mauro,i daban-daban Taambayoyin karshe Wasu daga cikin tambayoyi Tambayoyin da akafi karantawa

Taambayoyin karshe

Wasu daga cikin tambayoyi

ME AKE NUFI DAGA DARAJA TA GOMA

ME AKE NUFI DAGA DARAJA TA GOMA MENE NE MA’ANAR (DANA SO DANA CIRO MUKU DA HASKE DAGA WANNAN RUWAN)
Riwayar Salmanu Allah ya kara masa yarda cikin daraja ta goma me ake nufi daga gareta?
Sarkin muminai Ali (as) yana cewa:
(لو شئت لتخذت لكم من هذا الماء نورا)
Da na so da na fitar muku da haske daga cikin wannan ruwa.

Mene ne Sarkin Muminai (a.s) yake nufi daga wannan Magana?

 

Riwayar Salmanu Allah ya kara masa yarda cikin daraja ta goma me ake nufi daga gareta?

Sarkin muminai Ali (as) yana cewa:

(لو شئت لتخذت لكم من هذا الماء نورا)

Da na so da na fitar muku da haske daga cikin wannan ruwa.

 

Mene ne Sarkin Muminai (a.s) yake nufi daga wannan Magana?

 

Da sunan Allah mai Rahama mai jin kai

 

Ka sani shi Imani na daga Makula tashikikiya yana martabobi duliya da ardiya  kamar misalin haske da ake riskarsa banbanci nawa ne tsakanin hasken rana da haske kyandir amma ai dukkanin ka ga haske ne amma ina kasa ina sama, banbanci tsakanin haskayen guda biyu kamar nisan da yake tsakanin sama da kasa ne ta fuskan yalwa da zamani da bigire  da hali da yanayi to haka lamarin yake cikin Imani da Allah da ranar lahira da dukkanin abinda cikamakin Annabawa Muhammad (s.a.w) ya zo da shi da iyalansa tsarkaka amincin Allah ya tabbata a garesu, dukkanin Shia’r iyalan Manzo sun yi Imani da haka baki daya sai dai cewa imaninsu yana da martabobi da darajoji cikin ingantattun hadisai ishara kan haka ta zo cewa Imani yana da darajoji `dai`dai har guda 400, ya isar cikin ba’arinsu darajoji goma ta yiwu ya kasance ishara zuwa ga jiga-jigan darjoji daga 400 kamar yanda suke ga Salmanu muhammadi Allah ya kara masa yarda, lallai ya kasance cikin tsploluwar martabobin Imani da kurewarsa gwargwadon dai karfin da mutum  yake da shi kamar misalin Salmanu Imani y agama kwarara da dukkanin cikarsa gareshi sai ya zama ya cimma kololuwa da darajoji goma, daga cikin mutane akwai wanda ya cimma gud atara kamar misalin Abu Zarru  idan kana son sanin nisan da yake tsakanin darajojin goma to ya zo cikin hadisi  

 (لو علم‏أبوذر ما في قلب سلمان لكفّره ولقال رحم اللَّه قاتل سلمان)

Da Abu Zarru zai san abinda yake cikin zuciyar Salmanu da ya kafirta shi da yace Allah ya jikan makashin Salmanu.

Ma’ana daraja da Salmanu yake da ita misalin Abu Zarru bai zai iya daukarta ba, haka nisan zango yake cikin ma’arifa da Imani cikin wasu darajojin na Imani, babu wanda zai iya sanin darajar da Salmanu yake da ita sai wanda ya kasance sama da shi kamar misalin Imami Ma’asumi Amincin Allah ya kara tabbata a gareshi wanda ya kusantar da Salmanu daga Ahlil-baiti ko kuma wanda yake cikin martabar Salmanu cikin siffa, amma wanda yake kasa da shi ba zai taba sanin sa kamar yanda `dan aji `daya ba zai san abinda ke gudana a aji na biyu ba, amma wanda ya kasance a aji na iyu lallai shi zai san abinda yake cikin ajin da ma wanda yake aji `daya wannan bayyananne lamari ne, idan kana son sanin wane ne Salmanu wacce daraja yake da ita cikin Imani ta ka zage danste ka g aka zama irinsa a zamaninka cikin tak’wa da tsantseni da ilimi da falala da Imani don kasan wane ne Salmanu mene ne darajarsa a Imani, misalina bawa mai aikata sabo kaskantacce ta kaka zai iya sanin darajar Salmanu Allah ya kara masa yarda a cikin Imani, nesa-nesa?!!!

Amma tambaya ta biyu : daga cikin litattafan da aka wallafa a wannan zamani cikin ilimummukan dabi’a sun yada wannan hadisi mai daraja da bayani filla-filla kamar yanda yake cikin littafin Imani Imam yana kira zuwa ga Ilimi  da cewa shi daga ruwa yake da yake haifar da haske da makamashin wutar lanatarki, sai ka nemi wannan littafi. 

Tarihi: [2019/10/19]     Ziyara: [455]

Tura tambaya