mauro,i daban-daban Taambayoyin karshe Wasu daga cikin tambayoyi Tambayoyin da akafi karantawa

Taambayoyin karshe

Me nene hadafin halittar dan Adam?

Assalamu alaikum
Wasu suna cewa hadafin halittar dan Adam shine domin a bauta wa Allah ko kuma domin a san shi, amma sai gashi in muka lura da yawan mutanen da suka san Allah kuma har suke bauta masa ba su kai yawan mutanen da ba su sanshi ba, ko malam zai mana ka rin bayani akan haka?

Da sunan Allah me rahama me jin kai

Fadin Al’qur’ani ne ce (وَمَا خَلَقْت الْجِنّ وَالْإِنْس إِلَّا لِيَعْبُدُونِ) bamu halicci dan adam da Aljanba ba face su bauta min, sannan dukkan musulmai sun yarda da hakan, don haka daya daga cikin falsafar halittar dan adam shine ya bauta wa Allah sai dai wannan bauta bautace na tashri’I wato dokane wanda Allah yasan ya don haka zaa iya samin wasu mutane da bazasuyi bi ba domin duk dan Adam yana da zabi, amma kasantuwan cewa yawancin yan adam basa bin wannan doka bashi ne dalili da za ace dokar ba daidai ba ne, sai dai ace duk wanda baya biyayya ga wanna doka zai kasance cikin masu sabo da kuma bata, kasantuwan hakan ba shine zai sa dokan ya kasance ba daidai ba kamar yadda hankali da kuma ruwayoyi suka tabbatar, don haka dokan bazai kasance  kuskure ko shirme ba kamar yadda sauran dokoki da yan adam sukan sa, don wasu basa bin dokan bashi ne dokan ya kasance ba daidai ba

والله المستعان

Tarihi: [2016/9/7]     Ziyara: [994]

Tura tambaya