lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Arziki da ni'ima_tareda Alkalamin Assayid Ali bn Husaini Alawi

Arziki da fari ciki sababin samuwarsu na da tarin yawa; shi arziki wani hali ne na nafsu da yake zuwarwa mutum lokacin da sharuddan samuwarsa suka kammmala, daga cikin mafi muhimmancin sabubban samuwarsa akwai abinda ya zo daga hadisi mai daraja, (ya Allah ka azurta mu).

1 ـ حدّثنا أبي&، قال : حدّثنا عليّ بن الحسين السعدآبادي ، عن أحمد ابن محمّد بن خالد البرقي ، عن عثمان بن عيسى ، عن عبد الله بن مسكان ، يرفعه إلى عليّ بن الحسين عليه الصلاة والسلام ، أنّه قال ـروحي فداه ـ: من سعادة المرء أن يكون متجره في بلاده ، ويكون خلطاؤه صالحين ، ويكون له وُلد يستعين بهم ...[  مستدرک الوسائل :2 614، باب 1، الحديث 4.] .

Babana ya zantar damu yace: Aliyu bn Husaini Sa'ad Abadi ya zantar damu daga Ahmad bn Muhammad bn Khalid Albarka'I, daga Usman bn Isa daga Abdullahi bn Muskan yayi rafa'in hadisin zuwa ga Aliyu bn Husaini (as) raina fansarka cewa shi yace: daga cikin arzikin mutum shine cewa kasuwancinsa ya kasance a kasarsa kuma abokan mu'amalarsa su kasance mutane nagargaru,  ya kasance ya nada `ya`ya da suke taimaka masa.

Almustadrakul Wasa'il.

2 ـ  قال رسول الله|: ولد الرجل من كسبه ...[نفس المصدر: الحديث 5] .

Manzon Allah (s.a.w) yace: an haifi mutum tareda da arzikinsa.

3 ـ الحسن بن فضل الطبرسي في مكارم الأخلاق نقلا من المحاسن للبرقي ، عن الصادق×، قال : من سعادة الرجل أن يكون الولد بشبهه وخلقه وشمائله ...[الجعفريات : 187، باب برّ الوالدين] .

Daga Hassan bn Fadal Dabarisi cikin littafin Mukarimul Aklak ya nakalto daga Almahasin na Albraka'i, daga Assadik (as) yace: daga cikin arzikin mutum ya kasance yana da wani `da da yake kamanceceniya da shi cikin dabi'arsa da halayensa….

Daga littafin Ja'afariyat.

4 ـ عن أبي إبراهيم×، قال : كان أبي× يقول : سعد امرؤٌ لم يمت حتّى يرى خلفه من نفسه ...[مستدرک الوسائل :2 615، باب 2، الحديث 2. الجعفريات : 99، باب فضل الزوجة ،مع السند] .

Daga baban Ibrahim Imamul Kazim (as) yace: babana ya kasance yana cewa: mutumin da bai mutu sai da yaga halifansa daga gareshi hakika ya azurta.

5 ـ أخبرنا عبد الله بن محمّد، قال : أخبرنا محمّد بن محمّد، قال : أخبرنا موسى بن إسماعيل ، حدّثنا أبي ، عن أبيه ، عن جدّه جعفر بن محمّد، عن أبيه ، عن جدّه عليّ بن الحسين ، عن أبيه ، عن عليّ بن أبي طالب^، قال : قال رسول الله| من نعمة الله على الرجل أن يشبهه ولده ...[ مستدرک الوسائل :2 615، باب 2، الحديث 3. أصله في الجعفريات مع السند: 194،باب في ذكر البنات] .

Abdullahi bn Muhammad ya bamu labari yace: Muhammad bn Muhammad ya bamu labari yace: Musa bn Isma'il ya bamu labari, babana ya zantar dani daga babansa daga kakansa Jafar bn Muhammad, daga babansa Aliyu bn Husaini daga babansa daga Aliyu bn Abu Dalib (as) yace: Manzon Allah (s.a.w) yace: daga cikin ni'imar Allah kan bawa shine ace yana da `da da yake kama da shi.

6 ـ قال رسول الله|: من سعادة المرء: الزوجة الصالحة ، والمسكن الواسع ، والمركب الهني ، والولد الصالح ...[المصدر السابق : الحديث 4] .

Manzon Allah (s.a.w) yace: daga cikin arzikin mutum akwai samun mace ta gari, gida mayalwaci, kyakkyawan abin hawa, `da nagari.

