mauro,i daban-daban Taambayoyin karshe Wasu daga cikin tambayoyi Tambayoyin da akafi karantawa

Taambayoyin karshe

Shin akwai wata `yar gajeriya kaifiyya la’ana da sallama cikin ziyarar Ashura

Samahatus Assayid Adil-Alawi Allah ya daukaka mukaminka da sha’aninka ya kuma datar da kai ga soyayyarsa da kusanci ya tabbatar da mu da ku a kan hanyar gaskiya.. lallai shi mai Ji ne mai amsa addu’a.
Shin akwai wata gajeriya kaifiyar karanta la’ana da sallama cikin ziyarar Ashura? Shin karanta kafa daya yana isarwa musammam idan ta kasance da niyyar neman biyan bukata..?
Sakamakon kasantuwarmu masu neman gaskiya kololuwar burinmu gaskiya da kaiwa ga Allah shine hadafinmu, lallai zukatanmu sun damfaru da turakun Al’arshin Allah mai girma, muna rokon ku bamu wani wuridi da ya dace damu zamu kasance masu yabawa da gode muku.
Ina rokon Allah madaukaki mai iko ya baku dacewa yayi daidaitaku da daidaitawarsa kuma kada ya haramta muku failarsa da kyautarsa albarkacin Muhammad da Alayensa amincin Allah ya tabbata a garesu,
Daga karshe muna rokonku addu’a ta gari da taufiki da kyawun karshe,

Shin akwai wata `yar gajeriya kaifiyya la’ana da sallama cikin ziyarar Ashura

Samahatus Assayid Adil-Alawi Allah ya daukaka mukaminka da sha’aninka ya kuma datar da kai ga soyayyarsa da kusanci ya tabbatar da mu da ku a kan hanyar gaskiya.. lallai shi mai Ji ne mai amsa addu’a.

Shin akwai wata gajeriya kaifiyar karanta la’ana da sallama cikin ziyarar Ashura? Shin karanta kafa daya yana isarwa musammam idan ta kasance da niyyar neman biyan bukata..?

Sakamakon kasantuwarmu masu neman gaskiya kololuwar burinmu gaskiya da kaiwa ga Allah shine hadafinmu, lallai zukatanmu sun damfaru da turakun Al’arshin Allah mai girma, muna rokon ku bamu wani wuridi da ya dace damu zamu kasance masu yabawa da gode muku.

Ina rokon Allah madaukaki mai iko ya baku dacewa yayi daidaitaku da daidaitawarsa kuma kada ya haramta muku failarsa da kyautarsa albarkacin Muhammad da Alayensa amincin Allah ya tabbata a garesu,

Daga karshe muna rokonku addu’a ta gari da taufiki da kyawun karshe,

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

Kaifiyar karantawa itace yanda ya zo cikin ziyarar idan kana so ka zo la’ana da ta zo cikinta kafa guda sai ka karanta kafa daya la jigina mata Kalmar 99, zaka zo hakan da niyyar Allah ya karba mana, idan ko ba haka da zaka niyyaci karantakamar yand ata zo cikin ziyarar to lallai dole ka karanta kafa dari cif cif, amma batun damfaruwar zuciya da turakun Al’arshi lallai wannan da’awa ce mai girman gaske, sannan ni ban san wani zikiri da ya dace da shi ba.

Ina rokon Allah ya shiryar da mu zuwa abin da yake cikin akwai alheri da farin ciki, Allah ya dawwamar daku cikin kwanciyar hankali da lafiya. 

Tarihi: [2021/5/26]     Ziyara: [625]

Tura tambaya