ فَأْتُواْ بِالتَّوْرَاةِ فَاتْلُوهَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ"
Kace ku zo da Attaura ku karanta ta idan kun kasance masu gaskiya.

 

Salamu Alaikum

 1-menene ra’ayinsu malam dangane da wannan riwaya da fuskar isnadi da da ma’ana?

 hadisin nan da yake cewa: (duk wanda ya mutu bai san Imamin zamaninsa bay a mutu irin mutuwar lokacin jahiliya) shin wannan hadisi mutawatiri ne a wurin mu? Shin an rawaice shi da isnadai da basu da matsala don ya zama raddi kan wanda yake cewa isnadin hadisin zai iya karbar ishkali da nakadi?

2-Shin mi’iraji da Manzon Allah (s.a.w) yaje ya kasance a loukuta da dama ko kuma sau daya ya faru? Menene dalili da shaida kan hakan

3- wanne littafi ne ya fi falala fifiko don yin munakasha da shi kan abin da ya zo cikin litattafan Kiristoci da Yahudu da kuma yi musu martani da shi.

4-shin fadin Allah ta’ala

"قُلْ فَأْتُواْ بِالتَّوْرَاةِ فَاتْلُوهَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ"

Kace ku zo da Attaura ku karanta ta idan kun kasance masu gaskiya.

 zai zama dalili Kenan kan cewa abin da yake hannun su ingantacce ne? shin akwai wani daga malamanmu da ya tafi kan wannan ra’ayi?

5- shin daga cikin malamanmu akwai wanda ya dogara kan hadisai da hujjar cewa babu dalili da zai sanya a samu karya cikinsu tareda kau da ido daga batun isnadi?

6- shin Ayatullahi Assayid Ku’i ya janye daga daga wassaka duk marawaicin da ya zo cikin littafin Tafsirin Qummi?

7-shin duk abin da ya zo cikin Tafsirin Qummi daga mawallafin yake ko kuma akwai wadanda suka kara wasu abubuwa cikinsa? Ta yaya zamu iya banbancewa tsakaninsu?

Shin hakan zai yi tasiri cikin la’akari da riwayoyin da littafin ya zo da su?

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

1-   Hakika wannan julma da abin da ta kunsa yana daga tawatirul ma’anawi da Ijmali a wurinmu sakamakon yawan abin da ya zo daga wannan fage cikin sanin Imamul Zaman Amincin Allah ya kara tabbata a gareshi ba zai yiwu ayi suka kan isnadin riwayar da dalalarta abin da take shiryarwa zuwa gareshi.

 

3-kana iya komawa zuwa ga abin da Allama Shaik Balagi ya rubuta (ks) haka zalika kana iya komawa ga littafin (Anisul A’alam) hakika mawallafin littafin shekaru dari gabanin musluntarsa ya kasance mabiyin addinin Kiristanci daga baya sai ya muslunta ya rungumi Mazhabar Ahlil-Baiti Amincin Allah ya kara tabbata a garesu, sannan ya rubuta littafi mujalladi bakwai raddi kan Kiristoci.

 

5- Akbariyawa daga cikin malamanmu akwai wanda ya tafi kan inganci dukkanin hadisan da suka zo cikin litattafan hadisai guda hudu na mu sune Alkafi, Fakihu, Attahzib, Istibsar.

Amma malaman Usulul Fikhu sun sun tafi kan kassama Hadisai zuwa kashi hudu: Sahihu, Hassanun, Almuwassaku, Da’ifu, sannan yana karuwa zuwa kaso ashirin  kamar misalin Mursali da Makdu’i da Marfu’i da wasunsu, wannan yana zartuwa hatta kan litattafan hadisai guda hudu na mu.

 

Tarihi: [2019/10/5]     Ziyara: [488]

Tura tambaya