lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

Bahasul-Karijul Fikhu, Fadin (Kazalikallahu Rabbi) sau daya ko biyu ko uku bayan karatun suratul Iklasi

Fikhu (88) bakwai ga watan Shawwal shekara 1441

Wuri: Muntada Jabalil Amil Islami tareda Samahatus Assayid Adil-Alawi.

Na tara: shine fadin (Kazalikallahu Rabbi) sau daya ko sau biyu ko uku bayan karatun suratu Iklasi, ko ya karantawa da sigar Jam'i (Kazikallahu Rabbana) kuma bayan Limami ya kammala karatun Fatiha Mamu yace: (Alhamdulillahi Rabbil Alamina) bari dai ko da shi kadai yake sallarsa.

Ina cewa: hakan yana daga cikin mustahabbai cikin sallar farilla da nafila lallai suratu Iklasi sura ce da take bayanin Allah kamar yanda ya zo a riwayoyi da suke shiryarwa kan cewa Yahudawa sun cewa Annabi (s.a.w) ka siffanta mana yanda ubangjinka yake, sia wannan ta sauko kuma aka sanya mata suna da suratul Tauhid a wani karon kuma ana kiranta da suratu Iklas, mustahabbi ne karantata da tilawarta mai karatu Mai salla ya karanta ta a mukamin ikirari da dayanta ubangiji da tsantar dayanta shi ta hanya kawo daya daha cikin wadannan sigogi guda uku (Kazalikallahu Rabbi) shuhura da Sahihatu Ibn Hajjaju suna shiryarwa kan hakan.    

محمد بن الحسن بإسناده عن الحسين بن سعيد عن صفوان عن عبد الرحمن إبن الحجاج عن أبي عبد الله عليه السلام في حديث: أنّ أبا جعفر عليه السلام كان يقرأ (قل هو الله أحد) فإذا فرغ منها قال. كذلك الله، أو كذالك الله ربي([1]).

Muhammad Ibn Hassan da isnadinsa daga Husaini Ibn Sa'id daga Sufwanu daga Abdur-Rahman Ibn Hajjaj daga Abu Abdullahi amincin Allah ya kara tabbata a gareshi cikin wani hadisi: hakika Abu Jafar (a.s) ya kasance yana karanta (Kulhuwallahu) idan ya kammalata sai yace: (Kazalikallahu Rabbi).

Sakamakon fadinsa sau daya ya wadatar cikin koyi da Imam Bakir amincin Allah ya tabbata a gareshi, sannan lallai abin koyi ya tabbata agreku cikin Manzon Allah da iyalansa tsarkaka, dukkaninsu haske ne guda daya.

Na biyu: ko kuma ya fadi sau biyu kamar yanda ya zo cikin Alkafi da isnadinsa.

محمد بن يعقوب عن محمد بن أبي عبد الله رفعه عن عبد العزيز بن المهتدي قال: سألت الرضا عليه السلام عن التوحيد فقال: كل من قرأ (قل هو الله أحد) وآمن بها فقد عرف التوحيد، قلت: كيف يقرأها؟ قال: كما يقرأ النّاس، وزاد فيها: كذلك الله ربي كذلك الله ربي، ورواه الصدوق في كتاب (التوحيد) عن علي بن أحمد بن محمد بن عمران الدّقاق عن محمد بن أبي عبد الله الكوفي، عن محمد بن إسماعيل البرمكي عن الحسين بن الحسن عن بن زياد عن عبد العزيز المهتدي عن الرضا عليه السلام مثله.

Muhammad Ibn Yakub daga Muhammad Ibn Abu Abudullah yayi rafa'in hadisin zuwa ga Abdul'Aziz Ibn Muhtadi yace: na tambayi Arrida aminci ya tabbata a gareshi dangane suratul Tauhid sai yace: duk wanda ya karanta (Kulhuwallahu) ya kuma yi imani da ita  hakika ya san tauhidi, nace: yaya zai karanta ta?sai yace kamar yanda mutane suke karantawa. Ya kuma kara cikinta da (kazalikallahu Rabbi), Saduk ya rawaito  cikin littafin (Attauhid) daga Aliyu Ahmad ibn Muhammad Imranu Dakkak daga Muhammad Ibn Abu Abdullahi Alkufi, daga Muhammad Ibn Isma'il Baramaki daga Husaini Ibn Hassan daga Abdul-Aziz  Almuhtadi daga Arrida amincin Allah ya tabbata gareshi misalin wannan hadisi.

