lisdin makaloli sababun makaloli makaloli Mukalolin da akaranta dayawa.

dayanta Allah a cikin ibada

 

dayanta Allah a cikin ibada

Akida ta biyu wadda ake kidayata ada matsayin gamammun abubua a wajen wahabiyawa akidarsu cikin dayanata Allah a cikin ibada , lallai su ta hanyar shigar da wasu abubuwa a cikin ma'anar ibada hakika sun kuntatawa kawukansu da wasusnsu da'irar ibada ta yadda ta kai ga hatta ba zai iya yiwuwa ayi aiki kan doron haskenta ba, har sai ta kai ga al'amarinsu ya tuke ga fitar da su daga ma'abota dayanta Allah tsantsa cikin ibada, alhalin su suna tsammani cewa suna kyawunta aiki da akida, da kuma cewa lallai su ne ma'abota dayanta Allah duk wanda bai kasance cikinsu ba mushirki ne ko da kuwa ya kasance ana kidaya shi daga cikin musulmi.

Lallai ibn taimiya shi mahangar farko a wurin wahabiyawa salafawa, suna raya cewa ita ibada tan agasgatuwa kan dukkanin abin da Allah ke so yake kuma yarda da shi a kansa saki babu kaidi, babu banbanci cikin kasantuwarta cikin ayyuka ko kuma furuci ko aikin zahiri ko na badini, kamar misalin sallah zakka azumi sadaka da sauke amana da sadar da zumunci, dukkanin wani aiki dake hakaito girmamawa da karrama wanin Allah mai girma da daukaka to wanne aiki shirka ne cikin bauta, kai hatta cikinsu akwai wadanda suke hukunta yin hakan da kafirta da zindikanci, misali kan wannan akida ta su sun ce: yana daga cikin shirka mafi girma da kafirci cikin bautar Allah shi ne neman ceto daga wanin Allah da tawassuli da neman tabarruki da dai abin da ya yi kama da haka ga waninsa mai girma da daukaka, kai wajensu hatta ziyarartar kaburburan bayin Allah kamar misalin kaburburan annabawa da wasiyyai da saalihai maza da mata yana daga cikin shirka haka ma girmamasu da karrama ruhinsu a kaburburansu duka shirka ne.

Daga cikin abin da suke kirgawa a shiraka akwai yin salati ga annabi da daga sauti, musammam ma a gurin kabarinsa mai daraja, haka raya bikin zagayowar ranar haihuwar waliyyan Allah musammam yin mauludi annabi da raya ranakun tunawa bda wafatinsu.

 

Amsa:

Wannan fahimta ta `yan wahabiyawa ta saba karara da nassin ayoyin kur'ani mai daraja da hadisan annabi masu daraja da al'adar sahabbai  da dukkanin musulmai tsawon karnoni cikin kowanne zamani da kasa, kamar yadda hakan na sabawa hankali da tsarin halitta dayantatta.

Hakikanin gaskiya su dai `yan wahabiya sun fassara ibada da wani yanayi da yake toshewa da katangewa zuwa muslunci mara karkacewa ga barin gaskiya wanda yaransa hsine bin tsarin halitta da lafiyayyen hankali, bai buya ba cewa lallai ita ibada ga Allah kadai akeyinta, lallai bauatar wain Allah na cin karo da tauhidi amma sai dai cewa ba kowanne aikine ko furuci ba da ke gangarowa daga mutum ke hakaitar da girmamawa da karramawa ga wanin Allah kamar misalin waliyansa da manzanninsa, ko kuma ya kasakanta da kansa kamar misalinsa kaskantar da kan almajiri ke gaban malaminsa ke zama daya daga cikin abubuwan da ke gasagata bauta ga wanin Allah ba?

Lallai daga cikin mafi girman abubuwan da ke gasgata kaskantar da kai da yin kushu'i shi ne sujjada, hakika ya zo cikin littafinsa mai girma yin sujjada ga wanin Allah, lallai bawai kadai yin hakan ya halarta ba kai Allah ne matsarkaki madaukaki ya yi umarni cikin suratu bakara aya ta (34) cikin sujjadar da mala'iku su kaiwa adamu (as) bari madai hakan na lazimta cewa iblis bawahabiye ne fiye da wahabiyawa a kankin kansu, lallai shi iblis shi ne jagaban masu tauhidin cikin wahabiyawa tunda yaki yin sujjada ga wanin Allah wato adamu kamar yadda wasu ba'arin gurbatattun sufaye suke fadin hakan saboda kin sujjadarsa ga adamu (as) shin yanzu kenan lallai mala'iku sunyi shirka ta hanyar yin sujadarsu ga adamu wanin Allah? Me ya sameku ne kaka kuke hukunci?

Idan sujjada ta kaasance daya daga abubuwa da ke gasgata bauta ibada da zai lazimta cewa yakubu da matasra da `ya`yansa suma sunyiwa Allah tarayya da waninsa da shirka mafi girma cikin sujjadarsu ga annabi yusuf siddik (as)?

Bari da ace kaskantar da kai da rankwafawa wanin Allah ana kidanta shi daga shirka da hakan ya lazimta shirkantar da duk wanda ya yi dawafi gad akin ka'aba domin ai ita kanta ka'aba ba komai bace face duwatsu ba ta cutarwa ko amfanarwa kamar yadda suka fada?

Dukkanin abin da za a fadi kan basu amsa kan wadannan ishkaloli na su da tunkudesuda mu ke  kawo cikin dukkanin girmamawa karramawa ga waliayan Allah cikin rayuwarsu da bayan wafatinsu  kamar misalin ziyartar kaburburansu da neman cetonsu, lallai su tsanine zuwa ga Allah matsarkaki,  bawai kawai gundarin kaskantar da kai da rankwafawa ke kasancewa na gasgata ma'anar ibada ba.

 kamar yadda cikin neman ceto da kamun kafa da neman tabarruki da makamantansu.

Daga abin ban takaici da ban radadi da misalin wadannan asalai guda biyu cikin tauhidi da ibada sun kafirta daukacin musulmai dagta shi'a har sunna, sun wulakanta annabawa da waliyyai da imamai tsarkaka (as) bari ma dai sun ki su sun kaunaci abokanan fadansu kamar misalin dangin umayyawa da jelarsu halifofin abbasiyawa.

A hakika ahabiyawa sun kasance `ya`yan banu umayya cikin nuna kiyayyarsu ga ahlul-baiti da mabiyansu da masoyansu, tayiwu hakan ya kasance saboda biyayyarsu ga banu umayya suke zavar misalin wannan akidar vata main vatarwa, suka lalata hadin kai da kauna da ta ke tsakankanin musulmai, da kuma guvata tanadin musulmai kan yakar makiyinsu da sukai tarayya kansa daga yahudawan sahayomniya da masuniya da shu'iyya `yan gurguzu da `yan jari hujja a wannan zamani da muke ciki.

Lallai Allah matsarkaki ya yi alkawali kuma ba zai tava saba alkawalinsa ba, lallai kumfa za ta tafi cikin kekasa, abin da zai amafani mutane zai zauna a doron kasa, lallai karya da vata da sannu za su gushe su rushe, lallai gaskiya za ta bayyana ko da kkuwa zama ya yi duli ya tsawaita, shin akwai wani abu bayan gaskiya da ya wuce vata, ku fadaka yak u ma'aboata hankula da basira.         

 

Tura tambaya