mauro,i daban-daban Taambayoyin karshe Wasu daga cikin tambayoyi Tambayoyin da akafi karantawa

Taambayoyin karshe

NI BAZAWARACE JAHILA WANI YA AURE NI AUREN DA’IMI

Salamu Alaikum
Ni bazawara ce Jahila kuma I ina kan Mazhabar Ahlil-baiti to shine wani mutumi ya aureni auren da’imi yayi mini alkawari zai aure ni a bayyane bayan shudewar lokaci domin akai ga tsara al’amarin iyali da dangi su yarda da auren, bayan shekaru hudu sai gashi ya zo yana cewa wai dole ni in janye daga dukkanin hakkokina da suke kansa a matsayina matarsa da hujja cewa wai baya niyyar bani ko sisi daga gadonsa.

 

Salamu Alaikum

Ni bazawara ce Jahila kuma I ina kan Mazhabar Ahlil-baiti to shine wani mutumi ya aureni auren da’imi yayi mini alkawari zai aure ni a bayyane bayan shudewar lokaci domin akai ga tsara al’amarin iyali da dangi su yarda da auren, bayan shekaru hudu sai gashi ya zo yana cewa wai dole ni in janye daga dukkanin hakkokina da suke kansa a matsayina matarsa da hujja cewa wai baya niyyar bani ko sisi daga gadonsa.

Ni yanzu ina tsoran kada ma ya yaudareni ya sakeni bayan na janye daga hakkokina ba tareda ya bani wani mayi ba, yanzu gashi labarina duk ya bazu ya yada cewa wai auran mutu’a yayi da ni waini kyakkyawar mace ce duk yabi ya zubar mini da mutunci da garinmu.

Ina neman taimakonku da bayani ina godiya.

Da sunan Allah mai Rahama mai jin kai

Idan kin jarraba shi kin gano cewa lallai ba mai gaskiya bane cikin zantukansa to kada kiyi gangancin jingina da shi da sakin jiki da shi ki snaya hankali domin lamintar da gobenki sannan kiyi hakuri ki dogara ga Allah Allah ne abin neman taimako.

Tarihi: [2019/12/1]     Ziyara: [655]

Tura tambaya