Na uku: ko kuma ya fada sau uku: daga Fadalu Ibn Hassan Dabarasi cikin (Majma'ul Bayan) daga Fadalu Ibn  Yasar yace:

أمرني أبو جعفر عليه السلام أن أقرء (قل هو الله أحد) وأقول إذا فرغت منها: (كذلك الله ربي) ثلاثاً.

Abu Jafar (a.s) ya umarceni da in karanta (Kulhuwallahu) kuma idan na kammalata sai ince (Kazalikallahu Rabbi) sau uku.

Na hudu: yace: (Kazalikallahu Rabbana) hadisin da ya zo cikin littafin Uyunu Akbaru Rida yana shiryarwa kan hakan cikin wani hadisi da isnadinsa daga Tamimu Ibn Abdul Tamimi daga babansa, daga Ahmad Ibn Aliyul Ansari daga Raja'u Ibn Abu Zahhak_ wanda yayi masa rakiya daga Madina zuwa garin Kurasan-daga Arrida amincin Allah ya tabbata a gareshi cikin wani hadisi lallai shi ya kasance idan ya karanta (Kulhuwallahu) a sirrance sai yace (huwa Ahadun) idna y agama sai yace: (Kazalikallahu Rabbana) sau uku: hakama ya zo cikin Kabaru Yasari kamar yanda ya zo cikin littafin Almustadrak babi 16 daga abwabul kira'a fis salat hadisi na 8 tareda Karin: (wa Rabbi Aba'ina Awwalina). Mustahabbina fadin hakan cikin sallar jam'i bayan LImami y agama karanta Fatiha sai Mamu yace: (Alhamdulillahi Rabbil Alamina) abinda yake shiryarwa kan shine shuhura da kuma  abinda ya zo cikin babi na 17 daga abwabul kira'atu fis salati cikin littafin Wasa'il: babu adamul jawazi ta'amin- ma'ana hana fadin amin bayan kammala fatiha lallai hakanm yana daga kalaman mutane kawai kuma baya halasta fadinsa cikin sallah- kamar yanda yake a Mazhabar wadanda suka saba da Ahlil-baiti, da kuma mustahabbanci fadin Mamu : (Alhamdulillahi Rabbil Alamina) cikin babin hadisai guda shida suka zo, cikin riwaya ta farko

عن محمد بن يعقوب عن علي بن إبراهيم عن أبيه عن عبد الله بن المغيرة عن جميل عن أبي عبد الله عليه السلام قال: إذا كنت خلف إمام فقرأ الحمد وفرغ من قراءتها فقل أنت: (الحمد لله ربّ العالمين) ولا تقل آمين.

Daga Muhammad Ibn Yakub daga Aliyu Ibn Ibarahim daga babansa daga Abdullahi Ibn Mugiratu daga jamilu daga Abu Abdullahi amincin Allah ya tabbata a gareshi yace: idan ka kasance a bayan Limami sai ya zamana ya karanta Fatiha ya kammalata to kace (Alhamdulillahi Rabbil Alamina) ka da kace Amin.

Lallai wannan hani da yake fa'idantar da haramci kuma yana jawo baci da gurbatar salla idan ya zama an fade shi da ganganci, idan ko ba da ganganci ba to ba a maimaita salla sai da abubuwa guda biyar.

Na goma; karatun ba'arin wasu kebantattun surori cikin ba'arin wasu salloli …

Ina cewa: mustahabbi ne cikin ba'arin wasu salloli a karanta ba'arin kebantattun surori Almuhakkikul Hilli (k.s) ya kawo jimla daga cikinsu:

1-karanta suratul Naba'i (Amma yata sa'alun) haka (Hal ata da suratul Dahari) haka zalika karanta (suratu Hal Ataka) ko kuma muce suratu Gashiya, da suratu (Kiyama) a cikin sallar Asubahi, haka cikin wasu sallolin tareda kebantattub surorin da ake karantawa cikinsu, da karanta suratu (Sabbis ismaka Rabbika) da (Shamsu wa duhaha) da makamantansu cikin salolin Azuhur da Isha'i da karanta (Iza ja a)  da (Alhakumu takasur) cikin sallolin La'asar da Magariba, hujja kan haka shine shuhura da kuma abinda ya zo daga jumlar hadisai duk da cewa ba'arinsu suna da raunanar isnadi sai dai idan anyi riko da aiki da ka'idar (Attasamuhu fi Adillatil sunan) kamar yanda wannan shine ra'ayinmu, Muhammad Ibn Muslim ya rawaito cikin wani hadisi: cikin Wasa'il babi 48 daga Abwabul  kira'atu fis salati wama yustahabbu kira'atu bihi fil fara'id …. A cikin babin akwai riwayoyi guda uku.