7 ـ قال رسول الله|: من سعادة المرء الخلطاء الصالحون ، والولد البار... الخبر...[المصدر: الحديث 7] .

Manzon Allah (s.a.w) yace: daga cikin azurtar mutum shine ya samu abokan mu'amala nagargaru da `da mai biyayya….

8 ـ دعائم الإسلام : بإسناده عن جعفر بن محمّد، عن أبيه ، عن آبائه^، عن رسول الله|، أنّه قال : خمسة من السعادة : الزوجة الصالحة ، والبنون الأبرار... الخ ...[الزخرف : 32] .

Daga littafin Da'imul Islam da isnadinsa daga Jafar bn Muhammad daga babansa daga babanninsa (as) daga Manzon Allah (s.a.w) yana cewa: abubuwa guda biyar na daga cikin azurta: mace tagari,`ya`ya na kirki…..har zuwa karshen hadisin.

9 ـ أبو علي ابن الشيخ الطوسي في أماليه ، عن أبيه ، عن الحسين بن عبيد الله الغضائري ، عن أبي محمّد هارون بن موسى التلعكبري ، عن محمّد بن همام ، عن عليّ بن الهمداني ، عن محمّد بن خالد البرقي ، عن أبي قتادة القمّي ، قال : قال أبو عبد الله×: ثلاثة هي من السعادة : الزوجة المواتية ، والولد البارّ... الخبر...[ معدن الجواهر: 56، باب ذكر ما جاء في ستّة] .

Daga Abu Ali Shaik Dusi cikil Amali dinsa, daga babansa daga Hassan bn Ubaidullahi Algada'iri, daga Abu Muhammad Haruna bn Musa Altal'akbari, daga Muhammad Hammam, daga Aliyu bn Hamadani, daga Muhammad bn Khalid Albarka'i, daga Abu Katada Alqummi, yace: Abu Abdullah Assadik (as) yace: abubuwa guda uku su suna daga azurta: mace mai biyayya, `da mai biyayya da…… har zuwa karshen hadisin.

 

`da ni'ima ce

Mutum na cika da ni'imomin Allah tabaraka wa ta'ala, wacce ni'ima ce mafi girma daga Allah ya bashi `da da suke yi sadaukar da dukkanin karfinsu cikin yi masa tarbiya, koda yaushe suna jin tsoran kada wani abu mafi kankanta ya cutar da shi har zuwa girmansa da nunar hankalinsa, inama dai zai hankalta da wannan abu yayi musu biyayya farin ciki da murna zasu mamaye mahaifansa.

Daga cikin maganganun Sarkin muminai (as) da yake fadi cikin wani mutum da ya taya shi murna da samun `da: kayi godiya ga wanda yayi maka wannan kyauta, Allah ya sanya maka albarka cikinsa, Allah ya riskar da kai cikar karfinsa ya kuma azurtaka da biyayyarsa.

Daga littafin Gawali Durari:168, kan harafin wawun.

Debe haso da `da

Babu shakka ko kokwanto cikin cewa mutum yana debe haso da wasu ba'arin abubuwa da ya dabi'antu kansa, ta yanda shi mutum yana tafiya kafada da kafada da dabi'arsa ne, haka zalika babu shakka kan cewa abubuwa da aka dabi'antu da su sukan sassabawa a wurinsa wasu suna dacewa da dandanonsa dari bisa da dari wasu kuma kasa da haka haka dai, wannan dukkaninsu cikin garizozi na farko-farko kenan da halittar mutum.

Sannan su mutane suna sassabawa kan sassabawar dandanon kowannensu, sai kaga wani ya kasance abu so nda kauna wurin wasu ba'arin mutane amma kuma wurin wasu ba'arin ya zama abin kyama basu kaunarsa kwata-kwata, kamar yanda wani mai magana yake cewa: bada ban sassabawa dandanon mutane ba da kaya sun yi kwantai a kasuwanni.

Daga cikin abinda ya kamata mu tunatar a anan shine cewa tareda sassabawar dandanonsu da da yanayiyyikansu da mahallan rayuwarsu, sai dai cewa kuma dukkaninsu sun yi ittifaki cikin abu guda daya kai hatta dabbobi ma sun yi tarayya da shi cikinsa, ba komai ne wannan abun ba da ya wuce debe haso da `da, yara da babba, talaka da mawadaci, fari da baki mutum mai daraja da kaskantacce baki dayan kowannensu yayi tarayya cikin kauna da debe haso da `da yana kuma ganinsu mafi kyawun halittu.

Na hakaito cewa an cewa Hankaka: mun zo da mafi kyawun `dan tsako sai ya zo da `dansa daidai lokacin da `dan Hankaka yana daga cikin mafi munin `ya`yan tsuntsaye, to ka dora kan wannan.

1 ـ أبو علي الأشعري ، عن محمّد بن سالم ، عن أحمد بن النضر، عن عمرو ابن شمر، عن جابر، عن أبي عبد الله×، قال : أتى رجل رسول الله|، فقال : يا رسول الله إنّي راغب في الجهاد، نشيط ، قال : فقال له النبيّ |: فجاهد في سبيل الله، فإنّک إن تقتل تكن حيّآ عند الله ترزق ، وإن تمت فقد وقع أجرک على الله، وإن رجعت ، رجعت من الذنوب كما ولدت ، قال : يا رسول الله (صلّى الله عليه وآله الكرام البررة ) إنّ لي والدين كبيرين يزعمان أنّهما يأنسان بي ، ويكرهان خروجي ، فقال رسول الله صلّى الله عليه وآله الطاهرين : فقرّ مع والديک ، فوالذي نفسي بيده ، لاُنسهما بک يومآ وليلة خيرٌ من جهاد سنة ...[ معدن الجواهر: 51] .

Daga Abu Ali Ash'ari daga Muhammad bn Salim daga Ahmad bn Nadar daga Amru bn Jabir daga Abu Abdullah (as) yace: wani mutum ya zo wajen Manzon Allah (s.a.w) sai yace: ya Manzon Allah hakika ina kwadayi cikin jihadi, yace: sai Annabi (s.a.w) yace masa: to kayi jihadi cikin tafarkin Allah lallai idan aka kasheka zaka kasance rayayye wurin Allah kana mai azurtuwa, idan ka mutu lallai ladanka zai fada kan Allah , idan kuma ka dawo to zaka dawo daga barin zunubi kamar yanda mahaifiyarka ta haifeka fes, yace: ya Manzon Allah (s.a.w) inada wani mahaifa tsofaffi suna raya cewa suna debe haso da ni, ba kuma sa son in fita yaki, sai Manzon Allah (s.a.w) yace: kaje ka zauna wurin iyayenka, na rantse da wanda raina ke hannunsa debe hasonsu dakai yini da dare shi yafi alheri daga jihadi tsahon shekara guda.

2 ـ الصادق×: الاُنس في ثلاث : في الزوجة الموافقة ، والولد البارّ، والصديق المصافي ...[ الكافي :2 130، باب البرّ، الحديث 20. والأخلاق : 116، باب 10] .

Daga Assadik (as) debe haso na cikin abubuwa uku: cikin mace mai mika wuya, `da mai biyayya, aboki mai tace soyayya.

3 ـ قيل : اُنس المرء في خمسة أشياء، منه : الولد البارّ...[المستدرک :2 632، باب 77، الحديث 10] .

Ance debe hason mutum yana cikin abubuwa guda biyar, daga cikinsu akwai: `da mai biyayya.

4 ـ عليّ بن إبراهيم ، عن محمّد بن عيسى ، عن يونس بن عبد الرحمن ، عن عمرو بن شمر، عن جابر، قال : أتى رجل رسول الله|، فقال : إنّي رجل شابّ 

نشيط ، واُحبّ الجهاد، ولي والدة تكره ذلک ؟ فقال له النبيّ|: ارجع فكن مع

والدتک ، فوالذي بعثني بالحقّ ، لاُنسها بک ليلة خير من جهادک في سبيل الله سنة [معدن الجواهر: 60] .

Daga Aliyu bn Ibrahim daga Muhammad bn Isa daga Yunus bn Abdur-Rahman daga Amru bn Shimru daga Jabir, yace: wani mutum ya zo wajen Manzon Allah (s.a.w) sai yace: hakika ni mutum saurayi matashi mai jin nishadi, ina son jihadi, amma ina mahaifiya bata kaunar haka, sai Annabi (s.a.w) yace masa: koma wajenta ka zauna tareda ita, na rantse wanda ya aiko ni da gaskiya debe mata haso dare guda yafi alheri daga yin jihadinka cikin tafarkin Allah na tsahon shekara guda.

5-Kudub Rawandi ya awo cikin littafin Lubbul Albabu yace: wani mutum yace: Manzon Allah (s.a.w) na zo inyi maka mubaya'a kan hijira amma na bar mahaifana suna ta kuka, sai Manzon Allah (s.a.w) yace koma gida ka sanya su dariya….

 


Tura tambaya