2-

محمد بن الحسن بإسناده عن علي بن الحكم عن أبي أيوب الخزاز عن محمد بن مسلم في حديث قال: قلت  لأبي عبد الله عليه السلام: أي السور نقرأ في الصلاة؟قال: أما الظهر والعشاء الآخرة ـ أي بعد صلاة المغرب ـ تقرأ فيهما سواء، والعصر والمغرب سواء، وأما الغداة فأطول، وأما الظهر والعشاء الآخرة فسبح إسم ربك الأعلى والشمس وضحاها ونحوها، وأمّأ العصر والمغرب: فإذا جاء نصر الله، وألهاكم التكاثر) ونحوها، وأمّا الغداة: فعمّ يتساءلون ، وهل آتاك حديث الغاشية، ولا أقسم بيوم القيامة وهل أتى على الإنسان حين من الدّهر.

Muhammad Ib Hassan da isnadinsa daga Aliyu Ibn Hakam daga Abu Ayyuba Alkazzazu daga Muhammad Ibn Muslim cikin wani hadisi yace: na cewa Abu Abdullah amincin Allah ya kara tabbata a gareshi: wacce sura zamu karanta cikin sallah? Yace: amma sallar Azuhur da Isha bayan Magariba kayi karatu bai daya cikinsu, amma La'asar da da Magariba suma kayi bai daya, amma Asubahi ka karanta mafi tsayi, amma Azuhur da Isha ka karanta suratu Sabbi da Shamsu da makamantansu, amma La'asar da Magariba cikinsu ka karanta Iza ja'a da Alhakumut takasur, amma salllar Asuba it aka karanta Amma yata sa'alun , da Hal ataka, da La ukusumu da Hal ata Alal insani hinin minad dahari.

وفي الأولى: محمد بن الحسن بإسناده عن أحمد بن محمد بن عيسى، عن الحسن بن محبوب عن أبان عن عيسى بن عبد الله القمي عن أبي عبد الله عليه السلام.

قال: كان رسول الله صلى الله عليه وآله وسلم يصلي الغداة بعمّ يتسائلون، وهل أتاك حديث الغاشية (وهل أتى على الإنسان) ولا أقسم بيوم القيامة وشبهها، وكان يصلي الظهر سبح إسم ربك الأعلى، والشمس وضحاها، و(هل آتاك حديث الغاشية وشبهها، وكان يصلي المغرب بقل هود الله أحد، و(إذا جاء نصر الله والفتح) و(إذا زلزلت) وكان يصلّي العشاء الآخرة بنحو ما يصلي في الظهر، والعصر: بنحوه من المغرب (الوسائل: باب 48 ـ ح1).

Cikin  ta farko: daga Muhammad Ibn Muslim da isnadinsa daga Ahmad Muhammad Ibn Isa daga Hassan Ibn Mahbub  daga Abban daga Isa Ibn Abdur-Rahman Ibn  Abdullahi Alkummi daga Abu Abdullahi  yace: Manzon (s.a.w) Allah ya kasance yana karanta suartul Amma cikin sallar Asubahi, haka Hal ata hadisul gashiya da suratu Hal ata alal insani, da suratu Kiyama da makamantansu, haka zalika ya kasance yana karanta Sabbi cikin Azuhur da Asubahi da Shamsu wa duhaha, da suratu Gashiya da makamantansu, haka yana sallar Magariba da suratul Iklas da suratu Nasru, da suratu Zilzilatu haka yana sallatar Isha da da yanayin da ya sallaci Azuhur , haka La'asar da yanayin Mgariba.

Allama Yusuf Baharani mawallafin littafin Hada'ik a wannan mukami yana cewa: abinda wasu adadi daga Malamai suka fada na cewa Mustahabbi ne karanta wadannan surrori daki-daki su suna daga surorin Muhammad (s.a.w) har zuwa karshen Kura'ni , sai masallaci ya karanta doguwar sura cikin sallar Asubahi, ya kuma karanta tsakatsaki cikin sallar  Isha da kuma gajerikya cikin Azuhur da La'asar da Magariba.

Akwai cigaba wannan bahasi da yardarm Allah.


([1]).الوسائل: باب 20 من أبواب القراءة في الصلاة الحديث الثاني وفي الباب إحدى عشر رواية.

([2]).الحدائق: 8: 176.

 

Tura tambaya